Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 17

Sponsored Links

*GARKUWAR FULANI* Ido Laminu ya rumtse da ƙarfi.
Ganin Sheykh Jabeer yayi wani irin tsayuwa na ingarman, jarumin namiji nitsuwa da kamala, sai lips ɗinshi dake motsawa a hankali yana ambaton Allah.
Shi kuwa Ba’ana cikin tsantsar mugunta, ƙeda, da zalumci ya ɗago bulalar nan da azaban karfi ya zabgawa mishi ita a inda ya zabga ta forko.
Wanda yasa gaba ɗaya mutanen wurin suka rumtse idanunsu.
Especially Lamiɗo da tawagarsa,
Shi kuwa Sheykh Jabeer, zuciyarshi ta rigada ta gama tafasa, idonshi baya ganin komai sai wani irin azabebben duhu, kunnuwanshi basa jin komai sai sautin muryar mahaifinshi da kuwa Umaymah. Da suke bashi umarnin cewa dole yayiwa Lamiɗo mubaya’a.
Wani irin azaba mai girgiza ran mutun a jikinsa yakeji yana sukarshi har cikin ƙahon zuciyarshi, sai dai duk wani sihiri na jikin bulalar duk baya tasiri a jikinsa illa dai dafin kuna min kam tabbas yana jinsu.
Barmuji wanda shine al’ƙalin gasar kuma mai irga bulalin.
Da sauri ya rumtse idanunshi lokacin da Ba’ana ya tsulawa Jabeer bulala ta biyar waccee, a take jini ya fara tsastsafo duk inda ta konta.

Arɗo Bani kuwa da Bappa da Alhaji Haro da Alhaji Umaru, da Sarkin aska, da sauran dattawan garin da kewayensa wani irin fargaba ne da taraddadi mai firgitarwa suke ciki.
Gaba ɗaya bakunamsu addu’o’in ne a ciki.

Laminu kuwa tuni yanata ɗaukar duk abinda ke faruwa a ƴar ƙaramar na’ura sa. Yanayi yana dariyar farin ciki.

Related Articles

Jalal kuwa da sauri ya rumtse idanunshi kana ya koma baya.
Jamil kuwa cur-cur yake zubda hawaye ganin yadda jini ke tsastsafo wa, a tsakiyar bayan Hammansun.
Haroon da kanshi tsoro ya rufeshi, yaji ranshi ya fara zargin anya kuwa bada biyu aka haɗa wannan gasarba.

Muryar Barmuji ce ta cika wurin gaba ɗaya da alamun tsananin tausayawa yace.
“Goma!”.
Alamar anyi mishi bulala ta goma kenan.
Shi kuwa Sheykh Jabeer Idonshi a buɗe suke, sai dai basa ganin komai sai duhu na tsantsar baƙin cikin abinda sashi yayi cikin bainal nasi a sashi tsayuwa da ɗan kampai,
Idanun nashi suna buɗe ras.
Launin su kuma ya sauya daga farin zaiba, zuwa jazir tamkar wanda maciji ya watsa dafi a cikinsu.
Gaba ɗaya fararen faratun yatsun hannunshi sun rine sunyi jazir tamkar wanda aka ƙunsawa jan lalle.
Ji yakeyi tamkar tsikarinshi akeyi da bakin allurai.
Tabbas duk da bai san dafin kunama ko macijiba, ya gane cewa akwai gubar dafin wani abu a jikin bulalin da ake tsula mishi tamkar za’a zare ranshi dasu.
duk ta inda hudar gashi yake a jikin shi, ji yakeyi tamkar ana soka mishi ƙarin kunamai.

Bukar kuwa, wani irin murmushin farin ciki yakeyi, ji yakeyi kamar ya fito ya taka rawa dan farin cikin ganin halin da jikan Sarki ke ciki.

Muryar na rawa Barmuji yaci ga da irge.
“Goma sha ɗaya! Sha biyu! sha uku! sha huɗu! sha biyar!!!.”
Cikin sauri Haroon ya iso inda suke, hankali a tashe ya kamo hannun Barmuji cikin sanyi yace.
“Kai kasheshi zakuyi ne? Bulalin har nawa ne za’ayi?”.
Cikin rawan murya Barmuji yace.
“In sha Allah bazai mutuba, bulali Hamsin za’ayi a ƙa’idar gasar, ba abinda zai sameshi tunda har gashi ya juri bulali 15 wanda a tarihin gasar Ba’ana babu wanda ya taɓa jurar koda bulala biyar ne”.
Da ƙarfi Hashim ya zaro ido tare da cewa.
“50 wannan ai zalumci ne”.
Da sauri Galadima ya miƙa ya nufi tsakiyar taron ganin Jalal ya nufi inda suke gadan-gadan bisa dukkan alamu kamo hannun ɗan uwan nashi zaiyi yaja su tafi.
Da sauri Galadima ya kama hannunshi cikin ɗaga murya yace.
“Kai Jalaluddin ina zakaje?”.
Cikin faɗa yace.
“Zan ja ɗan uwana mu tafi, in ku bakwa sonshi bakwa da buƙatar shi, mu muna sonshi munada buƙatar shi, a rayuwarmu domin mu dai shine farin cikinmu, shine silar zamanmu cikin masarautarku, da tuni kun koramu tamkar karnuka, shine kuka haɗa Deel a kashe mana shi, to kuji ku sani zamu bar muku masarautarku in dai ganinmu ne bakwa tson yi.”
Cikin faɗa Galadima yaja hannunshi yaje ya ajiyeshi gaban Lamiɗo.
Yana mai jin tausayin yaran.
Da ƙarfi Barmuji yace.
“Ashirin da biyar! Ashirin da shida!”.
Zuwa wannan lokacin gaba ɗaya jikin Al’Sheykh Jabeer Habeebullah yayi ruɗu-ruɗu. Tuni farin boxes dake jikinshi ya cika da jinin dake gangarowa ta bayansa da cikinsa, inda bulalin suke taɓawa duka.
Babbar yatsarshi ta ƙafar damanshi da yatsun hannunshi kawai yake motsawa, wanda suke nuna alamun yana nan da rai daram da kuma haiyacinsa.
Bayan wannan babu abinda yake motsawa a jikinshi,
Cake ƙasar garin yakeyi da yatsar kafar tashi.
yatsun hannunshi kuma, motsasu yake yana tasbihi dasu, wanda shima cikin zuciyarshi yake ambaton Allah dayi mishi kirari da kyawawan sunayenshi.
Zafin da yakeji a jikinshi tabbas ya wuce zaton mai zato.
Taune lips ɗinshi na ƙasa yayi da fararen haƙoranshi tamkar zai hudasu, sai dai har cikin ƙashin haƙoran nashi yake jin azabar dafin dake cikin wadannan bulalin masu masifar siddabaru, sai dai babu wani siddabaru da yayi tasiri a kanshi ko a jikinsa domin shi Allah ya riƙe, Ba’ana kuwa tsafi ya riƙe.
Wannan gasace tsakanin gsky da ƙarya, bawai gasar caɗi bane kamar yadda mutanen wurin ke kallo.
Haka yasa duk da safin wannan bulalin sam basu kai zafin da yakeji a ranshi na sashi ya tsaya gaban dubban al’ummar garin da ɗan guntun wonɗo a jikinshi ba.
Allah ya sani shi mai kunya ne, kuma shi mai suturce kanshine, shida kanshi yana jin kunyar kanshi da kanshi.
Baya zama haka ko a ɗaki sabida yana tuna in mafa ya kaɗaice yana tare da Raƙib da Atib Mala’iku makusantan ɗan adam, wanda in ka bar tsiraicinka ma su kauda ido sukeyi daga gareka.
Shiyasa shima yake kauda ido daga kan kanshima bare wani.
Allah ya sani babu wani abu da aka taɓa yi mishi a duniya ya ƙona mishi rai sama da wannan abun.
Tabbas da an barshi hakama, yafi jin zafin hakan sama da waɗanan bulalin.
A ranshi yake wani irin kuka mai cin rai yana mgnar zuciya.
“Anci min zarafi an wulaƙantani an tozarta ni a gaban waɗan mutanen da wasun cikinsu zindigan kafuraine. An barni tamkar mara kima da galihu, wannan shine iya maƙurar zalumcin da akayiwa rayuwata a karo na biyu”.
Sam baya jin zuciyarshi tanada raunin da zai iya zubda hawaye kan bulalin nan shiyasa ko zafinsu bai zame mishi abin zubda hawaye ko ihu da bakiba ko gudu ko wani motsi.

Zuwa yanzu hankalin kafuran ƙabilar ɓachama ya yi masifar tashi domin wannan shine karo na forko a rayuwar tarihin Ba’ana da ya zana mutun bulalin shaɗi har talatin da takwas baiyi ihuba bai zubda hawayeba, bai sumaba, bai faɗi ba, bai guduba.
Kai wannan abun yayi tsamari wannan wanne irin mutum ne, anya kuwa mutun ne ko al’jan.

Ya Salmanu kuwa, cikin tsanani kuka cur-cur da hawayenshi sabida yasan azabar da Sheykh Jabeer yakeji.
Juyawa yayi ya fuskanci gabas, sujjada yayi tare da fashewa da wani masifeffen kuka mai cike da rauni murya na rawa yake cewa.
“Ya Haiyu ya ƙaiyum, ya ziljalali wal ikram. Ya Allah ka ƙarawa wannan bawa naka dauriya da jarumta, ya Allah ka bashi ikon jure wannan azabar, ya ubangiji ka sanyaya mishi masifun dake jikin waɗanan bulalin, ya ubangijin taliƙai ka hana wannan mugun mushirkin bawa naka samun nasara, ya Allah ka kare musulminka kan wannan kafurin matsafin da baya salla”.
Kuka sosai ne yaci ƙarfin Ya Salmanu.

Bappa ma wani irin raunine ya rufeshi tabbas kowa zaiyi tunanin Jabeer yana jin azabar duniya.
Sai dai kasan cewarsa Jarumin namiji haka yasa babu wata alama da ya nuna na yana jin zafi ko ciwo.
Sosai kuwa hakan ya tada hankalin kafuran.

Lamido da Galadima kuwa kallon juna sukayi tare da yin murmushi irin nasu na manyan fada, murmushi ne mai manufofi.

Jalal kam kife kansa yayi a cinyar Lamiɗo ya saki kuka mai sauti.

Haroon ma hawaye yakeyi zuwa yanzu.
Hankalin duk tawagar Lamiɗo yayi masifar tashi, ganin yadda wani irin azabebben zufa ya tsinkowa Jabeer tun daga tsakiyar kanshi, zufar nan take gangarowa har kan jikinshi gaba ɗaya, saida ya jiƙe yayi jilak tamkar an kwaza mishi ruwa bokati ɗaya.
Wani irin karkarwa jikin shi, ya farayi yana tsuma yana ɓari, gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi.
wanda duk fulanin wurin suka fahimci cewa tabbas.
Zai iya cinye gasar zai kuma iya faɗuwa.

Shi kuwa Sheykh Jabeer daga can cikin naman jikinshi yake jin jikinshi na rawa tamkar mazari.
Zuciyarshi kuwa wani irin duka takeyi, wanda muddin kana kusa dashi zakaji yadda take bada sautin harbawa.

Hankalin Ba’ana yayi ƙololuwar tashi, ganin har yayi mishi bulala ta arba’in da biyar.
Baiyi ɗaya daga cikin ababen da zai hanashi cin gasar ba.
Ganin hakane ya juya a fusashe, bulalin hannunshin ya wurgar kana ya sunkuyo kam ranɗar bulalin tsafinshi, bulali biyar ya zaro, ya haɗa su ya damƙesu cikin hannunshi.
Cikin azaban ƙarfi ya ɗagosu ya yarfawa Jabeer su a tsakiyar kanshi.
Wani irin azabane ya ziyarci ƙoƙon ranshi, wanda hakan yasa yaji wani irin fitsarin azaba yana cika mishi mara.
Jinine ya tsinko ta kafaɗunshi, yana bin cikinshi,
bai gama jin azabar waɗannan ba ya kuma zarma mishi su a cinyoyinshi.
Da sauri Arɗo Bani ya miƙa tsaye daga sujjadar da yayi jin ihun mutane, suna cewa.
“Ka karya dokar gasa ba’a haɗa bulali biyuma bare biyar kasheshi zakayine.
Cikin wani irin isa ta jarumta da jinin sarauta Sheykh ya buɗe kwayar jajayen idanunshi,
Barmuji da yayi kansu da nufin kama hannun Ba’ana ne,
Ya ɗagawa hannunsa alamun daka dakatarwa alamun ya tsaya kada ya iso ya bar Ba’ana yayi komai ba komai.
Cikin tsananin mamaki duk al’ummar wurin suka zuba musu ido ganin jarumta ziraran miraran tana tsaye da sawunta.
Shi kuwa Barmuji cikin rauni yaci gaba da nufosu yana cewa.
“A a Sheykh bazan barshi ba, ai ya karya ƙaida da dokan gasa”.
Ya ƙarashe mgnar yana isowa inda suke.
Cikin tsananin takaici da firgicin ganin faɗuwa a karo na forko na rayuwarshi, Ba’ana
Ya zargawa Barmuji bulalin da ƙarfi.
Wani azabebben ihu Barmuji ya narka tare da fara tsalle yana yarfa hannunshi yana zagaya wurin hawaye na shatata mishi sabida azabar da yakeji, cikin ihun azaban bulalin da aka yarfa mishi sau ɗaya, fitsari na tsiyaya a sawunshi yace.
“Arba’in da takwas!”.
Ta gabanshi ya dawo ya shauɗa mishi na arba’in da tara, wanda yasa Jamil yin tsalle yazo gabanshi cikin kuka yace.
“Kasheshi zakayi ne?”. Cikin tsananin azabar da yakeji ne ya buɗe jajayen idanunshi ya kalli ta inda yaji muryar Jamil.
Hannunshi yasa ya ture Jamil gefenshi.
Shi kuwa Ba’ana wani irin ihu yayi tare da buga tsalle yayi sama kana ya zabga mishi bulala ta hamsin kuma ta ƙarshe.
Wani irin dogon numfashi Jabeer yaja tare da buɗe idonshi kan fuskar Lamiɗo daya iso hango dishi-dishinsa yana nufo inda suke.
Wani irin ihu da karaji Ya Salmanu ya kurma da azaban ƙarfi,
Wanda ya haɗe ya gauraye da busar sarewa da al’gaita da dukan gamgar jami, aka saki a tare.
Wani irin sowa da ihu da hargowane ya cika illahirin gaba ɗaya Rugar Bani,
Wanda mutane fulani suketa rawan farin cikin jarumtar Jabeer,
Arɗo Bani da sauran dattawan rugar kuwa gaba ɗaya sujjadar godiya sukayi wa Ubangijinmu sarki gagara misali.
Gaba ɗaya an zagaye Sheykh Jabeer.
Wanda shi kuma ya juyawa Haroon baya alamun yasa mishi suturarsa.
Da tsananin rawan jiki.
Haroon ya wore al’kyabbar, ya zura mishi ita kan jikinshi daketa zubda jini.
Yana jin Haroon ya saka mishi Al’kyabbar ya ɗago kafaɗunshi ya gyara zaman al’kyabbar.
Jiki na rawa yasa hannunshi ya kama gefe da gefen bakin al’kyabbar ya hadesu a jikinshi ya suturce kanshi ya kare kanshi.
Barmuji na shirin kamo hannunshi yayi maza.
Ya ɗaga mishi hannunshin kana ya juya ya nufi inda motoncinsu ke jere.
Jalal da na ganin haka yayi maza yayi gabanshi.
Marfin motar ya buɗe mushi tun kafin ya iso.

Cikin taron kuwa, tuni Ba’ana da matasan ƙabilar ɓachama, sun ɗauki ranɗar bulalin tsafinshi sun nufi Bonon da tarin baƙin ci dan ganin Sheykh Jabeer bai faɗi gasarba, kuma ga mutanen fulani daketa yi musu dariya da ihun rashin nasarar su.
Hakan yasa suka tafi dan sun sani a ƙa’ida sai Jabeer yayi jinya ya worke da azabar da Ba’ana ya shayar dashi kafin ya dawo ɗaukar fansa.

Cikin taron kuwa cikin kukan rauni Arɗo bani ya rusuna gaban Lamiɗo da tawagarsa murya na rawa yace.
“Sauran ɗaukar fansar da zaiyi a duk sanda ya worke a duk sanda yaga dama, fatana kuyi shirya bulalin tarihin masarautarku, domin ramuwa akan wancan taƙadirin da baya jin koda harbin bindiga baya shigarsa.
Ina yakun farin cikin nasarar da Jabeer yayi a yau, ina kuma fatan yayi nasara a ramuwar da zaiyi a wannan kuma in yayi nasarar mu zaku taya farin ciki, ko ba komai zamu rabu da wancan taƙaɗirin.”
Cikin wani irin tarin ƙuna Lamiɗo ya gyaɗa kanshi.
Kana ya juya yayi gaba Dogari na rike masa da laima ɗanzagi na cewa.
“Gyara kimtsi, a bada hanya, sarki ya barku lfy”.
Waziri da Wambai Ɗan buram Ɗurɓi Da iya duk suka mara mishi baya.

Hakama Arɗo Bani da sauran dottawan wajen sukayo musu rakiya.
Sheykh Jabeer kuwa.
Yana tafe Galadima na biye dashi a baya. Haroon kuma na gefenshi.
Suna isa yasa kai ya shiga cikin motar,
kana Haroon da Hashim suka mara mishi baya, da sauri sarkin mota ya maida ƙofar ya rufe.
Kana ya buɗewa Lamiɗo motar, gefen bayansu Jabeer ya shiga, kana Galadima ya shiga kusa dashi, sannan aka rufe motar saura duk kowa ya shiga motar da yazo ciki.
Sannan duk suka rurrufe motocin.

Kana suma Fadawa da dogarai suka shiga nasu motoci biyun.
Ɗaya tayi gaba, sauran motocin suka bisu a baya, ta Lamiɗo na tsakiyarsu, kana ɗaya ta fadawan ta biyo bayan uku da ke bin bayan ta Lamiɗo.

A haka suka ja motocin a jere a jere suka bar cikin Rugar Bani.

Cikin Rugar kuwa kowa ya tafi cikin al’ajabi da farin ciki.
Da yawa gani sukeyi kamar dai Jabeer ba mutun bane.

Sauran dottawan kuwa, zama sukayi cikin fadar bayan sunyi sallan la’asar ne, Bukar yazo ya tsaya tsakiyarsu cikin rashin mutunci yace.
“Kuyi kuka da kanku akan duk abinda zai faru gaba”.
Kafin ma su bashi amsa tuni ya juya ya tafi.

Su kuwa nan sukaci gaba da al’ajabi da tuanjidin Jarumtar Jabeer.

A cikin motocin kuwa, mutanen ko wacce mota da abinda kowa ke tunawa.
Wani irin azabebben gudu sukeyi tamkar zasu tashi sama, sabida bin umarnin Lamiɗo wanda shi kuwa ya bada izinin gudun ne, dan ganin yadda Jabeer keta zubda jini, ga wani irin masifeffen karkarwa da jikinshi keyi.

Gudu sukeyi a 360 musamman ma da suka samu suka hau kan babban titin Shikan wanda zai sadasu da cikin babban birnin Ɓadamaya.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, wani irin karkarwa jikin shi keyi, idanunshi jinsu yakeyi tamkar zasu zazzago su faɗo ƙasa, sabida wani irin masifeffen azaba da yakeji.
Ji yakeyi tamkar ya haɗiyi zuciyarshi sabida masifar fushi da harzuƙa da zafin rai,
babban abinda ya tsananta fushinsa shine yadda yaga lokacin sallan la’asar ya gota musu,
akan shirmen banza da wofi da zalunci an hanashi yin salla kan lokacin ta.
Hannunshi yasa ya fizge rigarshi da ke hannun Haroon dake ta sa hiraminshi yana tare jinin dake zubomishi ta ƙeyanshi.
Taune lips ɗinshi yayi tare da sa hannun shi, ya kama wuyan rigar cikin ƙarfi yaja ji kakeyi,
Fasss sautin yagewar sabon saddan.

Ido suka zuba mishi gaba ɗayansu,
Ya Hashim kuwa jiki narawa ya kira Dr Aliyu wanda yake ƙanine ga mahaifinshi da kuma Abbansu Jabeer ɗin.

A can baya kuwa inda Galadima dake zaune gefen Lamiɗo ne daya bashi umarnin ya kira sarkin gida ya sanar mishi ayi tanadin jinyar Shaɗi cikin gaggawa.
Da sauri Galadima ya zaro wayarshi ya kira sarkin gida.
Cikin tashin hankali yake mgna a woya bisa alama duk da sarkin gida yake mgn.
“Ladodo, kayi maza yanzu ka sanarwa tsohon sarkin Shaɗin masarautar Joɗa yayi maza ya haɗa tsumin igiyar bulalin shaɗi, ya kaiwa Jakadiyarsu Jabeer,
A shirya duk wani abun buƙata, domin Jabeer yana zubda jini sosai.”

A can masarautar kuwa Sarkin gida yana jin haka ya miƙa ya nufi, sashin kananan sarakuna kai tsaye gefen Sarkin Shaɗin ya nufa, ya sanar mishi umarnin da aka bada,
ai nan take Sarkin Shaɗin da sarkin Gida, suka shiga bayan sashin mai martaba Lamiɗo,
inda bishiyoyin tarihi dana gargajiya da magunguna suke.
Forko bishiyar Goruba suka fara sassaƙan jikinshi.
Wanda shine babban makarin dukan shaɗun.
Sai kuma suka haɗa da wasu tsirran,. Koda suka gama kai tsaye gefen Jakadiya da sauran ma biyanta suka nufa,
Nan suka bata dukkan abinda suka ɗebo, suka kuma yi mata bayani.
Kana sukace maza ta haɗa su ta dafa,
Sauran kuma sai sun dawo Lamiɗo ya shiga ɗakin sirri ya ɗebosu.

Cikin tsananin tashin hankali da rawan jiki Jakadiyarsu ta amshi magunguna, ta nufi sashin Jabeer ɗin.
Cikin gaggawa ta shige kitchin ɗin shi, ta fara harhaɗa magunguna tana dafawa.

A can cikin motar kuwa cikin tashin hankali Ya Hashim yayiwa Dr Aliyu duk bayanin abinda ya faru da halin da Jabeer ke ciki.
Ya ƙara da cewa, a shirya komai na bashi taimakon gaggawa.
Jin hakane yasa Dr Aliyu tada motar Ambulance wanda take nan cikin asibitin dake cikin makarantar nasu, tazo bakin asalin babban gate ɗin masarautar nasu.
Kana ya kira babban abokinshi Dr Sanju wanda ba indiyene wani aikine ya kawoshi ƙasar,
tuni suka iso bakin gate ɗin, cikin motar Ambulance ɗin suka shiga suka zauna tare da haɗa duk wani abu na taimakon gaggawa da za’ayi mishi.

A cikin motar kuwa, gaba ɗaya ya gama yage rigarsa ya fizge wonɗonma ya yageshi fata-fata.
Ganin wani irin kallo da yayi Haroon ne, yasa Haroon yin maza ya matsa tare da yin mgnar zuci.
“Ka gani ko Lamiɗo hegen tsoho kai ka dace ka zauna kusa dashi.
Inma yagawarne ya yage ka”.
A zahiri kuwa fuska ya ɗan haɗe tare da cewa.
“Kafa gama yaga kayanka yanzu nawane suka rage a jikina, naga ji kake kamar ka yagamu, yaseen to bamu muka kar zomonba”.
Dai-dai lokacin kuma, sarkin ƙofa ya buɗe musu ƙofar babban gate ɗin.
Kana suka kutsa kai. Suna shiga ko parking basu gama dai-dai tawa ba
Jabeer ya sa hannu ya buɗe marfin motar, ƙafarshi ya zuro woje,
wanda ganin haka yasa Dr Aliyu ya fito da sauri.
Sai dai kafinma ya fito tuni Jabeer ya fito cikin motar ya nufi asalin ƙaramin gate ɗin da zai sadaka da asalin cikin farfajiyar.
Kusan a tare suka fito daga motocin gaba ɗayansu.
Cikin tsananin tashin hankali Ya Hashim ke ƙwalla mishi kira, amman ina bai ko juyo inda sukeba.
Baya kuma jinsu sosai sabida duhu da jirin da yake gani.
Da gudu Haroon da Jalal Jamil suka biyoshi a baya cikin rauni Jamil ke cewa.
“Hamma Jabeer dan Allah ka tsaya Baba Aliyu zai dubaka, kaga fa har yanzu jinin bai daina zuba ba.”
Ina ai baya tare dasu tafiya kawai yakeyi, ba tare da yasan inda yake jefa ƙafarsa ba.
Ganin hakane Dr Aliyu ya koma cikin Ambulance ɗin ya jata ya nufi inda yake, sai dai tuni har ya shiga cikin asalin farfajiyar.

Haroon, Jalal, Jamil, Hashim, ɗan Barrister Kamal Sulaiman, da Imran, duk suna biye dashi a baya da dudu-gudu da sassarfa.
Lamiɗo da tawagarsa kuwa, koma sukayi cikin motocin sukaja, suka nufi cikin gidan.

Shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya isa bakin side ɗinshi.
Cikin tsananin rawan jiki da duhu ya kusa kanshi ciki.
A babban falon ya samu Jakadiyarsu, tana ganinshi ta miƙe tsaye cikin tsananin tashin hankali ta tsaya ganin ya ɗaga mata hannunshi ɗaya, kana yasa hannunshi ɗaya kuma ya dafe kanshi.
Cikin wani irin kerma yake wani irin taku da jan wani irin dogon numfashi ya nufi part ɗin shi.
Yana shiga falonshi na musamman, su Haroon na shiga babban falon.

A nan su Jamil kan suka tsaya, shi kuwa Haroon da sassarfa yabi bayanshi.
Yana shiga falon nashi ya hangoshi ya shiga bedroom ɗin shi.
Ya kuma maida ƙofar ya rufe, kai tsaye bathroom ya wuce yana shiga wani irin duhu ya rufe idanunshi a hankali ya tafi…

A can Rugar Bani kuwa, kuwa Junainah har ta shiga kitchin ta sunkuyo zata ɗauki akoshin naman gasassun zabbin, sai kuma ta fito a guje.
Kai tsaye inda ake gasar Shaɗi ta nufa, haka ta rinƙa kutsawa cikin taron, har ta isa gaba-gaba kusa da ya Salmanu, ganin irin dukan da akeyiwa wannan kekyawan mutumin data ganine yasata kuka da ihu.
Kukanta ne yasa Salmanu kuka, ya kuma ja hannunta ya fito baya da ita.
Hannunta ɗaya riƙene yaji yadda jikinta ke karkarwar kamar mazari, bayan yayi sujjadar ya ɗagone.
Yace mata maza ta koma gida.

A haka ta koma tana kuka.

A inda ta bar Shatu dasu Rafi’a da Ummiy anan ta dawo ta samesu.
Kai tsaye kitchin ɗin ta nufa, da sauri ta ɗauko akoshin ta fito ta nufi inda suke, cikin rawan jiki ta sunkuyo ta sauƙe musu akoshin ta ajiye a tsakiyarsu, kana itama ta zauna a kusa da Ummiy dake jingine da jikin bishiyar mangoro.
Jiki na rawa tasa hannun ta janye fefeyin da aka rufe akoshin da shi.

Wani irin lumshe ido Rafi’a tayi, sabida wani irin ƙamshin daya buɗe hancinta,
Ummiy kuwa ido ta zubawa akoshin tana jin yawun bakinta na tsinkewa,
Shatu kuwa gyara zamanta tayi sabida wani irin azabebben ƙugin yunwa da cikinta yayi.

Cikin sanyi suka gyara zamansu gaba ɗaya, a hankali Shatu ta riƙe hannun Junainah cikin zubda hawaye tace.
“Jeki wonke hannunki sai kizo, da plet da ƙaramin akoshi mu ɗibawa Bappa mu sawa Ummiy a plet ɗin”.
Cikin sanyi ta tura baki kana ta miƙe tsaye, gindin randunarsu ta matso, yar ƙaramar butarta ta ɗauka ta wonke hannunta, sannan ta nufi cikin madafarsu.

Tana shiga ta ɗauki ludeyi da ƙaramin akoshi kana da pilet sannan ta fito.
Tana fitowa tazo ta zauna gabansu, ta miƙa Shatu, cikin sanyin jiki tace.
“Bawa Rafi’a ta ɗiba musu, wlh jikina duka rawa yakeyi”.
Amsar pilet ɗin Rafi’a tayi ta fara ɗibawa Ummiy rabin zabuwa.
Kana ta sawa Bappa gudar da romonta,
Tana cewa.
“Garkuwa yunwace fa, ace mutun ya wuni ya kuma kwana baici komaiba ya kuwa wuni ba abinda yaci ai dole kiji jiri, gashi yawan kukan da kikeyi ne yasa miki zazzaɓi.”
Ta ƙarishe mgnar tana rufewa Bappa nashi kana tace.
“To muci”.
A tare suka saka hannunsu cikin akoshin.
Junainah ce ta fara yago tattausan farin tsokar ƙundun zabuwar cikin haɗiye min yau ta kai hannunta bakin t….!

 

Dan Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina, in kinsan Zaki fitarne gaya min in baki kuɗinki, dan Allah.

By
*GARKUWAR FULANI*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button