Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 32

Sponsored Links

AmatulMaleek na fitowa bullowa palonsu su Farida na palon suna aiki shiyasa ta Jin Dan qarfin halin iya shiga dakinta har lokacin zuciyarta a Bata bugawa daidai ta Bude dakin ta shige.

Farida da karima Satan kallanta sukai ganin kofar data fito Kuma daga ita Se towel Amma ko dagowa su kalla Basu Isa ba sun sani.

Tana shiga dakin toilet ta nufa da sauri ya shige tareda rufewa Yana sakarwa kanta ruwa.

Related Articles

Ajiyar zuciya ta ringa saukewa tana Jan numfashinta Dake Neman shidewa cikin ruwan dayake saukar mata,
Ta jima a Hakan kafin Wani irin kuka me sanyi ya zuwar mata tana Jin kaman batada kowa,
Jin takeyi ko Husnah da Bata tareda mahaifiyarta Bata kaita maraicin uwa ba,
Bata taba Jin damuwan yanda maamah take fifita kulawan Husnah akanta ba sai yanzu,
Ina zata Saka rayuwart gameda wannan kaddarar Dake farautarta?
Batada tabbacin zata ringa tsira daga wannan mummunan kaddarar koyaushe,
Dan uwanta da Haydar dinta dasuke ture damuwar kowa su tsayu a tata basa tareda ita,
Mahaifiyarta Bata tareda ita Yaya zatai da wannan mugun abun dayake bibiyanta?
Da ASH TALBA Baya gidan a Daren zata iya mutuwa sbd tashin hankali da firgicin data samu kanta.

Kuka tayi sosai a toilet din idanuwanta suka kumbura sukai jajir kafin ta bawa kanta hakuri ta fito jiki ba qwari.

Dayake su Farida sun gyare dakin sunyi komai kafin ta fito sai Babu alaman komai na abinda ya faru jiyan
Sanyin AC da qamshin me dadi ne kawai yake tashi cikin dakin.

Batada karfin tsayawa shirywa gaban mirror Dan haka ko Mai Bata iya shafawa ba body mist kawai ta iya shafawa ta Saka Riga da wando masu Dan kauri ta koma kan gadonta ta Haye ta kwanta Dan ko apatite na cin abinci batada shi.

Daki karima ta kawo mata abincin ganin bata fitoba,
Yanda karima ta ajiye abincin har Azahar tayi Yana gurin ajiye Bata iya saukowa taci ba.

Sallan Azahar tai tayi addua sosai tana hawaye tana fadawa Allah damuwarta sbd batasan ma Yaya zatayiba.

Shiru shiru Bata fitoba duk ayyuka da abincin dasu karima sukaita kawowa suna jerawa Bata Ciba,
Kowacce daqiqa Daya idan ta wuce yammaci na kusantowa tareda dare tsoro ne yake cika zuciyarta.

Ana yin laasar ASH ya dawo gidan sbd hankalinsa Daya rabu biyu,Rabi akan aiki da tafiyan Dake gabansa a gobe Rabi Kuma akan Amatun Dake gida ba kowa hakama Yana tinanin tinda su Husnah Basu dawoba Kuma gashi kusan sati biyu koma fiye zasuyi yanason turata ta bisu Amman Kuma case da Akai na Faisal da familyn yasaka Bayajin zuwan nata acan yanada amfani,
Farha Kuma baijin tanada karfi ko iKon da zata iya tare Amatun idanma akace ta dawo gidan kafin dawowansu.

Jin shigowan motocinsa gidan ya Sakata Dan Jin sauki Sauki a tareda ita harta iya Dan daurewa taci abincin kadan Amma har lokacin ta kasa kunna wayarta sbd Batasan me zata fadawa maamah ba bayan tasan koma yayane itama tana buqatanta,

Ana yin magrib ta tashi jiki ba qwari Tayo alwala ta fito jikinta na tsananta sanyi hakama Kwanciyar hankalin zuciyarta na lalacewa sbd ganin duhu Dake Sako kai.

Kafin sallan ishai sbd ragewa Kai firgici da tashin hankalin datake ciki ta fita zuwa kitchen din dayake palon Dan dafa masa tea din data Saba dafawa a kwanakin.

Tinda ya dawo Bai fito ba sai da Akai kiran sallan magrib ya fito sanyeda dark ash jallabiya me tsananin santsi da taushi qamshinsa na Dan tashi ahankali ya nufi masallacin gidansa
kana ganinsa kasan hutawa yayi yanda ya kamata shigarsa gidan sbd bacci yayi bayan ta tashi wanka yayi ya shirya ya fito sallan.

Ma’aikatan gidan nasa suna ganinsa duk suka miqe suna tasowa ya daga musu hannu Yana Dan girgiza Kai a natse Yana cewa

“No,muyi sallah tukuna shine a gaba”

Gaba sukai zuwa cikin masallacin suka bi sahu Dan tada sallah.

Naufal Dake dakin mum Aisha cikin azababben duhu da zafi sbd komai a kashe yake hakama baida iKon ko motsawa bare kunna Wani abu a dakin asan akwai mutum ciki,
Azababbiyar yunwa da tsoro ne fal cikeda zuciyarta sbd Bai tsaya tinanin komaiba ya shigo gidan gashi fita ta gagaresa hakama a kunnuwansa yaji umarnin ASH na a harbe duk abinda aka Gani mutum ko Dabba ko aljan,
Daqyar yake iya motsawa sbd wahala da yunwa da tashin hankalin yanda zai fita yabar gidan.

Kaman Wanda baida kafafu a iska yake tafiya haka ya fito dakin Dan Daman dakon su shiga sallan magrib yakeyi duk da yasan akwai christians a ciki securities din da basa sallah suna tsare da Gidan amman dai ficewan bazata masa wuya ba tinda sunsan shi Dan gidan ne Kuma basusan shine ya shigo jiyanba da aketa nemansa.

Yana fitowa ya fara Sanda zufa na jiqasa koina idanuwansa kaman zasu fado ya fito Yana nufo hanyar kitchen da zata basa Daman ficewa da sauri.

Adaidai lokacin ne ita Kuma AmatulMaleek tana kitchen din ruwan zafin dayake Kan gas din yakusa tafasa Dan haka ta juya ta dauko flask kenan sukai arba da juna ya shigo baisan da itaba itakuma ta juyo Bata San da Shiba.

Sakin flask din hannunta tayi gabaki daya jikinta na daukan rawa ta Bude Baki da karfi zata Saki ihu
A rikice ya fizgo butan ruwan zafin Dake kan gas din Yana watsa mata ruwan tayi saurin yin Baya tana juyawa ruwan ya sauka a bayanta cikin matsananciyar azaba ta saki ihu me karfi shi kuwa ganin komai na Neman lalace masa ya tafi lahira ba shiri ya sanyashi cikin rudewa da tashin hankali Yanke shawarar bankawa kitchen din wuta yanda kafin a biyosa sai an tsaya cetan Amatun ya samu ya gudu.

Qananun towels da aprons dake Jere a kitchen din ya fizgosu duka ya jefa kan wutar gas din Dake ci Yana sake kwaso wasu kayan duk ya zuba
Yayo kanta tana zube qasa bayanta da gefen wuyanta da ruwan zafin ya taba suna Wani irin azababben azaba baiyi wata wata ba ya daga hannu zai mareta karima data shigo kitchen din ta qwalla qara me karfin gaske tana ambatar wuta.

Hayaqi da duhu tini ya cike kitchen din hakama wutan sosai ta kama duk da ruwan Dake kokarin kashe wutar Amma Sam abin ya gagara ga gas.

Ihun karima ya Saka Naufal bangajeta Yana fitowa da gudu yayi Baya,
Daidai isowan ASH su Jameel da securities na bayansa Kai karima Dake rawar jiki tana kuka ya kalla yace

“Abeeda fa??

Shiru tayi tana zare ido a rikice sbd batasan waye Abeedan ba Dan haka Bai tsaya sake Batawa kansa lokaci ba ya fada cikin kitchen din da wutarsa ta fara yawa sosai.

Cikin saa a kofa yayi tintibe da ita ya sunkuya ya daukota gabaki dayanta Yana fitowa

Muryansa a Bude abinda kowa baitaba jiba yace

“Kota yaya karya fita gidan Nan ku harbesa idan yaqi tsayawa”

Aikuwa tini suka bi bayan Naufal a tsiyace kan kace me Yana Neman guduwa ASH da Amatu ke jikinsa har lokacin cikin sautinsa Daya sake gigitasu yace

“Ku harbi duka qafafun bastard din,duka biyun ku harbesu”

Aikuwa take suka sakarwa kafafun Naufal din wuta kowacce harbi daddaya sukai mata take ya zube a gurin bayan Wani mahaukacin ihun Daya saki Yana cewa ya mutu.

Jameel ne ya Bada umarnin a kira ambulance ta daukesa zuwa asibiti hakama a kira Police suyi handing case dinsa su sungama dashi.

ASH juyawa yake Neman yi zuwa cikin gidan da ita Amma tini wutar tayi qarfi Ashe Dan haka da sauri akai Baya ana kokarin zare cylinder na gas da wainda suke Jere a bayan kitchen din ana ficewa dasu.

Gobara dai sosai da sosai ta kama gidan Dan haka dole aka fitarda mota aka dauke ASH daga gidan tareda Amatun kafin asamu kashe wutar before ta kama koina gidan.

Kai tsaye gidansa Hilton aka wuce dasu sbd duka gidajensa Dake garin akwai mutane a cikinsu haya ne da dai sauransu,
Ko kafin su Isa Jameel yayi making reservation Dan haka suna Isa Kai tsaye batareda sunbi ta main hall ba suka hau lift zuwa suite da aka kama.

Kwantar da ita yayi Yana taba jikinsa wayarsa Bata tareda shi Dan haka dole da landline yayi amfani ya buqaci likita ko nurses.

Babu Bata lokaci nurse biyu suka iso dakin tareda Neman izinin shigowa.

Suna shigowa da hannu Daya ya nuna musu inda Amatun ke kwance tana motsawa a hankali ta farfado sedai radadin datake ji abayanta da wuyanta.

Dubata sukai cikin kulawa sosai sukaga konuwar bata Riga ta taso ba Dan haka cream na qonuwa kawai suka bayar tareda Dan maganin zazzabin dayake Neman rufeta jikinta na rawa.

Bayan ficewarsu daga shi har ita Babu Wanda ya motsa bare magana,
Bacin Rai da fushi me tsananin gaske ne a cikin ransa Amma a Fili Babu me iya gane Hakan.

Ita kanta rawar da jikinta keyi da azaban datake ji yasa ta kasa ko dogon motsi Se hawaye masu dumin dasuke bin fuskarta.

A haka lokaci me tsayi ya tafi kafin ya miqe ya shige toilet sbd alwalan sallar ishai da Akai tin kafin isowansu.

Yana idar da sallah Jameel na zuwa ya kawo masa wayoyinsa da duk abubuwan buqatansa tareda sanar dashi an kashe wutan hakama masu aikin suna Nan Babu abinda ya samu bangarensu.

Maganar tafiyarsu gobe da safe yakeson yayiwa ASH din Amma baiga fuska ba sbd ran Maza a bace yake shine kadai yake iya gane tsananin bacin ran ASH din.

Shiru yayi tareda yimasa saida safe ya wuce Yana fidda wayarsa Dan siyawa Amatun ticket itama tinda dai Babu yanda zaayi Takoma gidan a wannan halin din da Naufal angama da matsalarsa bayajin har abada zai sake tafiya da duka qafafun biyu sedai Daya idan anyi dace ma kenan.

Mansion din ya sake komawa ya Saka karima dubo masa handbag din Amatun me daukesa wallet nata na Id cards da komai Yana Karba ya fito Saida yafara siyan ticket nata na tafiyan nasu kafin ya wuce gida Dan tafiyar safe zasuyi zuwa Lagos kafin daga can su zasu wuce Ghana.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button