Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 16

Sponsored Links

PAGE 16

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘

Related Articles

 

*FREE PAGE SUN ƘARE DAGA WANNAN PAGE 16 DIN IN DAI KIKAGA LITTAFINA GARKUWA BA TARE DA KIM BIYA NA SAKI A GROUP BA TO NA SATANE, DAN ALLAH DA MANZONSA KADA KU FITARMIN DA LITTAFI DAN ALLAH KU BARI IN SAMU KUƊI zuwa makka😂😂😂*

*Littafin GARKUWA na kuɗine dan Allah da Manzonsa kada ki karanta na sata, kada ki watsamin littafi a sata, turo katin MTN na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 ki biya ki karanta cikin aminci ba tare da haƙƙi naba. Ko kuma ki biya 1k domin shiga Special Group wanda cikin sati biyu rak za’a gama Part 1, da izinin ubangiji kana a shiga 2, turo dubunki ɗaya ta wannan asusun 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidan biyanki ta wannan number 09097853276 in baki da halin biyan dubu ɗaya ko baki da ra’ayi kina iya turo ɗarinki uku kacal da ban tsauwalaba sabida halin rayuwa da muke ciki. Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki sai littafina in dai kin san niyarki ki saya ki fitar da shine in kuma. Har kin sayane to dan Allah da Manzonsa gaya min in baki kuɗinki in cireki a group na, dan Allah🙏🏻 nace badon niba*

“Na Amince!”. Cikin tarin mamaki Jalal, Jamil, Imran, Haroon, Hashim, da duk sauran tawagar Lamiɗo suka, zazzaro ido cikin tarin mamaki da al’ajabi, sam basuyi zaton jin haka daga gareshi ba,
Ya Salmanu kuwa wani irin farin cikin mara misaltuwa ne, ya rufewa, domin yana ganin ikon Allah da yake nuna mishi zahirin abinda yake nuna mishi a mafarkansa tsawon kwanakin da yake a gadon asibiti.

Ba’ana kuwa da tun ɗazu ya iso, wani irin ihu yayi mai cike da farin ciki, da jin daɗin yana ganin zaiyi abinda gaba ko kashe mutanen Rugar Bani sukayi gaba ɗaya, masarautar Joɗa bazata kulasuba,
Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi keyi sabida azabar muguntarsa dake tasowa.

Arɗo Bani ma wani murmushi manufa yayi tare da cewa.
“To, ina gwanin naku?”.
Cikin karaɗi Ɗanzagi, ya kalli Jabeer tare da cewa.
“Malami ba faɗen Allah, malamai magada annabawa, Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa, GARKUWAN sarki Lamiɗo, jikan sarki, mai martaba Nuruddee. Jarumin Masarautar Joɗa.”
Gimtse bakinshi yayi ganin wani irin kallo mai ma’anoni da yawa da Jabeer ke watsa mishi,
Cikin yin ƙasa da murya tare da tsuke fuskarsa, ya ɗan ronƙofo kanshi, kusa da Lamiɗo murya a kausashe yace.
“Wannan tatsuniyar da kukeyi, bafa koyarwan shariya bace”.
Da sauri Lamiɗo ya katseshi da cewa.
“Eh amman koyarwar Masarautar Joɗa ce”.
Cikin kufula yace.
“Ya ina ce maka Allah kana cemin gadon masarautar Joɗa ce”.
Cikin haɗe fuska da ƙasaita Lamiɗo yace.
“Eh ba addini bane, kuma sai an yishi dan gadon masarautar muce”.
Kanshi ya kuma motso dashi jikin kakan nashi cikin taɓe fuska yace.
“Okay to ai sai ka tashi, ka tsaya su zaneka ciki da woje”.
Cikin kausasa murya Lamiɗo yace.
“Kai ne dai zaka tashi”.
Cikin watsawa kakan nashi wani kallo na lallai ma tsohon nan kanka ya kwance yace.
“Ai bani bane sarkin, kaine sarkin ko?”.
Cikin faɗa Lamiɗo yace.
“To ko Ubanka bai isa in sashi abu yace bazaiyi ba”.
Jin muryar Lamiɗo ta ɗan yi samane, yasa fadawanshi suka miƙe tsaye,
Ware rigunansu sukayi, suka kamgesu da jajayen rugunan nasu, ta yadda babu mai ganinsu,
Cikin haɗe fuska Jabeer yace.
“Yesss shi bazai ƙiba, tunda kai ubanshi ne, Ni kuwa babu wanda zai sani in zauna in bawa wani ƙaton fatar jikina ya zane, kai jimin zancen son zuciya, kai ni kaɗaine jikanka, a duniya, a nanma baga Ya Hashim ba ai shine babban jikanka, zancen gsky na gaji da wannan tirsashe-tirsashen naku, kanada ƴaƴan ai, ka kira ɗaya daga cikin ya’yan ka yazo ya wakil ceka mana, Amman ni dai kam Muhammad Jabeer babu wani tsohon da zanyiwa mubaya’a in tsaya wani gardin makiyayi ya ɗimeni, tunda ba faɗin Allah bane”.
Ya ƙarishe mgnar yana yunƙirin tashi tsaye.
Da sauri Galadima yasa hannu ya kamo nashi, fuskar ya kwaɓe tare da komawa zaune yana gyara hiramin kanshi da al’kyabbar jikinshi,
Cikin tausasa harshe Galadima yace.
“Jabeer kafa san ma’anar GARKUWA a masarauta.”
Cikin sanyi da ganin kima da darajar dottijon Jabeer ya kwaɓe fuska tare da cewa.
“Nifa shiyasa wannan mulkin bawai sonshi nakeyi ba, sabida wannan tsarabe-tsaraben daba na addiniba, a buwayi mutun dashi, yaya nasan abu ba Allah ne da manzonsa suka wajabta mana shiba, ace in zauna a cutar dani.”
Cikin sanyi Waziri ke jujjuya mishi kai a hankali yace.
“Jabeer Garkuwa fa, kake dole ka kare martabar Masarautarmu kana ka nunawa su fulanin da kake Garkuwarsu kai Jarumine”.
Rai a ɓace ganin sufa da gske sukeyi, cikin dakiya yace.
“Bana so, ita wannan sarauta ta GARKUWAN FULANI ku bawa duk wanda kukeso, ni ban nemaba dama”.
Shiru Haroon yayi dan gskya harga Allah shi wannan abun yazo masa a bazata.
Jalal kuwa cikin haɗe fuska yace.
“Wannan ma ai zancen banza ne,
An bawa Ya Jafar Galadima, ko kwana ashirin baiba a kai, aka birkita masa rayuwa, kana yanzu kun likawa Hamma Jabeer wani GARKUWA kun kwasomu kun kawomu Rugar fulani, wai kuna cewa ayi gasar duka dashi.”
Da sauri yayi shiru ganin Jabeer ya ɗaga mishi hannu.
Jamil kuwa tuntuni idonshi ke tsastsafo ruwan hawaye dan gani yake so ake a kashe Hammansu a ƙarar da ƴaƴan ɗakinsu,
Laminu kuwa ɗan Gimbiya Saudatu matar bappansu Sheykh kuma Kani ga Yah Hisham wani irin dariyar jin daɗi yakeyi.

Shi kuwa Lamiɗo, wayarshi ya zaro, Mai alfarma Sarki Jalaluddin ya kira wanda yake kane ga Jabeer. Wanda ya haifi Mamanshi.
Bayan sun gaisane yayi mishi bayanin abinda ke faruwa, jin haka yasa yace ya bawa Jabeer wayar.

A tsakar filin Rugar Bani kuwa, tuni.
Arɗo Bani ya bada dama na suduka yana shekantawa gari cewa.
Ana gamgamin Shaɗi yanzu-yanzu tsakanin Ba’ana da kuma jikan Sarki Nuruddeen.

Tuni an firfito da ganguna anata kaɗe-kaɗe da bushe-bushen sarewa, kana ana buga babban gangan dake tsanar da makotan Rugar Bani sauran rugage alamun za’ayi Shaɗi yanzu.

Kafin kace kobo, Rugar Bani ta cika tayi maƙil da mutane, Maza da mata, matasa da tsoffi, sabida an san duk sanda za’ayi Shaɗi ana bada sanarwar, kwana uku kafin nan to jin wannan na gaggawa kuma da jikan Sarki za’ayi yasa, mutane taruwa, gashi ranar jumma’ace, duk matasan rugogin suna, gida tunda suka dawo sallan jamma’a.
Rugar Bani ta cika tayi maƙil da bani adam, tako wacce kusurwa tsastsafo akeyi kusufa-kusufa.
Jin karan tamɓarin ganganr Shaɗi ne ya ƙara gaiyato mutane harda na cikin garin Shikan, tuni ƙabilun Bonon sun garzayo cikin Rugar Bani.

Bukar kuwa mahaifin Ba’ana shida kanshi yaje, cikin Garkensu ya ɗauko tukunyar tsumin bulalim shaɗin da Ba’ana ke tsumasu da dafin kunamai da sauran sihirurruka, na dodon tsafinsu Bonon.

Matasa majiya karfi ne keta ɗebo ruwa, cikin rijiyoyin garin.
Suna jiƙa taron wurin dandamalin, da za’ayi gasar kaɗe-kaɗen duk sun taru sun cika kunnen kowa.
Jabeer kuwa bugun da zuciyarshi keyi shiyafi komai tada mishi hankali.

A can cikin gidajen Rugar kuwa, duk yan samari da yara sun firfito.
A gidansu Shatu kuwa,
Tunda taji Shelan da Nasuduka yakeyi cewa gasar Shaɗi tsakanin Ba’ana da jikan sarki.
Kuka ta farayi, cikin tashin hankali da kiɗima ta kamo hannun Ummiy da tayi shiru sai ido take binsu dashi, murya na rawa tace.
“Ummiy kijifa, zasuyi ya kashe, wani wanda baijiba bai ganiba, sunfa san illar dake cikin bulalinshi.”
Ganin Ummiy dai ba mgna zatayi ba, yasa ta kamo hannun Junainah cikin tsananin tashin hankali tace.
“Junainah ki gudu, kije kicewa Bappa kada ayi gasar nan, Ni dai a bari na haƙura zan auri ya Ba’ana a yadda yake, zan zauna dashi, zanyi ƙoƙarin gyara mishi, rayuwa na gaji, kada a sake cutar da wani a kaina”.
Da sauri Rafi’a ta kalleta jin ta kamo hannunta cikin zubda hawaye tace,
“Rafi’a wlh ya Ba’ana zai iya kashe mutun a kaina, da dafin kunamai yake tsuma bulalinshi, da wani tsafin, me ribata ayi ta cutar da mutane a dalilina, babu fa wani mahaluƙin da zai iya cin Ya Ba’ana gasar Shaɗi, babu wanda zai iya jurar azabar bulalinshi fa.”
Cikin sauri ta miƙe tare da miƙar da Junainah, sai kuma duk suka koma suka zauna,
Jin muryar maƙocibsu Sarkin aska, yana cewa.
“A a Shatu kada ki tura kowa, kada kuma kije kin tsumayi sakamakon gasar yau in sha Allah zata banbanta da na baya .
Yanzu ma Arɗo Bani ne ya aikoni da in gargaɗeki.”
Yana faɗin haka ya juya da sauri ya fita, kana ya nufi wurin gasar.

Da ido suka bishi. Ita kuwa Junainah da sauri ta miƙa ta nufi kitchin ɗin su, tana cewa.
“Yauwa Adda Shatu, barin in kawo mana gasassun zabbin da Ya Ba’ana ya kawo mana muci.
Ɗazu da nace muci Adda Rafi’a ce, tace mujiraki.”
Cikin sanyi Rafi’a tace.
“Yauwa Junainah kawo mana, muci yau tunda gari ya waye bamuci komaiba.”
Gyara zansu sukayi, kana ta kalli Shatu cikin kula tace.
“Dan Allah Shatu muci abinci, kinga Ummiy ma taƙi cin komai ganin, yadda kiketa kuka tunda kikaji ɓatansu ya Giɗi da rasuwar Ya Lado da Inna.”
Cikin zubda hawaye ta gyaɗa mata kai, sabida ita kanta tasan tana jin wani irin masifeffen yunwa, tamkar zai kasheta.
Da sauri Junainah ta nufosu riƙe da akoshin gasassun zabbin da aka zuba dafin macijin a cikin.

A can cikin tsakiyar garin Rugar Bani kuwa.
Tuni su Ba’ana an gama shiryawa zalumci, domin dama ai a ƙa’ida shi zai fara duka,
Yana tsaye sai zagaya filin yake yana zane iska, makaɗa da mabusa nata yi mishi kirari.

A cikin wurin da Fadawa suka kange Lamiɗo da tawagarsa kuwa, anata kai ruwa rana da Sheykh Jabeer,
Cikin kufula, yake cewa Sarki Jalaluddin da suke waya dashi.
“Nifa babbar matsalarta wannan abun da za’ayi ba *Sunna* bace ba kuma *Farilla* bace, ba kuma *Mustahabbibace*, kai ko a babin *Makaruhi* ban taɓa cin karo da wannan banzar al’adar da kukeso in yarda ayita dani ba,
Ina kuma da yaƙini in da zan bajeta a babin musulunci, kai tsaye za’a iya karhantashi, sabida ai cutar da kaine kuma, Musulunci bai yarda mutun ya cutar da kanshi ba, haka kurum kuce wai in tsaya a zaneni, inji shi kanshi kakan Lamiɗon Joɗo da yaji haza a gasar Shaɗin shine ya hana wannan al’adar a masarautarsa sannan yanzu ace za’a saketa a kaina bayan tsawon shekaru 145 ba’ayishi ba, tun zamanin jahiliyan ma an bar abu sai yanzu ku tara abu a kaina, to wallahi bafa zai yiwuba.”
Cikin kufula Sarki Jalaluddin yace.
“To ya kakeso ayi ɗan masu ilimi kowa jahiline sai kaine mai ilimi sabida tsabar tsoro da ɗan karen son jiki kana gudun abinda zai taɓa lfyarka shine zakayi ta jawo mana wasu dogin falsafofi, a hir ɗin kafa Jabeer ko uwarka bazan sata abu taimin musuba”.
Gaba ɗaya sun hautsuna mishi zuciya,
Ji yadda suketa zageshi, dan kawai yace bazaiyi abinda al’adace ba addiniba sai wani ce mishi suke ko uwarka ko ubanka, bayan sun san baya kuran hakan, rai a ɓace yace.
“Uwata kace ai tunda ita ai ka haifa ba niba ko?, zancen gsky bafa za’ayi wannan abunba, sun daɗe basu ce mana lusaraiba, dolene, sai sun yarda mu fulanine, kai yau nifa ba bafulatani bane.
A kirani da ko wacce ƙabilar ma in anga dama aikin kawai!”.
Yana faɗin haka ya katse kiran.
Laminu kuwa da yake cikekken ɗan jarida, tuni yana naɗe komai a faifai jawaban su.

Shi kuwa Sarki Jalaluddin, ido ya zubawa wayar jin jikan nashi ya katse kiran, murmushi yayi, irin nasu na manya, kana da sauri ya kira, Umaymah.
A can Babba birnin Katsina, kuwa Gimbiya Khadijah Umaymah kenan , wacce take matar ɗan Sarkin Tsinako, Kekkyawar mata mai cikar haiba nitsuwa, tana kishinɗe, bisa wata tattausar doguwar kujera, yayinda Hadimanta biyu ke mata tausa.
Jin wayarta na suwane, yasa ta buɗe idanunta dake lumshe, tunda sukayi waya d, ɗan ta Haroon ke gaya mata inda sukaje da ƴaƴan ƴar uwarta mafi soyuwa a rayuwarsu ne, taketa murmushi.
Ganin sunan mahaifinta ne yasa tayi saurin amsa kiran.
Bayan sun gaisane, Sarki Jalaluddin ya ɗanyi murmushi cikin nitsuwa yace.
“Khadijah, kira ɗan ki, ki bashi umarnin bin umarnin mu, domin yana nuna mana ai bamu muka haifeshi ba, bazamu tirsasashi ba”.
Cikin tarin girmamawa tace.
“Ranka ya daɗe, me kukeso in bashi umarni a kai nasan bazaiyi min musuba”.
Cikin jin daɗi yace.
“Kice dashi ya amince da gasar da za’ayi”.
Cikin sauri tace.
“To An gama yanzu kuwa, in sha Allah zaku sameshi mai biyayya a gareku”.
Daga nan sukayi sallama,
Kana ta kirashi, sau biyu tana kiranshi baya ɗagawa, sabida kanshi ya ɗau zafi yana ganin za’a tirsasashi ya cutar da kanshi.
Ga wani irin azabebben tsinkewa da zuciyarshi keyi,
Ji yake tamkar zata faso ƙirjinsa ta fito, tayi ta tsalle a doron ƙasa.
Gashi duk tsoffin Masarautarsun sun zagayeshi.
Kowa da abinda ke ce mishi.
Ga uban kiɗen-kiɗen dake hawa mishi kai.

Ita kuwa Umaymah ganin bai amsa kiran bane, yasa ta kira Haroon yana ɗagawa tace.
“Ina Jazlaan bashi wayar”.
Da sauri yace.
“To Umaymah uwar Garkuwa gashi nan ido ya raina fata”.
Cikin barkwancinta da yaron nata tace.
“Kaci gidanku Haroon Ni ɗana ba ragobane”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“To mu gani a ƙasa mana Umaymah”.
Yana faɗin haka ya miƙa Jabeer wayar wanda yake cewa Lamiɗo.
“Bafa zan yiba, tsohon nan gwara ka miƙe kaje ayi da kai tunda kaine sarkin Masarautar Joɗa, Ni nan babu abinda na sani bayan nonon uwata sai al’ƙur’ani da hadisai, sai likitancin da kuka sani na karanta a dole badon raina yasoba, tun ina yaro kullum Ni a cikin sani dole kuke da tsabar rainin hankali, kaje a jibgeka, Ni kuwa nayi al’ƙawarin zan jinyaceka, Lamiɗo Joɗa.”
Ya ƙarishe mgnar yana amsar wayar da Haroon ke miƙo mishi cikin faɗa yace.
“Mitsss wai meye kaketa tura min wannan argar wayar taka ne?”.
Cikin mamaki Haroon yace.
“Kan uba Jabeer wayar tawace ma arga, wayar da kuɗi ta sun kai rabin million To inma argace Umaymah ce bisa layi”.
Ba tare da ya kara wayar a kunneba yace.
“Hello Umaymah”.
Cikin tausayi Jalal yace.
“Hamma Jabeer baka kai wayar kunneba”.
Lips ɗinsa ya taune tare da cewa.
“Au, zama su sani yin abu da yawa”.
Haroon kuwa mamaki yakeyi domin karo na forko kenan da yaji Jabeer yace Hello a madadin Assalamu alaikum, da shine abinda yakeyi.
Ita kuwa Umaymah tana jin ya kara wayar a kunne shi ya kira sunanta cikin rauni.
Murya a kausashe tace.
“Jabeer”.
Da mamaki ya amsa dan sama da shekaru goma sha biyu kenan da Jazlaan take kiranshi, cikin sanyi yace.
“Na’am Umaymah”. Cikin bada umarni tace.
“Jabeer ka tashi maza yanzu ka shiga fagen gasar nan ayishi da kai, bana son musu umarnine ba shawara ba”.
Cikin sauri ya zaro siraran kyawawan idanunshi,
Dai-dai lokacin kuma Lamiɗo ya miƙe tsaye cikin tashin hankali da kiɗima da firgici da baƙin cikin dakatar da gasar Shaɗi da akayi a masarautarsu ya sani da anayi da Jabeer bazai ƙalubanceshi ba, cikin sanyi yace.
“Zanje za’ayi dani, zan tabbatar da darajar masarautatarmu bata rusheba.”
Da ido yabi Dottijon kakan nashi wanda a ƙalla ya kai shekaru 91 a duniya.
Cikin kauda kai yace.
“To Umaymah yadda kikace haka za’ayi amman bari in kira Sheykh Abdulkareem in sanar mishi in ya amince dai zanyi”.
Da sauri tace.
“A a ban yafe ka kirashi ba, wato don kasan in ka kirashi zai kira Sitti da Mai alfarma Jalaluddin da Sarki Nuruddeen ya dakatar da duk abinda za’ayin, tunda na san cemishi zakayi ba addini bane, al’adace, to ban yardaba maza tashi”.
Ganin Ya Hashim na miƙa masa wayarshi ne yasashi cewa Umaymah.
To cikin sanyi.
Yana amsa wayar da Ya Hashim ya miƙa mishi yaki Muryar, mahaifinshi cikin sanyi da kuma alamun yana kukane yace.
“Jabeer ashe har kayi girman da Lamiɗo zai umarceka da yin abu kaƙi yi mishi mubaya’a,
Ashe har na haifi ɗan da zai ja da mahaifina.”
Cikin sanyi da rauni yake jujjuya kai murya na rawa yake cewa.
“A’a Abba, kayi haƙuri kada kayi kuka a kaina.”
Bai kulashiba yaci gaba da cewa.
“Jabeer Ashe zuciyarka har tayi tauri da kangarewar da kanaji kana gani za’a daki mahaifina a gaban idonka, bazaka zame mishi GARKUWA ba, Jabeer wannan shine tukuicin tsantsar son da mahaifina keyi muka, wanda har ya jazamin ƙiyayya a wurin yan uwana sunaga ya fifitaku kan sauran jikokinsa Especially ma kai Jabeer komu daya haifa baya nuna mana son da yake nuna maka, shine zaka bari a dakeshi mutun mai shekaru 91 da ɗaya a duniya kai me shekaru 30 bazaka iya zame mishi GARKUWA ba?”.
Cikin rauni da ƙunar zuciya, ya miƙe tsaye hannunshi yasa ya kamo na Lamiɗo cikin tarin ƙuna da zafin rai da takaici yace.
“Na Amince, zanyi gasar na yarda, ka koma ka zauna”.
Wani irin farin ciki ne ya ziyarci, zuƙatansu gaba ɗaya, sai dai kowa da irin manufar farin cikinsa.

Jin haka yasa fadawan janye labulen da sukayi musu.
Shi kuwa Lamiɗo hannunshi yasa ya kamo hannun Jabeer, cikin tsantsar farin ciki da al’fahari da ƙasaita ya fara taku, suna ratsawa cikin taron.
Kana fadawansu na biye dasu a baya.
Ɗanzagi yana.
“Takawarka lfy Sarki mai daraja Lamiɗo ɗan Lamiɗo jikan Joɗa. Gyara kimtsi”.
A haka har suka isa cikin asalin dandamalin da aka jiƙashi jilak da ruwa, sabida hana ƙura wanzuwa.

Gaba ɗaya taron mutanen wurin maza da mata manya da yara, Jabeer suka zubawa ido, sabida duk wanda ya ganshi yaga sahihin Balarabe, mai kamala da nitsuwa, uwa uba kima da haiba, ƙwarjini shi ya cika dukkan idanun magautanshi dake wannan yanki,
yayinda masoyanshi ke taraddadin abinda zai faru.
A tsakiyar filin suka tsaya, hannunsu dake raƙe dana juna Lamiɗo ya ɗaga tare da fuskantarta gabas, kana ya juya yamma, ya kuma juyawa kudu da Arewa, sannan suka dawo tsakiyar filin,
Cikin ƙasaita, yace.
“Ga GARKUWAN FULANI, kuma daga Wannan nasarar da zaiyi a gasar nan,
Zai tabbatar GARKUWAR Masarautar Joɗa, GARKUWA kuma mai ikon zama inda yaso a cikin fada”.
Dariya Bukar yayi kana ya ɗaga hannun Ba’ana da yaketa wani abu da ƙirjinshi kamar damisa,
Cikin isa da yaƙini da al’fahari yace.
“Mu kuma ga namu Garkuwan, da muke da tabbacin bai taɓa gasa ya faɗiba”.
Sake hannunshi Lamiɗo yayi kana ya juya ya koma ya zauna, cikin rumfar da akayi musu masauƙin.
Al’ƙalin gasar ne yazo tsakiyar taro, kamar ko yaushe, hannun Ba’ana ya kamo, ya ɗaga sama, hakan yasa, gaba ɗaya makiɗa da mabusa suka ƙara sautin kiɗe-kiɗen su, wanda Jabeer ke jinsa har tsakiyar kansa, Allah ya sani, baya son hayani koda dai-dai da ƙwayar zarra ne, ga wani masifeffen fargaba da tsinkewar da zuciyarshi keyi, yanaji tamkar yasa hannunshi ya toshe kunnuwanshi.
Ɗan wani gajeren tsaki yaja sabida Allah ma ya sani baya son kallo, to kuma yanajin yadda idanun mutane ke yawo a jikinshi.

Shi kuwa al’ƙalin gasar, yana sake hannun Ba’ana yazo ya kamo hannun Jabeer,
Da sauri ya juyo ya kalleshi sabida kamo hannunshi da yayi sai yaji tamkar hannun jariri ya kamo dam laushi da taushin fatar, hannun sanyi ƙalau,
girgiza kanshi yayi cikin tausayawa, sabisa, ya za’ayi ace mai wannan taushin hannun fatarsa ta iya jurar azababbun bulali masu masifar zafi.
Ɗaga hannun Jabeer yayi sama.
Yana mai nunawa taron mutanen shi a matsayin dashi za’a gwabza.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, duk abinda akeyi idonshi na cikin ɗan siririn farin galashi mai garai-garai dake liƙe a fuskarshi,
Hannunshi kuma riƙe da carɓinshi, kana bakinshi ambaton sunan Allah.

Cikin tarin mamaki ya kalli,
Al’ƙalin gasar tare dasa hannunshi ya riƙe bakin al’kyabbar jikinshi cikin haɗe fuska yace.
“Me hakan!?”. Cikin saurin rusunar da kai Al’ƙalin gasar yace.
“Za’a cire kayan jikin naka ne!”.
Cikin tarin mamaki ya zazzaro ido waje, a baiyane yace.
“Akan me kenan, suturar da Allah yayi min a matsayin mulmi, in killace kaina, shine zaku yayemin a cikin dubban dubatan mutane?”.
Cikin dakiya Al’ƙalin ya ɗan kalleshi domin kwarjinin Jabeer ya cika masa fuska cikin sanyi yace.
“Allah rene, ƙa’idar gasar ce, ba’ayi da kaya a jikin mutun sai ɗan kamfai, kawai ake bari a jikin mutun”.
Cikin kufula da harzuƙa yace.
“To bada niba, Ni nan Muhammad Jabeer wallahi banyi lalacewar da zan tsaya tsirara a gaban jama’a ba”.
Yana faɗin haka ya juya a fusashe, zai fita cikin taron.
Ganin hakane yasa Galadima, yayi saurin tasowa, kana Ɗan buram na biye dashi a baya, tareshi sukayi tare da kamo hannunshi.

Da sauri suka juyo suna. Kallon gungun wasu matasa wanda suka kece da dariyar ƙeta cikin hausarsu ta ƙabilu suke cewa.
“To ku ɗan naku ko yadda ake gudanar da gasar ma bai sani bane? Ya zaiyi zaton da wannan shigar tasa za’a dakeshi, to ai ko bulali dubu za’ayi mishi ba jinsu zaiba,
Kai Ɗan kazagi, ka gaya mishi nan ba cikin masallaci bane.
Nan wurin shaɗi ne”.
Jiyo hakane ya sa ran dukkan musulman wurin ɓaci.
Sabida sun fahimci kafuraine masuyin wannan zancen.
Galadima kuwa da Ɗan buram sun ɗauka abin wasane, a zatonsu zasu shawo kan Jabeer a sauƙaƙe, amman ina ya tiƙe yace babu wani zinɗiƙin ƙaton da zai sashi ya yaye suturar dake jikinshi.
Dariyar da su Arɗo da sauran mutane keyine ya hautsuna lissafin Lamiɗo.
Cikin harzuƙa ya taso, har kamar zaiyi tuntuɓe ya nufi inda su. Waziri, Wambai, Ɗan buram, Ɗurɓi, Da Galadiman, cikin tashin hankalin alamun akwai wata babbar manufa da Galadima ke son cimmawa cikin lamarin ya riƙe hannun Jabeer tare da cewa.
“Haba Jabeer kai wanne irin mutun ne mai kafiya da taurin kan tsiya, yaya muna binka kana zillawa, muna haɗaka da Allah da Manzonsa amma kana tunzuramu, wallahi da yau sai anyi gasar nan!”.
Cikin tsananin ɓacin rai yace.
“In tsaya a tozarta ni kuke so.
Ayimin tijara kukeso, da wanne idon zan kalli al’ummar Annabi da jiki tsirara”.
Cikin kufula Waziri yace.
“Waya ce maka tsirarane?”.
Murya a sama yace.
“Tsirara ne mana! Tunda sunce wai dagani sai Boxes zan tsaya, ka kuwa san ko Mahaifiyata data haifeni tun ina shekaru shida a duniya bana tsayuwa a gabanta dagani sai ɗan kamfai, tunda nake Mahaifiyata, Mahaifina, Yayuna, Uncles, na Aunty’s na, babu wanda ya taɓa dukana, sabida ban cutar dasu da komaiba bare su hukuntani da duka haka kurum rana tsaka kunce in tsaya a dakeni, na yarda, sannan yanzu kuma ace nai tsirara, kai bafa wanda zan yiwa mubaya’a akan hakan..!.”
Tas! Yaji sauƙan wani irin gigitaccen mari sai dai babu wanda ya ga sauƙan marin sabida suna tsakiyarsu Waziri ne, kuma sauran mutanen garin duk kowa bayan su Waziri suke iya gani.
A harzuƙe ya ɗago kanshi,
Lamiɗo ne ya gani tsaye a gabanshi.
Jan hannunshi yayi da iya ƙarfin shi na tsufa.
Tsakiyar filin suka koma, cikin fushi yace.
“Galadima zoka cire mishi kayan.”
Da sauri Galadima ya motso gabanshi.

Su Waziri kuwa duk suka koma cikin Rufarsu masauƙinsu.
Wani irin tsuma da karkarwa jikin Jabeer ya farayi, tun sanda yaji sauƙan marin.
A take idanunshi nan su kaɗa sunyi wani irin masifeffen juyewa sunyi jazir,
Hatta lips ɗinshi karkarwa sukeyi. Wani irin tarin baƙin cikin da bai taɓa jin irinsa ba a duniya ne, ya lulluɓe masa zuciya.
Koda randa Ya Jafar ɗinsu ya zauce, baiji makamancin wannan ɓakin cikinba.
Ji yakeyi Tamkar ya haɗiyi zuciyarshi ya mace ya bar duniyar kowama ya huta,
Rumtse idonshi yayi da azaban ƙarfi lokacin da yaji, Galadima ya gama komce masaƙalan al’kyabbar jikinshi,
kana ya buɗe shi, yayi ƙasa dashi, har saida ya cire hannayenshi a ciki.
Haroon dake gefensu ya miƙa wa al’kyabbar, kana a hankali ya kuma matsowa gareshi, hannunshi yasa saman kanshi ya ɗage zagayen baƙin abin da yake kan Hiramin, kana yasa hannunshi ya janye hiramin.
Kekyawar fuskarshi ta fito ras, tattausan baƙin gashin kansa dake kwance lib-lib ya baiyana, wanda hakan yasa kaso 70 cikin ɗari na dubban mutanen dake wurin suka zuba ƙwayar idanunsu kanshi, da yawa tasbihi da ta’ajjudin irin kyau da haibar da Allah ma ɗauka kin sarki yayi mishi sukeyi.

Jalal kuwa ji yake tamkar ya rinƙa kurma ihu, Allah yasani baya son abinda zai cutar musu da Hammansun,
Jamil kuwa tuni hawaye yake zubdawa,
Ya Hashim, Imran, Sulaiman, kuwa dukkansu sunkuyar da kawunansu sukayi ƙasa.

Laminu kuwa wani irin masifeffen jin daɗi yakeyi, hakan yasa ya ƙara kutsowa cikin filin hakan ya bashi daman yin viewing da kyau.

Shi kuwa Jabeer tafarfasar da zuciyarshi keyi yayi masifar tsananta lokacin da yaji, Galadima ya zare mishi tattausar rigar shaddar dake jikinshi.
jin yasa hannunshi yana shirin zare mishi singlet ɗin jinshi ne yasashi, ƙara ambaton sunan Allah da sauri-sauri, sabida ji yakeyi tamkar ya buɗe ido ya shaƙo moƙoshin Galadima sai ya sumar dashi, tabbas da ace al’ƙalin gasarne ke cire mishi kaya da tuni ya daku.
Cak ɓari da karkarwan da jikinshi keyi ya bari,
Lokacin da yaji Galadima yasa hannunshi ya kwance zariyar dogon wondon jikinsa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani’imanwakil.
Allahumma ajjirni fi musubati!!..”
Ƙasa idawa yayi, jin an saɓule wondon jikinsa yayi ƙasa,
da ƙarfi ya buɗe kwayar idanunshi da suka koma tamkar garwashin wuta. Tafarfasar da jininshi keyi shine abu mafi tartsatsi a rayuwarsa.
Hannunshi Galadima ya jawo da ƙarfi wanda dole yasa ya ɗaga sawunshi ya tsallake wondon ya zama babu komai a jikinshi dagashi sai Boxes wanda Allah yayi mai ɗan tsawone yazo har kusa da guiwarsa saidai a matse yake.

A tsakiyar filin ya tsaidashi kana ya juya ya koma ya zauna kusa da Lamiɗo.
Jalal ne ya sunkuya ya ɗauki wondon da sauri ya miƙa wa, Haroon.

Shi kam Jabeer zuwa yanzu,
Ya sani a duniya ba’a taɓa yi mishi tozarci sama da wannan ba, ji yakeyi a duk faɗin duniya babu garin daya tsana sama da garin Rugar Bani, bai taɓa jin haushi da tsanar wani abu a duniya ba sama da mutanen garin Bani, ji yakeyi ya tsanesu gaba ɗayansu, ya tsani komai nasu, baya so da fata da sha’awan komai nasu.
ƙasar garin ma da yake tsaye a kai ya zuba mata ido ji yake tamkar ya ƙonata ta sauya launi daga farin yashi zuwa baƙin yashi.

A tsakiyar taron kuwa, da sauri al’ƙalin gasar ya jawo hannun Ba’ana da ya zaro wata asirtaciyar bulalar tsamiya, daga cikin randar bulalinshi
sai wani motsi bulalar keyi tamkar tanada rai.

Bayan Jabeer al’ƙalin gasar ya kawoshi. Yana sake hannunshi masu busar al’gaita da sarewa suka farayi da ƙarfin su.

Lokaci ɗaya kuma ranar data take buɗe tarwal ta lumshe.
Mutanen kuwa sai tasowa da ife-ife akeyi. Kallo kuma kab ya dawo kan farar kekyawar fatarshi da kekyawan baƙin tattausan gargasa yayi mishi ƙawanya, iya kyan fatarshi kaɗai ya ishi ɗan adam kallo.
Da ƙarfi Jabeer ya taune lips ɗinshi, yana maiji tamkar zai hudasu sai ambaton sunan Allah yakeyi, babbar yatsar ƙafarshi ta dama yasa yana caka ƙasar garin, kana yatsunshi na hannun kuwa yasa babban yana zagaye kan ƴar manuniyarshi.
A yadda yake jin zafi da ƙuna da baƙin ciki a cikin zuciyarshi ya tabbatar babu wani abu da za’ayi mishi a yanzu yaji zafinsa fiye dashi, to me za’ayi mishi mai zafi sama da tsiraiceshi da akayi.

Ba’ana kuwa cikin dariyar mugunta da sautin amo mara daɗin ji, ya taƙar-kara ya ɗago bulaliyar asirin nan, da iya ƙarfin shi ya zabga mishi ita a tattausar fatar tsakiyar bayanshi.
Da ƙarfi su Jalal kab suka rumtse idanunsu.
Lamiɗo kuwa wani irin kallo yayiwa Jabeer da yayi.
Wani ir…..!

 

Biya darinki uku kacal domin jin wannan labari har ƙarshe.
Dan Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina.

Wannan shafin nakune gaba ɗaya waɗanda suka karanta FREE PAGE🤝🏻😘🥰

 

 

By
*GARKUWAR FULANI*
By
*GARKUWAR FULANI*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button