Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 21

Sponsored Links

By
*GARKUWAR FULANI*Ganin wani irin hayaƙi fari tas yana fitowa, tako wacce ƙofa na jikin curin.
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya kamo hannun Jabeer yaja da ƙarfi.
Alamun ya nitsu ya zauna, cikin mamaki ya zubawa tarin hayaƙin dake bulbulowa daga ƙofofin ramin shirgegen curin.
Su kuwa ga ɗayansu hankali konce suke zaune.
Ido ya zuba musu tare da cewa.
“Me hakan?”.
Da sauri Lamiɗo ya girgiza mishi kai hakanne ya sashi jan gajeren tsaki tare da cewa.
“Nifa ba son wannan soki burusun naku da surkunlenku nakeyi ba. Me gamina da ku da tsare-tsaren naku. Fisabilillahi me wannan?”.
Cikin faɗa Lamiɗo ya sa hannu zai bugi bakinshi da sauri ya kauce.
Cikin hatsala Lamiɗo yace.
“Wannan bakin naka da baya mutuwa, komai sai kayi inkarin a kai tabbas sai na kashe bakin nan”.
Wani kallo yayi mishi tare da cewa.
“Uhumm ai babu mai kashe bakin Muhammad Jabeer sai Allah”.
Ganin zaija suma suyi surutune ya sasu kauda idonsu kanshi.

Bayan kusan mitinu goma, sai ga hayaƙin nan ya bar fitowa,
Sai wani irin huci.
Da sauri Jabeer yace.
“Nifa zan tafi, inma kun mance in tuna muku yau jumma’a ace, inada abinda yafi wannan abun naku mahimmanci a rayuwata ta duniya da ƙiyama, yanzu gashi har kusan sha biyu.”
Murmushi sukayi baki ɗayansu ba tare da sunce mishi komaiba.
Sabida dama sun san za’ayi haka kam.
Sabida kowa ya sani shi Jabeer yana barranta da duk irin waɗannan ababen gado na sarauta shiyasa sarautar kanta shi bata ɗaɗashi da ƙasa ba.

Da sauri ya buɗe siraran idanunshi da kyau.
Sabida ganin wani irin ƙaton maciji ya sako kanshi cikin babban ramin da yafi girma.

Related Articles

Da sauri yace.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun!.”
Sai kuma ya zubawa maciyar nan idanu.
Tana fitowa cikin ramin ta, zuɗuɗuɗuɗuɗu. Haka yake zaro jikinshi.
Haƙiƙa dole duk wanda bai taɓa ganin macijinba bai kuma san da zamanshi ba, dole ya razana.
Dan ma shi zuciyarshi na cike da tsoron Allah so irin wadannan ababen ba kasafai suke firgitashiba.
tashinsa fahimtar ko wani ɗan abin sihirin za’ayi mishi ne.
Wani dagon numfashi yaja mai ƙarfi ya sauƙe ganin. Yadda macijiyarna taketa keta fitowa taƙi ƙarewa.
Su dai su Lamiɗo shiru sukayi a zaune.
Saida ta gama fitowane, ya rage iya bindinta sai gashi ta fito bindinta na kananmaɗe da wasu irin kitsastsun bulalin da ka gansu kasan tsoffine.
A hankali ya turo bindinshi gaban Lamiɗo,
Ya ajiyesu, sai kuma ya sumkuyo da kanshi ya zaro harshensa ya rinƙa lasar bulalin nan saida suka fito ras kamar an wonkesu.
Kana ta juya ta nufi cikin curin zuɗuɗuɗuɗuɗu ta koma,
Kamar forko sai ga hayaƙin.

Wani nannauyan numfashi Jabeer ya sauƙe tare da cewa.
“Uhum inda ranka kasha kallo. Oh ni Muhammad Jabeer an ɗauramin jakar tsaba za’a jazamin kaji su bini su tsastsageni.
Du wai wadannan abubuwan na menene wai dan Allah”.
Ya ƙarishe mgnar yana kallonsu baki ɗayansu,
fuskarshi cike da alamun fargaban gudun saɓawa ubamgijinshi.

Su kuwa saida hayaƙin ya gama ɓacewa baki ɗaya sannan Lamiɗo ya fara miƙewa kana suma duk suka miƙa.
Sarkin Shaɗi ruggume da bulalin.

Juyawa sukayi zasu nufi hanyar da zata ɓullo ta falon Lamiɗo,
da sauri ya ɗan motsosu tare da cewa.
“Dan Allah shi wannan abun me amfanin zamanshi a nan? Wurinda Kum san duk baƙin da suke zuwa tako wani sashi na duniya ganin abin tarihin masarautar Joɗa muna kawosu nan.
Yanzu in wata ran yunwa ta koroshi ya fito ya cutar da mutane fa me zakuce?”.
Cikin ƙosawa da mgnar Galadima ya gyara riƙon da yayiwa sandarsa cikin sanyi yace.
“Bata tare da yunwa, macijiyar da duk wata sai an ajiye mata motar ƙwai a cikashi da kiret-kiret na ƙwai shine abincinsa”.
Da sauri Galadima ya nufi hanyar fita.
Lamiɗo kuwa tuni sun tafi.

Ganin sun tafi sun barshi a nan a tsayene. Yasashi sauƙe numfashin tare da juyawa ya nufi, ƙofar da zata sadashi da falonshi.

A hankali yake taku, cikin kasala da mutuwar jiki, da mgnar zuci.
“Wai ya zanyine? Wanna wacce irinyar masifeffiyar rayuwace? Yaushe zamu samu Allah ya gama tsarkake mana wannan masarautar Joɗa ya rabata da wadannan tsarabe-tsaraben gargaji.
Wannan wacce iriyar fitinace?”.
Dogon numfashi yaja lokacin da ya shigo falonshi,
babu kowa, can babban falo ma babu kowa bisa dukkan alamu duk sunje shirin sallan jumma’a ne.

A hankali ya kutsa kai cikin bedroom ɗin shi.
Kai tsaye bathroom ya wuce.
Jallabiyar jikinshi da hirami da vest ɗin ya cire,
Cillasu yayi cikin injin wonki.
A hankali yake taku kanshi a sunkuye dagashi sai boxes Sky blue.
A hankali ya shiga cikin wurin wonkan.
Kamar yadda ya saba haka yayi wonkan jumma’a anshi.

Bayan ya fitone ya nufi drower’n glass ɗin dake cikin bathroom ɗin.
Wani tattausan Baby towel ya ɗauka bisa saman kafaɗunshi ya ɗauri ya fara gogewa, yana tsane ruwan jikinshi.
Kana a hankali ya ɗauki wanni babban towel ɗin ya ɗaura daga saman ƙirjinshi.
Wanda ya sauƙo har guiwa shi, a hankali yasa hannun ta ciki ya fara murza boxes ɗin yayi ƙasa, dashi yana zuwa sharabanshi ya riƙe shi ya zare ƙafa ɗaya, kana ya zare ɗayar ma.
Lallaɓeshi yayi ya matse kana ya shanyashi kan ƙarfin silver da yake na shanya.
Farar jallabiya ya zura a jikinshi, kana ya kwance towel ɗin. Dashi ya goge suman kanshi.

Cikin hamzari ya fito bedroom,
Kai tsaye gaban dreesing mirror ya nufa, mai ya shafa a dukkan sashin jikinshi. Kana ya taje tattausan suman kanshi tare da shafa mishi manshi, wani Duaol jannah mai masifar daɗi ya shafawa jikinsa, kana ya ɗauki wani ƙaramin kum ya tace tattausan sajenshi ya kontar dashi lib-lib hakama gemunshi.

Saida ya gama komai na gaban Mirror kana ya nufi babban drower’nshi da sauri-sauri yakeyin komai.
Wani tattausan jallabiya mai masifar kyau da taushi fari ƙal ya zaro.
Kana ya ɗan yi sama da kanshi ya kalli cikin tsep ɗin ƙarshe na drower’n inda al’kyabbanshi suke jere a kimtse tamkar shagon saidasu.
Hannu yasa ya zaro wata sabuwa dal tana cikin ledanta tana haɗe da hiramin ta da komai.
Rufe wannan wurin yayi kana, ya buɗe wani sashin inda ƙananan kayan shi ke jere, boxes and singlet ya zaro farara ƙal suma sabbi ne.
Da sauri ya rufe drower’n kana yazo ya ajiyesu bakin gadonshi.
Ba tare da ya cire jallabiyar jikinshi ba, ya saka boxes ɗinshi saida ya dai-dai-ta zamanta a jikinshi da kyau ya kimtsa komai nashi yadda zaiji daɗi tafiya, kana ya zare jallabiyar ya ajiyeta bakin gadon
Singlet ɗin ya yasa, sannan ya ɗauki farar tattausar jallabiya mai dogon hannun ya saka, jallabiyar daya cire ya ɗauka ya gaban ƙaton drower’n nashi ya nufa, wani side ɗin ya buɗe nan ya saƙalata.
Kana ya dawo bakin gadon.
Ledan al’kyabbar ya farka da ƙarfi da kuma sauri sabida ganin tuni ƙarfe ɗaya da rabi tayi, yasan yanzu masallacin ya cika maƙil da mutane.
Ɗan gajeren tsaki yaja, tare da ci gaba da warware al’kyabbar.
Yana gamawa ya zurata a jikinshi, al’kyabbar baƙace, sai gefen bakinta da akayiwa kolliya da wani zare mai masifar kyau Golding color irin mai sheƙi da ɗaukar ido, hakama, kan kafaɗunsa har zuwa hannunta anja zirin irin wannan kolliyar.
da sauri ya dai-dai-ta zamanta a jikinshi, kana
Ya juya ya nufi, gaban dreesing mirror da hiraminshi a hannunshi,
Yana isa ya ajiye baƙin abin, kana ya ware farin hiramin shima da kolliyar Golding color a jikinshi, ya ninkeshi kamar yadda muke ninke dankwali, bayan ya gama ne.
Ya ɗaurashi a kanshi ya dai-dai-ta zamanshi kana, ya ɗauki baƙin abin wanda shima an zagayeshi da Golding color ya sakashi a akanshi, ya fito ras tamkar a Saudia.
Allah ya sani yana masifar son wannan shigar da jin daɗinta a jikinshi babu takura babu matsi gashi ka suturtu da kyau mayu masu kallon tsiya irinsu Jazrahda Batool duk basa iya ganin komai a jikinshi ba.

Da sauri ya nufi wurin aje takalma shi wanda yake na glass ne marfin ya buɗe kana, ya ɗauki wasu takalma irin nasu na sarauta Golding color ne kuma half cover ne, zura jajayen sawunshi yayi a ciki, kana ya koma gaban mirror, wani kolba turaren OudKareem mai masifar ƙamshi mai sanyi, ya fesa a duk sashin jikinsa.
Kana yasa hannunshi ya ɗauki carbinshi. Farin galashi ɗan siriri ya manna a idonshi.
Kana ya juyo da sauri zai fita, sai kuma ya tsaya cike da mamakin ganin. Haroon tsaye ya zuba mishi ido.
Ya buɗi baki zaiyi faɗa sai kuma yayi shiru jin Haroon na cewa.
“Kada kace zakayi faɗa Lamiɗo ne yace inzo in kiraka, lokaci na tafiya fa.”
Bai kulashi ba kawai yayi gaba, da sauri Haroon ya bishi tare da cewa.
“Wannan baza ƙamshi haka sai kace wurin amarya zakaje, gsky kayi kyau sosai masha Allah”.
Bai kula Haroon ba sabida addu’o’in da yakeyi.
Amman duk da haka saida ya bawa Haroon amsa a zuciyarshi, yake cewa.
“Akwai wani wuri da yafi cancanta da ɗan adam yayi shiga ta tsabta da kyan shiga da ƙamshi sama da masallacin ne? Innal masajida lillafa, duk duniya da babu wurin da Allah ya keɓanta yace dakinshine sai masallatai. Nan zamu gana dashi. Domin idan mu bama ganinshi ai shi yana ganin mu”.
Murmushi Haroon yayi, dan Jabeer bai san mgnar da yakeyi a zuci ta fito filiba.

A haka dai suka shiga Masallaci.

Dole yau a gaggauce yayi Kudbar jumma’a dududu 13 minutes yayi yana kudbar kan halaccin mace ta kalli mijin da yakeson aurenta, kamar dai yadda yayi al-ƙawari a wancan satin.
Daga nan aka kabbarta sallah.

A can Rugar Bani kuwa.
A hankali Shatu ta ɗago kanta ta kalli Ba’ana jin tunda suka tsaya baice mata komaiba, ganin yadda ya zuba mata idone yasata, saurin yin ƙasa da kanta,
cikin sanyi muryar tace.
“Ya Ba’ana zamu tafi rana tanayi fa!”.
Wani dogon numfashi ya ja ya sauƙe da ƙarfi, kana a hankali ya ƙara matsowa kusa da ita da sauri tayi baya cikin tsoro, hannunshi ya ɗaga mata alamun karta gudu, kai ta jujjuya tare da ƙara matsawa cikin rawan murya tace.
“Ba kyau ina tsoro”.
Kanshi ya jingina da jikin bishiyar gamjin da suke ƙasanta, ido a rufe yace.
“Da dai inada niyar cutar dake, da bamu kawo zuwa yau ban cutar dakeba Shatu, kadafa ki mance tun kina ƴar tatsitsiyarki nake sonki kuma nake tare dake, dare da rana, kada ki mance kullum sai kinje gidanmu da dare da asuban fari kin amsowa Ummey mgninta, da har ina son cutar dake da tun wancan lokacin zan cutar dake.
To amman bani da niyar cutarki, ina sonki ne sabida Allah, da kuma gsky da zuciya ɗaya, Shatu koda zaki ƙi yarda dani a kan komai dan Allah ki yarda dani cewa ina sonki, na kuma soki a baya zan soki har gaban abadan, wlh babu ƙarya a cikin soyayyarki a zuciyata, Shatu sonki shine babban raunina a duniya.
Har yau babu wani abu dake firgitani da bani tsoro sai rasaki.
Babu wani abu na duniya daya taɓa sani zubda hawaye sai soyayyarki, dan Allah ki dena zaton dan na matso kusa dake zan cutar dake, ki amince dani in baki abinda idonki zai buɗu da gane sihiri duk ƙanƙantarshi”.
A hankali take juya mishi kai cikin sanyi tace.
“Na sani Ya Ba’ana wlh na yarda da kai akan soyayyata, na sani bazaka cutar daniba, tunda baka cutar dani a bayaba, nasan kana sona, na kuma yarda da son gsky kakemin, to amman ni bana son wadannan abubuwa asirce-asircen sabida haramun ne.
A hankali ya zame jikinshi ya zauna kan jijiyan bishiyar.
Ganin haka itama tayi sauri ta zauna bisa guiwowinta ta durƙushe a ƙasa.
Cikin mamaki tace.
“Dan Allah ya Ba’ana meyasa kwanan nan duka sai kayi ta zubda hawaye a gabana, hankalina yana tashi.”
Kanshi ya ɗan ɗaga ya kalli sama, a hankali yace.
“Shatu ina sonki zan kuma soki har iya numfashin na, bazan bari wani abu ya rabani da keba, in kuma akasamu wani ya zama ƙaddarar rabani dake, to shi kuwa tabbas zan rabashi da rayuwarshi, kiyi haƙuri in dai a kanki ne zan iya yin komai, na kuwa san duk duniya babu wanda yasan hanyar da za’abi a kamani ko aci galaba a kaina, sai ke ranki ke ɗaya tak ce kikasan duk wani sirrina ban saniba ko zaki iya min halacci ki sirranta min rayuwata”.
Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa.
“Ya Ba’ana ai rayuwa a hannun Allah take, wata ƙilma in rigaka mutuwa, kuma in dai nice in sha Allah bazan baiyana sirrinka dan a cutar da kaiba, ko ba komai kana soma kuma kace dan zaka nemo su ya Gaini ne kayi wannan tsarin gudun kada mugaye su cutar da kai, Ni na sani Ya Ba’ana waɗannan layun bazasu kareka ba, sabida ba hanyar Allah ka biba amman ni zanyi ta maka addu’a”.
Ido ya zuba mata a zahiri da baɗininta gsky ta faɗi dan yaga hakan cikin ƙwayar idanunta.
A hankali ya jawo tandun duma dake rataye a kafaɗunshi, cikin sanyi yace.
“Ga ruwa kisha”.
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
“Bana jin ƙishi”.
Tura mata tandun yayi gabanta tare da cewa.
“Eh ba mgnin ƙishi bane, kishi dan kiji sanyi a zuciyarki naga kina kuka”.
Cikin share hawayenta tace.
“Ba kai bane ka sani kukan kana ta barmin amanar sirrikanka bayan kuma shi amana rikeshi nada girma da nauyi da wuya”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Zaiyi wuya ki riƙe kenan?”.
Da sauri tace.
“In sha Allah zan riƙe”.
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
“Bazaki sha bako?”.
Kanta ta gyaɗa mishi alamar eh.
Kana ta miƙa tsaye, gaba ta ɗan yi kusa da Rafi’a, tace.
“Rafi’a mu tafi”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Rafi’a ku tsaya”.
Cikin tsoronshi Rafi’a tace.
“To Ya Ba’ana”.
Da sauri ya ƙara so gabansu, tare da cewa.
“Mata ɗago hannunki mu gani kinada zobene?”.
Kai ta girgiza alamar a a babu.
kana ta ɗaga hannunta na dama,
Yatsarshi ya karkaɗa mata tare da cewa.
“Lalala ɗago hannun hagu mu gani”.
Cikin gajiya ta ɗago hannunta, fararen tausasan zara-zaran yatsunta suka zubawa ido gaba ɗayansu.

Babu zobe ko ɗaya a yatsunta,
Murmushi yayi kana yace.
“To bari in baki zoben ziyara, koda bakya tare dani, duk lokacin da na nake kusa dake kawai zakiga zoben a yatsunki”.
Da sauri ta buɗe baki da nufin cewa a a.
Kawai sai tayi shiru ganin wani irin zoben azurfa mai masifar ƙyalli da sheƙi sai ɗauke ido yakeyi.
Ta juyo zata ce mishi a a Ya cire sai kuma tayi shiru ganin ya ɓace daga gabansu.
Yatsunta tasa da nufin cire zoben da sauri ta barshi jin tamkar yatsunta zasu tsinke.
Rafi’a kam tuni tayi gaba, haka yasa itama tabi bayanta.

Suna zuwa bakin titin suka samu motar zuwa cikin Ɓadamaya.

A can cikin masarautar Joɗa kuwa,
Bayan an idar da salla, kamar kullum Lamiɗo ya gaggaisa da mutane, talakawan garinshi.
Shi kuwa Jabeer dashi da tawagarsa duk sun nufi cikin gida.
Sabida Galadima nata ce mishi su tafi cikin gida su fara shirin tafiya.

Haka yasa duk suka nufi cikin gidan masarauta.
A nan babban farfajiyar suka ɗan tsaya.
Ido Jabeer ya ɗan zubawa jerin motocin da a ƙalla sun kai ashirin da biyar zuwa talatin an bisa alamu anyi manyan baƙi ne ko kuma za’ayi fita mai mahimmanci.

Cikin suka wuce a falo suka samu Umaymah, Hajia Mama, Aunty Juwairiyya, da Ummi, duk suna zaune suna ɗan hira.
Hibba kuwa tana kitchen.

Suna isowa ta fito da sauri jin muryarsu.
A hankali ta isa gefen Jalal cikin yin ƙasa da murya tace.
“Ya Jalal kazo kaci abinci karku tafi bakaci komaiba”.
Kanshi ya ɗan gyaɗa mata,
Jamil ne ya hararesu tare da cewa.
“Allah shi ƙara, ai in dai Jalal ne kaɗan kika gani da gwatsalel, mutumin da ba’a iya masa bare a masa gwaninta”.
Haroon ne ya ɗanyi dariya tare da cewa.
“Haka suke shida Jabeer yadda suke kamanninsu iri ɗaya hakama halinsu”.
Da sauri Jamil ya zare ido tare da ɗan ja da baya yace.
“Tab a a Ni dai wlh bance hakaba”.
Jabeer kanshi Jamil ya bashi dariyar da dole ya ɗan murmusa, tuni sukuma sauran dariya sukeyi.
Ya Jafar kuwa shi ganin murmushin Jabeer shine ke sashi murmusawa.

Ita kuwa Hibba tura baki tayi ta koma gefe ta zauna alamun tayi fushi, baibi ta kantaba, sai Jamil ɗin ne ya ɗan lallasheta, haka dai sukayi ta yar raha, saida Lamiɗo ya aiko su fito kafin.
Suka miƙa duk suka fita, shi kuwa Sheykh Jabeer gefensu Hajia Mama da Umaymah ya ɗan rusuna kusa da Umaymah a hankali yace.
“To Umaymah bari inje bisa umarnku ba don raina yaso ba”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Allah ya bada Sa’a ya kaiku lfy ya kuma dawo daku lfy, Allah ya tabbatar mana da al’khairan dake cikin wannan tafiyar, al’farma Annabi da Alqur’ani”.
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu, Hajia Mama dasu Ummi ma duk sukayi mishi addu’a, kafin ya fito.

Yauma kamar ranar mota ɗaya suka shiga da Haroon da Lamiɗo da Ya Hashim da Laminu.

Kana sauran tawagar sarki.
Daga nan suka nufi hanyar fita gari su nufi garin Shikan.
A cikin motocinsu kamar na ranan.

A tsakiyar garin Ɓadamaya ne suke tafiya sun zo dai-dai bakin Genaral Hospital Ɓadawaya.
Lamiɗo ya bada umarnin cewa su shiga cikin asibitin zai kai ziyarar dubiya wa marasa lfya.

Nan take kuwa suka jujjuya akalan motocin.
Suka fara kutsa kai cikin asibitin.
Da ƙarfi Jabeer ya rumtse idanunshi tare da furta.
“Lahaulawalaqutailla billah”.
A hankali sabida wani irin masifeffen bugu da zuciyarshi tayi da ƙarfin masifa.
Wani irin taraddadi ya diro masa.
Ya ilahi shine abinda ya ambata a saman lips ɗin shi.
Dip dab dip dab dip dab dip dab haka zuciyarshi ke harbawa da bugawa a tare a tare,
addu’o’in ya fara karantowa a zuciyarshi da harshenshi, yadda suke ƙara kutsawa cikin asibitin haka bugun zuciyarshin ke ƙaruwa.

Anan cikin asibitin kuwa, A maraba da baƙi Shatu take tun zuwanta sabida, anan aka juye duk fulanin da suka samu rauni sanadin wannan faɗan,
an zubesu a wurin gwamnatin jiha kuma tayi burus da batunsu sam bata bawa likitoci damar dubasuba,
Sai ma cewa sukayi sai fulanin sun nemo polices kafin a karɓesu.
Su kuma dama ƴan agaji ne ma suka taimaka suka kawosu nan ɗin ma.

Zuwan Shatu ne da Rafi’a da ta samesu a yashe hankalinta ya tashi.
Ranta yayi matuƙar ɓaci nan ta haura gidan sama inda can jerin jadawalin officer’s ɗin DOCTOR’S suke.
Rafi’a na biye da ita tana rabka mata kira.
“Garkuwa! Garkuwa!! Ke GARKUWA!!! Ina zakije ne wai?”.
Sam bata kula Rafi’a ba sabida abin da akayiwa ƴan uwanta yayi masifar ci mata rai.

Ganin yadda take gudu-gudu da sassarfa ne yasa itama Rafi’a ta fara Binta da gudu-gudu da sassarfa.

Yayinda kuma dai-dai lokacin Lamiɗo da tawagarsa ma ke tafe suna shiga cikin gidan saman.
Lamiɗo ne a gaba sai Jabeer da Galadima dake gefenshi da Sarkin Shaɗi.
Kana su Waziri da Wambai Matawalle da Makawa Ɗurɓi Turaki Tafida da dai sauransu, kana Dogari na rike da laima wa Lamiɗo,
Ɗanzagi kuwa ya kware murya yanata.
“Gyara kimtsi sarki ya gaisheku”.
Kana sauran fadawa masu red and blue ɗin Uniform kuwa da tabka-tabkan rawuna babu kunne ko ɗaya suna biye dasu a baya da gefe gefe, suna tafe babu takalma, ga dogin bulali masu masifar tsawo da kauri suna jansu a ƙasa.

Lamiɗo, Galadima, duk shigar manyan kaya na sarakuna, masu al’farma sukayi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer shigarsa ta al’farma na limamai yayi, wannan yasa kwarjinshi ya fi nasu.
Daga nesa zakace yafi shekarunshi in ka hangoshi sabida kamala da haibarsa da suka baiyana a fili.

Laminu kuwa tuni yayi gaba yana ɗaukar shigowarsu.
Sabida aikinshi na jarida dama neman rohotone aikinshi.

Sanadin saurin da suke ɗanyi ne yakesa al’kyabbar jikinshi ɗan buɗewa tana bazuwa hakan sai ya zama kamar ƙasaitace tasa yake wannan abun a wurin mai kallonshi.

Gaba daya duk ta inda suka zo wucewa, sai ya ɗaga hannunshi duka biyu, yayi musu sallama tare da cewa.
“Ya mai jiki?”.
In sunce da sauƙi. Sai yace.
“Laah Ba’as ɗuhhuru in sha Allah”.
Duk inda suka gilma sai an bisu da ido. Especially Jabeer da babu wanda zai kalleshi bai ƙaraba

Tuni labari ya kai ga kunnen Dim din asibitin.

Lokaci ɗaya ya kikkira DOCTOR’S ɗin ta wayar salulu ya sanar musu su kimtsa komai su kula da kowa yadda ya dace.
Mai martaba Lamiɗo na cikin asibitin.

Ita kuwa Shatu tana haurawa sama.
Ido take ɗagawa ta duba sunan Office da mai Office ɗin Office na forko taga musulmine haka yasa ta kutsa kai ciki.
Zaune yake babu kowa sabida duk majinyatan sun tafi.
Wasu an duba su, wasu kuma korarsu akayi da cewa yau half day ne, sabida haka su tafi.
Da mamaki ya ɗago kanshi jin an shigo mishi Office babu sallama. Da sauri yace.
“Waye?”.
Sabida cikin shigar yan matan larabawa take.
Arabian gawd ne mai masifar kyau da taushi a jikinta wanda samanshi yake a dai-dai jikinta ƙasa shi kuma yake a buɗe, wasu irin duwatsune a jikin rigar tun daga sama har ƙasa sai wal-wali sukeyi suna ɗaukar ido.
Tayi rolling kanta da ɗan kwalin rigar fuskarta ta fito ras a ciki.
Wasu takalmi Golding color ne masu ɗan tudu dai-dai misali sai Ƴar ma dai-daiciyar hand bang mai masifar kyau shima Golding color ne, sai wayarta ƙirar iPhone 11.
Fuskarta babu kolliya sai dai duk da haka bai hanata yin kyau ba gashin girarta ya konta lib-lib. Sai dai kuma ta rufe fuskar da tattausan Niƙab sai dai bashi da duhu sosai.
To wannane ya hana Dr Salim ganin fuskanta, ita kuwa Shatu cikin tsananin ɓacin rai da zafin tozarcin da akayi wa yan uwanta tace.
“Dr Salim”.
Cikin Mamaki yace.
“Na’am”. Yatsarta tasa tana nuna mishi maraba da baƙi ta wondon shi, cikin rauni tace.
“Dr Salim na tabbatar kai musulmine, kuma nasan kasan cew manzon Allah yace shi musulmi ɗan uwan musulmine! Shin ko ka mance hakane, da ka kasa taimakawa yan uwanka musulmai da kafurai sukayi musu rauni akazo aka watsar dasu a nan kuma kuka ƙi dubasu meyasa, ko dan kawai sun kasance fulanin dajine laifinsu?”.
Cikin sanyi Dr Salim yace.
“Wallahi umarni ne ba’a bamuba daga sama”.
Cikin tafasar zuciya tace.
“Umarni wanne irin umarni kuma zaku jira bayan Allah da Manzonsa sun baku dukkan dama da umarnin taimakawa ɗan uwanku musulmi muddin kunada dama”.
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
“Dim ɗinmu ne ya hanamu dubasu”.
Cikin kufula tace.
“Kan kafurar uwarshi! wato a cikin asibitima sai an mana ƙabilan ci, dan Allah Dr kuje ku taimakawa bayin Allancan”.

Cikin jin ƙarfin guiwa ya juya, ya fita, ya nufi can.
Ita kuma haka ta rinƙa bin duk Office ɗin da taga na musulmi ne tana shiga.

Tawagar Lamiɗo kuwa suna isa baƙin wani tamfatsetsen Office Sheykh Jabeer, ya ɗan kalli Lamiɗo tare da cewa.
“Ni bari in shiga office na, ko mutun biyar in duba kafin ku gama zagayawa”.
Cikin gamsuwa da hakan Lamiɗo yace.
“To bisimilla”.
Nan ya nufi babban barandar da Nurses suke tare a wurin maza da mata.
Jamil kuma na biye dashi da System ɗinshi a hannunshi. Hakama Haroon ya biyoshi.

Nurses ɗin kuwa suna hangoshi duk suka mimmiƙe tare da cewa.
“Sir barka da zuwa”.
Barka dai yake ce musu tare da ratsawa yana wucewa.
Su kuwa sun taru a wurin ne dan tawagar Lamiɗo na wucewa su sauƙa ƙasa su duba Fulanin nan kamar yadda Dim ɗinsu ya basu umarni sabida kada Lamiɗo ya gansu a yashe a ƙasa yasan abun bazai mishi daɗi ba.
Suna ganin ya shiga Office ɗin suka juya da nufin zasu tafin sai kuma suka tsaya jiyo muryar Shatu na cewa.
“Ku tsaya ina kuma zakuje? Baku da aikin yi ko? Amman da yake ba taimako ne a zuƙatankuba kun bar bayin Allah a wulaƙance ko?”.
Cikin masifar Nurses da su ba komaiba sai iya ciwa mutane zarafi a hatsale tace.
“Ke kuma waye”.
Kallonta Shatu tayi sama da ƙasa tare da kallon rubutun dake saman aljihun rigarta ganin sunan arniyace ga kai da gashin doki ga uban faratu kamar na jaki yasa taja tsaki tare da cewa.
“Banyi da keba, da masu hijabi nake mgn”.
Yadda tayi mgnar da ƙarfi ne yasa, su Jabeer ma jiyo muryarta,
wanda shi kuwa zuwa yanzu yana jin zuciyarshi zata iya faɗowa ƙasa dan bugawar da takeyi.
Jin muryar wata nurse ɗin tana cewa.
“Wannan ma ai iskanci ne”.
Cikin taɓe fuska ya nunawa Jalal yatsa alamun ya buɗe mushi ƙofar yaga meke faruwa da suka cika mishi kunne da hayaniya.
Da sauri Haroon yabiyo bayan Jalal suka fito.

Shi kuma Sheykh Jabeer komawa yayi ya jingina da jikin kujerar shi.
Tare da rage girman idonshi ya zubawa bayan Shatu ido.

Ita kuwa Shatu cikin zafi ta kalli arniyar nan da tace mata wannan ma ai iskanci ne tace.
“A kul kada ki kuskura ki sake kira min iskanci a gabana, ke kika sanshi ba niba, ke kika taso cikinsa”.
Sai kuma ta juya harce cikin fillanci tace.
“Shegu masu wari”.
Sai kuma ta juyo ta fuskancesu da kyau, Haroon kuwa da Jalal ido suka zuba mata cikin mamaki.
Shima Jabeer idon ya zuba mata so yake yaji meyasata ihun nan.
Ita kuwa Shatu cikin sanyi ta fuskanci musulman ciki murya a ɗan tashe tace.
“Kada dai ku manta nace daku nakeyi masu hijabi sabida nasan kun san ma’anar Al’muslim akul muslim. Kun kuma san girma da daraja da kuma wanda ya faɗi hakan”.
Cikin gamsuwa duk suka ɗaga mata kai, rai a ƙuntace tace.
“To meyasa kuka bar waɗanan can bayin Allah’n a tozarce a yashe a maraba da baƙi koda dreesing na raunuka su bakuyi musuba, menene laifinsu, kawai dan sun kasance fulanin daji, shiyasa DOCTOR’S da Nurse’s kab bazaku jiƙansu ba”.
Cikin sanyi ɗaya daga cikinsu tace.
“Ayyah yanzuma can zamu tafi. Sabida sai yanzu Dim ya bamu umarni”.
Wani dogon tsaki taja tare da cewa.
“Daga baya kenan yau kwanansu goma cib babu wanda daya dubasu, sai da suka gama jigata”.
Tsaki arnan ciki sukaja tare da juyawa suka tafi.

A hankali Jalal ya juyo ya kalli Hammanshi da yake cewa.
“Rufe min ƙofa wannan ta cika min kunne da ihu”.
Da sauri yace to.
Haroon kuwa murmushi yayi tare da juyowa zai shiga ciki kafin Jalal ya rufe ƙofar.
Da sauri ta juyo jin takun mutun a bayanta,
Cikin muryar umarni tace wa Jalal.
“Kai mai kamar larabawa tsaya kada ka rufe ƙofar, Office ɗin na arne ne ko musulmi?”.
Cikin dariya Haroon yace.
“Na musulmi ne”.
Taku ta fara tare da nufo cikin Office ɗin.
Wani irin sunkuyawa Jabeer yayi ya kifa ƙirjinshi kan babban Glass table dake gabanshi, sabida ji yakeyi tamkar kan zuciyarshi take taku. Ji yakeyi zuciyarshi zata fashe tsabar yadda take bugawa da azaban ƙarfi yadda take ƙara matsoshi haka bugawa zuciyarshi ke ƙara tsananta.
Cikin mamaki ta zubawa Office ɗin ido. Office ne mai matukar girma da kyau da tsaruwa, kai bakace Dr Office bane in ba ɗan wannan gadon da labulanshi da sauran kayan aiyukansu ka ganiba.
Duk da sai sati-sati yake zuwa nan Office ɗin tsab-tsab sai wani irin sanyi da ƙamshi yakeyi, cikin taɓe fuska tace.
“Me hakan shima DOCTOR baida lfy ne? Kodai tsabar wulaƙanci ne?”.
Murmushi mai kama da dariya Haroon yayi sabida yasan babu abinda Jabeer ya tsana yake kuma tsoro kamar a tsaya a kanshi ana mgna da ƙarfi, yo shi ko a hankali kake mgna sai yace kana mishi ihu a kai bare kuma wannan da take tsaye a kusa dashi kuma tana mgna da ƙarfi cewa zaiyi haushi takeyi.”
Shi kuwa Sheykh Jabeer hannunshi yasa yana dafe ƙahon zuciyarshi da yakejin yana tsalle.

Rafi’a kuwa tsaye tayi a bakin ƙofar tana kallon ikon Allah.

Sauran Nurses ɗin kuwa suma, tuni sun tafi, maraba da baƙin.

Ita ko Shatu a hankali ta ƙara motsowa gaban table ɗin hannunta tasa ta bug…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button