Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 25

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

25
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

Related Articles

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

***************
kawu tsabar farin cikin auren da rawar jiki shi da kawu ashiru rungume juna suka ringa yi sunawa juna barka barka da Arziki.

‘Yayansu ma da a take sukasan tinda ASH ya aureta sallamarsu zeyi tini suka hau washe Baki ba baqin cikin komai suna juyewa zuwa yayun amarya Kuma wainda suka hada dangataka yanzu da ASH TALBA suka hau amsa gaisuwar masu Allah ya Sanya alkhairi.

Jamaar masallacin sai murna ake Taya ahalin Sanda Fulde ana Basu hannu suna gaisawa da mutane.

Su kansu iyayen Naufal dole suka tashi suka iso gaban ASH din suka miqa masa hannu cikin tsananin girmamawa suna masa Allah ya Sanya alkhairi da albarka.

Abdulhameed kasa gasgata dauruwar auren yayi da ASH sbd a yanzu bama Faisal dayake gabansaba yajiwa sai Haydar Talba Wanda yasan yanda yafi kusan kowa son Amatun.

Faisal da Daman yasan ASH TALBA bazai taba aura masa Amatu da hannunsa ba sbd magana Daya yake Kuma yayita atin lokacinda aka fasa aurensu farko da Amatun,
Amma Kuma Bai taba tinanin su kawu zasu barwa ASH komai a hannunsaba bare Kuma wannan mamakin na karshe Daya kashesa daga inda yake zaune.

Abdulhameed da Faisal dinne kawai Basu motsa ba kaf masallacin sbd shiga Mafi girman mamaki da tashin hankalin wannan auren.

Kawu Bello ne ya ankare dashi ya Dan waske ya iso inda yake da qafa ya shuresa Yana cewa

“Tashi zakayi ka nuna farin cikinka Koda kuwa bakayin farin cikin Dan kuwa wlh ko uwarku bazata kunce wannan aurenba ya dauru Se lahira tinda muka daurasa”

Kasa magana Abdul yayi sai miqewa tsaye da yayi Baya gane komai ya nufi gaban Dad din ya Dan ranqwafa zaiyi masa Allah ya Sanya alkhairi Amma ya kasa Bude Baki yace komai Saida kawu ashiru dayake kusa ya karbe zancen da cewa

“Abdulhameed Allah dai yayi muku albarka yaji qan mahaifinku Sanyawa wannan auren albarka da tsawon Rai”

Sai alokacin Abdul ya iya Bude Baki ya amsa da Amin Yana tofa tasa adduar shima cikin girmamawa ga Dad Wanda ya amsa Yana miqewa tsaye ya fito masallacin gaba Daya su kawu na biye dashi kowa bakinsa a Bude sai gasar nuna jajayen hakora sukeyi.

Acan cikin gida kuwa Abdulhameed ne yafara shigowa jikinsa na Dan rawa Amma Yana kokarin dannewa da nutsuwa ya qaraso gurinsu maamah wadda tinda ta gama sallah tana kan shimfidar sallan zaune Bata tashi ba, Husnah na gefenta kusan a maqale da jikinta, AmatulMaleek kuwa tana gefe kan shimfidar sallah a lokacin take sallar Azahar din.

Husnah ce ta dago daga jikin Maamah cikin sauri tana kallan Abdul din zuciyarta a qage da son jin idan an daura auren Kuma da waye.

Maamah Bata motsaba bakuma ta tambaya ba Dan kuwa zuwa yanzu ta fadawa Allah,ta sake fadawa Allah Dan haka ta San Allah zai dubi maraicinsu itada yayanta yayiwa Amatun zabi Mafi Alkhairi.

Abdulhameed na zuwa tsayawa yayi daga gefe Yana tauna yanda zai isar musu da wannan sabon lamarin da zai girgiza sauran nutsuwarsu.

Husnah ce ta miqe tsaye tana nufarsa muryarta na Dan rawa idanuwanta na cikowa da hawayen da batasan na Menene ba tace

“An daura auren ne?
Da Faisal aka daura?

Idanuwansa da suka sauya ya zuba mata Dan Jin ita Faisal ne kawai a gabanta ba damuwar kowa ba,
Kan maamah da baisan Yaya zata amshi lamarinba yayi kafin ya Maida kallansa kan Amatu Dake sallah a natse kafin ya Bude Baki zaiyi magana maamah ta dago ta kallesa sbd itama zuwa lokacin amsarsa take Jira hakama wainda suke dakunansu kusa dasu suna jinsu kasa kunnuwan abinda Abdul din zai fada sukai a qage.

Ajiyar zuciya ya sauke tareda numfashi me dami kafin ya Bude Baki Kai tsaye yace

“An daura Auren…..

Shiru yayi ya sake Dan numfasawa kadan
Zuwa lokacin zuciyar Husnah takusa bugawa har rawa qafafunta keyi sbd son Jin idan Faisal aka daura dashi.

Miqewa maamah tayi ahankali tana kama Husnah da qafafunta ke rawa ta kalli Abdul din zatai magana ya rigata da cewa

“Da Dad dinsu Husnah din aka daur……”

Qarasa zubewa qasa Husnah tayi hawayen datake riqewa idanuwanta suna gangarowa.

Maamah kuwa Bata gama fahimtar wane Dad dinsu Husnah din ba Dan haka ta saki Husnah din tana dagowa idanuwanta jajir akan Abdul tace

“Wane Dad dinsu Husnah din?
ASH??

Gyada kansa yayi ahankali cikin sanyin jiki da damuwa sedai Bai gama jimaminba yaga maamah na Neman zubewa qasa
Kawu Dasuka shigo gidan cikin daga murya da sauri yace

“Karki yarda ki Suma bari a qarasa Miki Dalla Dalla tukuna ki sumen gaba Daya”

Kawu ashiru kuwa Abdul ya hau yiwa fada Yana cewa

“Abin farin ciki kukeson mayarwa na baqin cikin??

AmatulMaleek Dake sallah kasa riqe firgicinta tayi sbd sallarta ta riga ta lalace bayan duhu Babu abinda Idanuwanta ke Gani sai kawai ganin sukai ta silale qasa ita Kam a somen da Husnah da maamah suka kasa qarasawa.

Sakin maamah Abdul yayi yai kan Amatun Yana ambatar sunanta a cikin tsananin kauna da kulawa tareda firgici da tsoron kada Wani abun ya sameta.

Husnah ajiyar zuciya ta ringa jerowa a jejjere kaman me asthma sbd a mummunan bazatar da Bata taba tinanin shiga ba da Jin zancen Dad dinta yayi aure a yau bayan shekarun Daya dauka jiran mum dinta ta tashi
Hakama auren da AmatulMaleek wadda ko Haydar Bata taba hangowa aurenta ba Amma Dad dinsu gaba Daya shine ya aureta.

Maamah ma numfashin take fitarwa zufa na jiqata sosai sbd ciwonta kawai Daya yunquro Yana Neman tashi Dan haka amaryar kawu bello Tayo kanta da sauri tana mata fita taba ambatar sunanta.

Kawu bello Daya ga alamar wankin hula na Neman kaisu nesa batareda sun sanar da ita cikakken bayanin wannan auren duk Wanda yace bayayinsa wlh sedai ya mutu su binnesa Kuma a Dora inda aka tsaya ya Bude murya yanda maamah din zata jisa yafara cewa

“Amatu dai an daura mata aure da Me girma ASH TALBA Kuma wlh ko ciwo kika kwanta Se ta tafi Abuja ayau dinnan gwara ki daure ki danne ku tafi sbd Dake ya buqaci komawa ASH din,Idan Kuma kika kwanta ciwo saiki zauna anan jinyar aurenda bakiso dinba atafi ayi zamansa.,
Abdul Maza kamata ta miqe ku nemo ruwa a zuba mata zata qarasa dawowa daidai ku fara shiri.

Amatu Dake jikin Abdul har lokacin ya kalla Kai tsaye ya Kalli amaryarsa da matar kawu ashiru datakewa Amatun firfita yace ku zuba mata ruwa itama farfadowa zatayi ana jiransu komawa zasuyi.

Kan Husnah Dake fidda numfashi daqyar ya Maida kallansa yace

“Itama ciwon zuciyar ne da ita???
Ku kamata itama a Dan yayyafa mata ruwa ta dawo daidai.

Maamah duk yanda take cikin matsanancin halin tashin hankali da mummunan shock da rawar jiki sosai Saida maganganun kawu bellon suka Sakata Bude idanuwanta dasukai jajir batareda ta iya kallan kowaba a cikinsu sbd kirjinta Daya riqe Bata iya ko dogon motsi bare iya magana sai kawai wasu irin hawaye masu tsananin zafi da radadi suka gangaro idanuwanta.

Kawu ashiru ne yace

“Eh kiyi kukan farin ciki Allah ya cika Miki burinki yau an aurar da Amatun,
Allah ya Basu zaman lafiya karki lalata mana farin cikin aurar da ‘yarmu da mukai ayau din”

AmatulMaleek kuwa ruwa kawu bello Dayaga su saratu na sanyar zuba mata ruwan ta farfado kada ta firgici da tashin hankali ya aikata suga samu da rashi lokaci Daya da kansa ya debo ruwa zuba mata Yana ambatar sunanta cikin kulawa Yana cewa

“Abdulhameed Maza tayar da ita zaune kada ruwan ya shigar mata hanci”

Tayar da ita Abdul yayi zaune har lokacin Bata dawo hayyacinta ba tadai farfado ne kawai.

Shiru su kawu sukai suna kallanta cikin kulawar da ayau sukaji sunai mata me qarfi.

Kawu ashiru ne ya zauna kan tabarbar Da Amatun ke Akai Yana tattare babban tigarsa guri Daya yana kokarin fara jero bayanai ganin maamah da Amatun suna jinsa.

Kafin fara maganarsa babban yayansu Daya yashiga Mallam Shima gurin ya samu ya zauna sbd baisan abinda yake faruwaba Yana kauyen kusa dasu acan yake kasuwanci sai yayi wata Bai dawoba sai yau din cikin qanqanin lokaci kafin daurin auren akaje aka sanar dashi abinda yake faruwa a gigice Shima ya iso kada su bello da zalamarsu su cinye komai sedai Koda yaxo an daura auren tini Amma Jin Wanda aka daura dashi ya sakashi zubewa gaban ASH din a waje Yana zunduma Godia da Allah ya Sanya alkhairi harda hawayen cewan da Dan uwansu na duniya yau dayayi farin cikin ganin Yan uwansa sun aurar da ‘yarsa ga mutumin arziki.

Daqyar yagama gaisuwar ya nufi cikin gidan dayasan ana can ana kasafin sadakin Amatun Daya kusan kunce zariyar wandonsa sbd mamaki da farin ciki.

Zama yayi gefen kawu ashiru Yana gaisawa dasu sama sama Ya amshe zancen ashiru Dayake kokarin farawa na nasihar aure ga Amatun da uwarta datake da niyar daga hankalin auren.

Ganin hawayen da maamah ke tsiyaya bata iya magana ya Saka Mallam cewa

“Asama’u yanzu auren kikewa kuka?
Auren ne bakyaso kokuw mijin da aka daura dashi ne bakyaso?

Cikin mawuyacin hali da radadin zuci me girman gaske ta Bude Baki daqyar ta iya fizgo Kalmar “Babu aure tsakanin ASH TALBA mijin Abeeda da Amatu sbd bazan taba iya karban wannan auren…….

Cikin takaici me tsanani da zafin zuciya kawu bello ya katseta da cewa

“Uban waye ya haramta auren yarinyar data Riga ta zama mata mijinta…

Mallam da zuciya Shima ta siqesa dan idan maamah tace zata cigaba da maimaita maganar rusa auren a shirye yake da jefeta ta kurmance ta yanda bama zata iya maganarba bare harsu riqa jin wannan bayanin nata dayake Shirin musu ta leqo ta koma.

Kawu ashiru kuwa da baimaga dalilin tsayawa saurarontaba wa’azinsa yaci gaba da yiwa Amatu akan zaman aure wadda Babu abinda kunnuwanta ke ji mata dif take.
##MAMUH#
#ASH TALBA
#AMATULMALEEK TALBA
#HUSNAH TALBA
#ABEEDA TALBA
#HAYDAR TALBA
#NAUFAL TALBA

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button