Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 28

Sponsored Links

By
*GARKUWAR FULANI*”To Alhamdulillah. Allah ya kawomu watan Ramadan, wata mai tarin al’farma da al’barkatu da tarin ni’imomi. Mutane da dama Allah bai basu wannan damarba, da yawa sun rasu.
Wasu kuma basu da lfy, basu san me sukeyi ba ko a ina suke, bare su ribaci wannan dama da Allah ya bamu.
An ga wata wanda haka keda tabbacin gobe zamu tashi da azumi.
Duk kuyi niya, ɗaukar azumi talatin ko talatin ba ɗaya.”
Sai ya kuma ya ɗan tsagaita tare da kallonsu Jalal da Jamil cikin sanyi yace.
“Dan Allah Jalal Jamil ku nitsu kunsan halin da muke ciki. Kun san matsalar rayuwarmu kunsan damuwarmu, wannan dama ce da zamu yi amfani da ita wurin tsananta addu’o’in ba dare ba rana.
In sha Allah, Wata rana komai zai dai-dai-ta domin Allahu sami’uddu’a ne.
Jamil kaji tsoron Allah ka ribaci wannan watar, ka raba kanka da zuwa club, ka yayewa kanka masifar nacin liƙewa mata da waya.”
Juyowa yayi ya ɗan kalli Jalal kana yaci gaba da cewa.
“Jalal yawon bin yan iska da wani shegen shiga mara kan gado ba tsarine na Musulmin ƙwarai ba.
Aunty Juwairiyya Hibba Ummi Ke uwar bacci”.
Ya ƙarishe mgnar da kallon gefenda Shatu da take zaune tana ɗan lullumshe ido,
da sauri ta waresu don a sama taji muryar tasa. Baki ta tura tare da sunkuyar da kanta, shi kuma jenye idonshi yayi daga gefen da take cikin ɗan ɗaga sauti yace.
“Watan Ramadan ya bambanta da sauran watanni.
Domin a cikin watanne daren laylatul Ƙadir yake, kuma a cikin watanne Allah ya sauƙe al’ƙur’ani mai girma.
Kana a cikin watar akwai ranakun da malamai sukeyi hasashen a daren laylatul Ƙadir yake, Daren 21, 23, 25, 27, 29. Sai dai ba’a tabbatar, da sahihin rana ɗaya tsayeyye ba ƙauli mafi rinjaye shine ranar 27.
Abi mafi kyau shine kada mutun ya sake koda dare ɗaya na Ramadan ya wuceshi.
Mu raya dararen da ibada da ambaton Allah, wajibine mutum ya tsare bakinsa, da munanan zantuka walau a baki walau a rubuce a social media,
Domin mu ribanci watar da ambaton Allah da samun ruɓanyar lada, wannan abubuwane da kullum nake gaya muku su, sai dai aiki dasu ya gagareku.”
Kusan haɗa baki sukayi wurin cewa.
“In Sha Allah zamuyi ƙoƙarin kiyayewa”.
“Allah yasa yace, tare da sallanmansu duk suka fita sai Ya Jafar da Ummi.

Ganin yadda Hibba keta zuba hamma ne ya sashi cewa.
“Muhibbat tashi
Kije ki kwanta”.
Kusan a tare ta mike ita da Shatu.
da sauri yace.
“Banda ke”. Cikin bacci ta turo baki tare da cewa.
“Ayyah dan Allah fa”.
Murmushi Ya Jafar yayi tare da zuba mata ido.
Wanda koda baya mgna ana iya gano yadda yake sonta a ranshi, so kuma irin son da yakeyiwa su Hibba.
Ummi ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
“A barta tai bacci aiki mukeyi tun ɗazu”.
Shiru bai kulasuba, ganin haka ita kuma tabi bayan Hibba.
A zatonta bai saniba, har sunje bakin ƙofar taji yace.
“Saura ki binƙire kiyi ta bacci, kada ki tashi ki raya daren. Sai gari ya waye ki buwayi mutane da ife-ife da rashin kunya”.
Ya ƙarishe mgnar cikin jin haushinta tare da Binta da kallon fitinenneyar yarinya.

Ganin Ya Jafar ya miƙa ya juya zai fitane yasa yayi saurin.
Bin bayanshi ya rakashi kana ya dawo ya konta.

Related Articles

Ummi ma ta konta.

Ƙarfe ɗaya da rabi Sheykh ya tashi yayi ta nafilfilinshi tare da jere addu’o’in da neman warakar damuwar rayuwarshi data ahlinshin.

Ummi ma tuni ta tashi. Ƙarfe uku ta fito.
Falon hango haske a ɗakun Shatune ya tabbatar mata sun tashi.

Kitchen ta wuce. gas ta kunna ta ɗumama musu miyar, kana ta haɗa plate spoons and cups tazo ta jere bisa Dinning table.

Sannan ta koma kitchen ta ɗauko musu drinks and water masu sanyi tazo ta jere komai yadda ya dace.

Kana ta dawo falon ta zauna riƙe da carbinta.
Ƙarfe huɗu dai-dai su Jalal suka buga ƙofar sanin sune yasa, ta tashi ta buɗe musu.
Suna shiga ana buga bindigar sanarda mutanen masarautar Joɗa cewa lokacin sahur yayi.
Bayan mintuna talatin kuma za’a kuma sakin bindingar.

Cikin gudu Shatu ta fito falon jiki na rawa, kiciɓis tayi da Ummi da takeda niyar zuwa ta ta kirasu suzo suyi sahur.
Ruggume Ummi tayi ƙam-ƙam tare da neman inda zatasa ranta.
Allah ya sani tana tsoron ƙaran abu biyu, ƙaran aradu da walƙiya da kuma ƙaran harbin bindiga”.
Cikin mamaki Ummi tace.
“Oho Aysha duk wannan tsoron na ƙaran harbin bindiga ne, lallai kuwa in baki sababa kafin Ramadan ya ƙare zakisha wuya.”
Hibba ce ta fito tana dariya tace.
“Allah ko Ummi ana ɗaukan alhaƙin Aunty Aysha”.
Babban Falon suka nufo yayinda duk jikinta ke karkarwar.”
Dinning area Suka wuce.
Bayan duk sun zaunane Ummi tace Hibba tasa musu abinci.
Buɗe kulolin tayi.
Jolof ɗin taliya da kifi Aunty Juwairiyya tayi, sai kuma
Flaks ɗin kunun gyaɗa.
nasu kuma tuwon semo da miyar ɗanyar kuɓewan sai tea da sauran kayan sha.
Ta zubawa kowa abinda ranshi keso.
ita dai Shatu mamakin abincin Aunty Juwairiyya na yau takeyi sabida idonta bai gano mata wani mugun abu a cikiba.

Haka yasa itama shi taci. Da kunun.
duk sunyi nisa a yin sahur ɗin. Amman shi bai fitoba,
Sai ƙarfe huɗu da rabi ya fito.
A hankali ya iso Dinning area ɗin gaban washing hand Baby ya ɗan tsaya tare da wonke hannunshi.
Ita kuwa Shatu tana ganinshi ta ɗanyi gyatsa tare da cewa.
“Alhamdulillah kana ta miƙe”.
Kujerar dake gefen Jalal ya zauna,
Yana zama ita kuma ta juya ta nufi cikin falon.
Shi bai ma kalli inda takeba.
Cikin falo ta koma hannunta riƙe da cup ɗin kunun da take sha.
Cikin kula Ummi tace.
“Sai yanzu?”.
ta ƙarishe mgnar tana zuba mishi tuwon semo da miyar ɗanyar kuɓewar da yaji nama da kifi da man shanu.
gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“A jinkirta sahur a gaggauta buɗa baki Ummi Manzon Allah yace.”
Murmushi tayi tare da cewa.
“Hakane”.
Bismillah yayi tare da gyara zaman shi, ya fara cin abincin.
yaci mai ɗan yawa dan daren jiya baici komaiba.
tea ta haɗa mishi.
Hannunshi ya wonke kana ya amshi tea ɗin ya fara sha.
Jalal, Jamil, kuwa ci sukayi sukayi haninƙan kana suka miƙe zasu tafi.
Cikin kallonsu yace.
“Kadafa kuje ku kwanta, kuyi al’wala ku wuce masallaci.”
To sukace kana suka tafi.
Shi kuwa yana gama yin sahur ɗin ya koma Side ɗinsa,
Wonka yayi tare da al’wala kana yayi shigarsa ta farar jallabiya.
Bayan sun idar da salla gari ya ɗanyi hasken ya taso ƙeyansu, suka dawo gida.

Side ɗin su suka wuce. raka Ya Jafar yayi har Side ɗinsa kafin yazo ya shiga sashinsa.
Shiru falon babu kowa, bisa alamu kuwa tuni Ummi ta kimtsa ta share da goge ko ina, ta sassake labulaye, tare da sa turaren wuta mai ƙamshi.
Kana ta kashe hasken ko ina, babu abinda ke tashi sai ƙamshi da sanyin A/C da karatun Alqur’ani mai girma da kuna.

Falonshi ya nufa yana shiga,
ya zauna a falo, Dua Azkar ya fara yi cikin zazzaƙan muryarshi.
Bayan ya isane kuma ya fara karatun al’ƙur’ani. Sai bakwai da rabi dai-dai ya shafa addu’a kana ya wuce bedroom ɗin shi.
Wutan ya kashe tare da ƙara ƙarfin gudun AC.
sannan ya nufi luntsumemen gadonshi ya kwanta bisa gefen damanshi tare dasa hannun ya jawo blanket ya rugu.
A hankali lips ɗinshi ke motsawa, alamun tasbihi yakeyi.
Cikin 13 minute bacci mai daɗin gaske ya kwasheshi”.

Haka can wurinsu Shatu ma, saida tai karatun al’ƙur’ani sosai kafin ta konta hakama Hibba.

Ummi kuwa wonka tayi tayi al’wala ganin bakwai ta wuce ne tayi walahan ta raka biyu.
Kana tayi karatu sai ƙarfe tara da rabi ta konta take kuwa bacci yayi awon gaba da ita.

Ƙarfe goma dai-dai ya tashi daga baccin da yakeyi.
Wonka yayi tare da al’wa kana ya fito ya kimtsa cikin shiga ta al’farma. Turare mai ɗan sanyi ya fesa kaɗan kana.
Ya ɗanyi tafiya kaɗan zuwa gefen Bedside drower’n dake tsakanin gini da gado, wanda akwai tazarar fili mai ɗan faɗi ana yake shimfiɗa sallayarsa wurin ya zama keɓantaccene.
Walaha, yayi raka biyu kana yayi addu’o’in yau da kullum ya shafa, miƙewa yayi ya ɗauki System ɗinshi ya riƙe a hannunshi, kana ya ɗauki woyarshi ɗaya cikin su huɗu da suke bisa Bedside ɗin.

A hankali yake taku, har ya fito tsakiyar falon. Shiru gidan tamkar babu mai rai a ciki.
A haka ya buɗe ƙofar ya fita, tare da ja musu ita ta baya.
Koda ya fito asalin farfajiyar masarautarma ko ina shiru kakeji, sai ɗan zirga-zirgan fadawa da hadimai masu tattara ɗan sharan dake ko wanne bakin part.
Suma kowa a hankali yake aiki alamun akwai bacci tare dasu.
Motarsa kirar Tolls Royce, wacce kuɗinta zai iya kai kimanin Billion 4, 959,630, naira. Baba Lado shine Drevernshi da sauri ya taso yana suka tafi.
Daga nan masallacin jumma’a na kasuwa ya wuce.
Sha ɗaya saura ya isa, inda ya samu tuni masallacin ya cika yayi maƙil da al’ummar Annabi maza yara da manya tsoffi da tattawan, yan kasuwa sun cika sunyi maƙil iso warshi kawai dama ake jira.

Motarshi na gama tsayuwa yan agaji suka rufa mishi baya, babban cikinsu ne ya buɗe mishi marfin motar tare da ɗan rusunawa yace.
“Barka da safiya Malam”.
Cikin tsananin kulawa Sheykh Jabeer ya kalli dottijon da ya kai ya haifeshi.
Hannu ya miƙa mishi tare da cewa.
“Barka dai Baba Sule Ya ibada”.
Cikin jin dadi yace.
“Alhamdulillah”.
Sai kuma ya kalli sauran wanda yawanci bazasu wuce sa’annim ƙaninshi mai binshiba Affan kenan,
Murmushi yayi tare da basu hannun yana mai tuna cewa tabbas da Affan yana ƙasar nan To bana a Ɓadamaya zaiyi azumi, kuma ya sani da yanzu suna tare anan, dan shi ba irinsu Jalal bane.
Zagayeshi sukayi suna buɗa mishi hanya yana wuce.
Ta kofar da liman ke shiga ya shiga.
sit kakeji da yake duk mazane, gashi kuma ansan ƙa’idarshi shi baya son surutu in yana tabsir.
Zama yayi tare da kallon ɗan agajin dake saƙala mishi abin ɗaga sauti mgn a jikin al’kyabbar jikinshi.
Yayinda wasu kuma suka koma bayanshi wasu suka tsaya gefenshi, yan ɗaukan awazin kuma na gidajen Radio da TV duk sun kafa na’ura su a gaban table ɗin da yake zaune.
Bayan an gama kimtsa mishi komaine, ya gyara zamanshi tare da kallon alaramma Abdulƙadir wanda shine zai jamishi baƙi.
System ɗinshi ya buɗe tare da gyara mata zama, haka shima Alaramma Abdulƙadir yayi da Qura’an ɗin gabanshi.

Gyara murya Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero yayi tare da fuskantarta taron al’ummar dake gabanshi cikin ɗan ɗaga sauti yace.
“Bismillah rahmanirrahim. Assalamu alaikum warahmatullahi wa barka tuhu.
Innal hamdalillah nahmaduhu wanasta inuhu wanastagfiru wana uzubillahi min shururi am fusina wa sai’yi ati amalina. Manyahadillahu fala mudillah, famanyuddul fala hadiyala wa asshahu’alla’ila’ha’illalahu wahdahu lasheri kallah, wa asshahadu annamuhammadan abduhu warasulu.
Ya ayu allazina amanuttaƙullaha haƙƙa tuƙatil wala ta mutunna illah wa antum muslimun ya ayu hannasu taƙu rabbakum.
Kalakum min nafsin wahida, wa kalaƙa minha zaujaha wa bassa minhuma rijalan khasiran wa nisa’ah wattaƙullah lazitasa’aluna bihi, wal’arhama innallaha kana alaikum raƙiba, ya haiyu allazina amanutaƙullah wa ƙulu ƙaulan sadidah yuslahlakum amalakum wayagfirlakum zunuba kum, waman yuɗillah wara sulahu, faƙadfaza fauzan azeema ambaduhu fa inna’asdaƙal hadisi kitabullah wa’ahsanal hadi hadiyu Muhammadin (S.A.W) wa sharal umuri muhdasatuha fa innakulla mudasatin bidi’a wa kulla bidi’atin balala wa kulla balaltun finnar.”
Nufamshi ya sauƙe mai ɗan nauyi sabida jan dogon numfashin da yayi, kana ya kalli taron al’ummar musulmi dake zaune gabanshi manya da yara, masallacin yayi maƙil har woje.
Kusan gaba ɗaya taron jamar suka haɗa baki wurin cewa.
“Wa alaikassalam warahmatullahi wa barka tuhu”.
Kanshi ya ɗan rusunar tare da ci gaba.
Gyara masaƙalin abin sautin mgnar dake wuyan al’kyabbar jikinshi yayi tare da cewa.
“Alhamdulillah. Kamar yadda aka saba haɗuwa a wannan masalaci mai Al’barka bana kuma Allah ya ƙaddara dani za’ayi.
Kamar yadda aka fara a wancan shekarar, zan ɗaura a kan darasin da Malam Abubakar ya fara, duba da kasantuwar mafiya yawa yan kasuwa ne, to zamuyi maudu’in bisa haƙƙin tauye mudu, da kuma barin salla ta wuce dan gudun cinikayya ya wuce ka.”
Daga nan ya shiga cikin shirin gadan-gadan.
Yayinda gaba ɗaya mutane sukayi tsit suna jin nasiharsa da hujjoji da yake jawowa daga al’ƙur’ani zuwa ahadisai, yana shigarsu yana ratsa musu jiki, jini, da zuciya.
Musamman dama mutane nason wa’azinshi.
Haka yasa koda lokacin tashi yayi sai suka ga kamar miti biyar sukayi ba awa ɗaya ba.

Yana tashi a wurin yan agaji sukayi mishi rakiya, har bakin motarshi.
Daga nan Masallacin Masarautar Joɗa ya nufa.
Sha biyu dai-dai tayi mishi yana cikin masallacin
tuni an shirya an kimtsa komai yadda abu zai tafi, shiyasa yana isa shida Alaramma Abdulƙadir suka fara.

A can cikin masarautar Joɗa kuwa.
Dai-dai lokacin Shatu ta fito cikin ɗakinta ta nufi falo.
Shiru babu kowa, haka yasa ta wuce kitchen da nufin yin wonke-wonken da sauran gyara-gyare ganin komai tsab-tsab ne yasa ta dawo falonta.
A hankali ta nufi ɗakin Ummi.
daga bakin ƙofa ta tsaya tare da yin sallama.
Cikin kula Ummi ta amsa mata tare da cewa.
“Ki shigo mana”.
To tace kana ta shiga, cikin sanyi tace.
“Ina kwana Ummi”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Lfya lau Alhamdulillah, amman yanzu dai ina wuni ne ko”.
Cikin murmushi tace.
“Eh hakane fa, yanzu har sha biyu da rabi tayi”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ai tunda naji Sheykh ya fara tabsir nace to rana ta tsala”.
Shiru suka ɗan yi tare da kasa kunne, ras muryarshi ke tashi sabida ansa amsa kuwa ta cikin masarautar.
shiru Shatu tayi tare da yin ƙasa da kanta tana mai lumshe ido, Allah yasani tana masifar son tabsir ɗin shi, in taji yana jan baƙi sai take jinta kamar a harami take.
Ummi ce ta ɗan kishin ƙiɗa tare da cewa.
“Gyara zamanki muji wa’azin.”
Kai ta ɗan ɗago tare da cewa.
“Ummi naje kitchen zan mana wonke-wonken na samu an gyara komai ba dai ke kikayi aikinba?”.
Cikin maida hankalinta ga sauraron tabsir ɗin tace.
“Nice nayi, amman daga yau Saratu zata na zuwa tanayi wanke-wanke da share-shere da yan gobe-goben da dai sauran ƴan wasu aiyuka, kamar fere dankali ko doya da tsinkan ganyen ko wanke wake ko jiƙa shinkarfa masa da kai markaɗe, duk itace zatayi mana, mu kuwa in munyi azahar mu shiga kitchen,
zatake ɗan taimaka mana da wasu aiyu kan. Amman banda girki, hadimar Gimbiya Aminatu ce, amman duk azumi nan ake bamu ita”.
Cikin gamsuwa da hakan tace.
“To ba damuwa Ummi, amman dan Allah in ɓata zoba, kada kice zakiyi aikin ki barshi ni zanyi”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Zama tazo, kullum da asuba ana idar da salla zata zo.
In ta gama aiyu kanta kafin ƙarfe goma dai zata tafi, sai anyi sallan azahar kuma zata zo.
Daga nan kuma sai mun gama aikin buɗe baki, ta tafi dana Gimbiya Aminatu da nata, sannan sai ansha ruwa anyi sallan isha’i da asham sai ta dawo tayi yan wonke-wonken da taimaka mana aikin sahur, to in ta tafi kuma sai washe gari in anyi sallan asuba ta dawo.”
Cikin ɗan fito da idonta tace.
“Wannan zirga-zirga haka Ummi to ta zauna anan kawai mana ta huta”.
Juyowa tayi ta ɗan kalleta kana tace.
“Mijinki ba irin waɗannan mutanen bane, baya son a turo mishi yara suzo suyi ta zirga-zirga a kanshi, kinga duk lokutan da take zuwa basa haɗuwa.”
Baki ta ɗan taɓe tare da yin mgna a zuci.
“Kai mutun komai tsari, wannan babu shakka baida gskya ne wannan ɓoye-ɓoyen waya sanima ko cin zan-zanane a jikinshi da saɗaure wata ƙil shiyasa yake kima tabka-tabkan Al’kyabbar ajikinshi dan ya boye abubuwan”.
Murmushi Ummi tayi dan ta lura Shatu bata san mgnar ta fito fili ba.

Shiru Shatu tayi ganin alamun Ummi na jin wa’azin,
Hakane yasa tayi shiru sabida kada ta takura mata.

Ƙarfe ɗaya dai-dai na rana, akayi addu’a aka rufe taron sai kuma Goben in Allah ya kai rai.

Da yawa mutane basu fitaba,
mafi akasari Kur’anai suka ɗauka suna karatu.
Kamar yadda Sheykh yakeyi.

Ƙarfe ɗaya da rabi aka kira sallan azahar.

Miƙewa Shatu tayi tare da cewa.
“Ummi bari inje inyi salla zan zo muyi wata mgna”.
Cikin binta da ido Ummin tace.
“To”.

Bayan anyi sallan azahar an idar ne, ta fito ta nufi ɗakin Ummi, ganin bata nan ne, yasa ta nufi falo, nan kuwa ta sameta zaune bisa kujera.
gefenta taje ta zauna.

Tana zama wata ƴar matashiyar budurwa ta shigo,
cikin nitsuwa tazo ta rusuna gabansu tare da gaidasu, Cikin kula Ummi tace.
“Yauwa Saratu kin zo ko?”.
Cikin nitsuwa tace.
“Eh Ummi nazo ɗazu bakwa nan sai na koma sai yanzu na kuma zuwa”.
Kai ta jinjina tare da cewa.
“Yayi kyau,”. Inda Shatu take ta ɗan kalla tare da cewa.
“Ɗiyata ga Saratu. Saratu ga Saiyada Shatu matar Sheykh Jabeer”.
Cikin mamaki da dariya sunan da Ummi ta liƙa mata wai Sayyada, ta kalli Saratu tare dake gaisheta cikin ladabi da biyayya,
fuska a sake ta amsa.

Cikin sanyi Saratu tace.
“Ummi me za’ayi ne?”.
Gyara zama Ummi tayi tare da cewa.
“Ki wonke shinkafar masa dama na jiƙata, kana ki gyara mana ganyen alaiyahu, sannan ki fere Arish.
Sai kuma ki jajjaga kayan miya, ki yanka al’basa mai ɗan yawa.”
Cikin nitsuwa da bin umarni tace.
“To Ummi”.
Ta ƙarishe mgnar tare da miƙewa ta nufi kitchen, tana shiga ta fara aiyukan da aka sata.

A falon kuwa, gyara zama Shatu tayi tare da kallon Ummi cikin sanyi tace.
“Ummi dama mgnar da zamuyi ko!.”
Sai kuma tayi shiru tana nazari, jin muryar Ummi nace mata,
“Uhum ina jinki faɗi”.
Sunkuyar da kanta tayi a hankali tace.
“Uhumm dama cewa, zanyi in ba matsala a rinƙa yin abun buɗa bakin ana kaiwa masallacin Masarautar Joɗa mana, tunda dole talakawan gari na zuwa nan sallan magriba.”
Murmushi mai yelwa Ummi tayi tare da cewa.
“Allah sarki, Shatu mai tausayi, ba matsala amman ki tambayi mijinki in ya amince dai ba matsala, dama kuma ana fitar da abinci a sashin Gimbiya Aminatu, da Gimbiya Saudatu da kuma gidan Galadima, da Hajia Mama.
Da gidan Dr Aliyu da sauran duka, kuma ko Juwairiyya ma tanayi”.
Murmushi ta ɗanyu tare da cewa.
“To Ummi muma ai muna son ladan wannan aikin”.
Da sauri tace.
“A sosai ma kuwa. Sai dai ki sanar da maigidankin in ya yarda yanzu incewa Saratu ta ƙara hannun sosai”.
cikin kwaɓe fuska tace.
“To Ummi shi wannan sarkin zirga-zirgan ina zan ganshi?”.
Cikin yin ƙasa da murya Ummi tace.
“Yana falonshi yanzu ya dawo, yana wucewa kina fitowa, jeki sameshi da sauri kada yayi bacci ya zama kin tadashi a bacci dan babu abinda yafi ɓata mishi rai sama da ya fara bacci a tadashi”.
Cikin juya ido tace.
“Ummi to ni me zan ce mishi?”.
Murmushi Ummin ta kumayi kana tace.
“Abinda kika cemin shi zaki ce mishi, tashi kije musan yadda zamu fuskanci aikin”.
Ta ƙarishe mgnar tana miƙar da hannunta, a hankali ta miƙe tsaye, doguwar rigar jikinta ta gyara tare da yane mayafinshi.
Ganin ta tsaya ne yasa Ummi cewa”
“kije mana.” Allah yasani badon tana son ladan aikin ciyar da marasa ƙarfi da basu abin buɗa bakiba da bazata sake zuwa tambayar abu wurin wannan kurman ganganɗinba, tun randa taje tana mishi mgnar yacewa Umaymah ta bar musu Hibba ya shareta take jin haushinsa in ta ganshi kamar ta ɗirka mishi dundu a baya.
Muryar Ummi data kuma jine yasata, juyawa, ta nufi corridor’n da zai sadata da falonshi.

A hankali take taku, tana jin sanyin tayis ɗin wurin na ratsa mata ƙafa,
sallama tayi a bakin kofar tare da kutsa kai ciki, tana mai murtuƙe fuska.
Bisa 1 str ta sameshi zaune, da alamun waya yakeyi da Umaymah.
Dan taji yana kiran sunanta.
Gefenshi ta ɗan tsaya tare da kallonshi ta wutsiyar ido.
Shi wai ko shi kaɗai ko a ɗakinshi shi ɗaya sai ya zauna da kima-kiman riguna, ganshi wata ƙil basa damunshi”.
Haka taketa maganar zuci, har ya gama wayar da yakeyi bata, saniba.
shi kuwa baibi ta kantaba yaci gaba da ɗan aikin da yakeyi a wayar.
Jin shirune yasa ta ɗan kalleshi, ganin ya gama wayar da yakeyi ne yasa, cikin dakiyar murya tace.
“Uhummm dama so nake in ba matsala ko zamu rinƙa yin abin buɗa baki ana kaiwa masallacin, da kuma bawa bayi nasu daban”.
Bai kulata ba, asalima yamutsa fuskarshi yayi, ya lura wannan abar bata gama iya sanin makamar mgna ba, ji yadda take mgn a kaikace.
Kamar ba ba fullatanaba, bayan anyi ittifaƙin bayan larabawa babu ƙabilar dake da luggar iya sarrafa harshe sama da Fulani.
Shiru tayi tare da tura baki kana ta ɗan murguɗashi, tare da cewa.
“Ayyah ka amince mana?”.
kanshi ya sunkuyar tare da ɗaga system ɗinshi ganin biyu dai-dai ta cika.
Miƙewa tsaye yayi tare da motsa lips ɗinshi a hankali yace.
“Eh”. Da sauri ta juya ta fita tana hararan bayanshi.
Shi kuwa bedroom ɗinshi ya wuce.

Rage kayan jikinshi yayi kana yasa hannunshi ya jawo pillow’nshi ya wurgar can gefe gaban gadon inda babu carpet,
a hankali ya kwanta a wurin,
Gudun kada daɗi gado yasashi yayi baccin da zai makara sallan la’asar, Yana konciya ba jimawa yayi bacci.

Ita kuwa cikin jin daɗin amincewar da yayi, tacewa Ummi.
“Ummi ya yarda yace muyi”.
Miƙewa Ummi tayi tare da nufar kitchen a tare suka shiga.
Tana cewa.
“Yauwa to taho mu gayawa Saratu abinda za’ayi.

A tsaye suka sameta a tsakiyar kitchen ɗin kusa da kitchen table, tana gyara ganyen.
“Yauwa Saratu kin wonke shinkarfa masan ne?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh na wonke,kuma mafa tun ɗazu da nazo kuna kuma bacci na jiƙa wani, sai dai hannuna ya zarce yayi yawa, yanzu ina gama tsinkar ganyen zan kai markaɗen ne in na dawo an kwaɓashin sai in fara firan Arish ɗin”.
Ajiyan zuciya Ummi tayi tare da cewa.
“Mugamshin”.
Babbar robar dake gefenta ta jawo tare da cewa.
“Gashi kinga yayi yawa wlh mancewa nai sai naga kamar na gidan Gimbiya Aminatu zan jiƙa shiyasa, kinga da na haɗa da wanda kika jiƙan yayi yawa sosai, ko zamu rabashi biyu”.
Murmushi Shatu tayi ganin shinkafar tanada yawa, kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Ba matsala hakanma yayi dama mai yawan akeso”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Ga kuma ƙullun na dafa tun ɗazu har yayi sanyi, shiyasa nake sauri in kai markaɗen naga lokacin yayi nisa”.
Motsowa tayi inda take tare da cewa.
“Ɗauki markaɗen ki kai bari in ƙarisa wannan aikin”.
Cikin mamaki tace.
“A a bar”.
Da sauri ta katseta da cewa, jeki”.
To tace cikin mamakin sauƙin halinta ta ɗauki robar jiƙeƙƙiyar shinkafar da ta kai mudu biyar har ta ɗaura a kai,
Ta kuma sauke jin Shatu na cewa.
“Yauwa naga akwai murjejjiyar gyaɗa, ɗebo, da wata shinkafar kizo ga dabino da kwakwa a nan ki haɗa ki jikasasu ki tafi dasu, na kunune kafin a markaɗa wannan na masan shinma ya jiƙa sai a markaɗa miki shi.
Da sauri ta juya tayi yadda tace ɗin tanayi tana nuna mata dai-dai yadda takeso, saida ta gama kana rufe babban roban da marfinshi sannan ta ɗaura ƙaramin a kai ta tafi.

Ita kuwa Shatu matsowa tayi taci gaba da tsinkan ganyen, ita kuma Ummi freezer’n ta buɗe tare da ɗebo kayan ciki mai yawa, tazo.
Ta wonƙeshi fes, kana ta watsa al’basa mai yawa a ciki, Sannan tasa citta,kanamfari, cory tare da sauran kayan ɗanɗanon.
Gas ta kunna ta ɗaura tukunyar, sannan ta dai-dai-ta wutar.

Wani babban roba ta ɗauko kana ta nufi Store Arish ta ɗebo mai ɗan yawa tazo tana fereshi cikin ɗan injin ɗin firar lokaci ɗaya tayi nisa a fitar.
Ita kuwa Shatu tana gana gyaran ganyen ta ɗebo kayan miya tazo ta jajjagasu yadda takeso.
Kusan a tare suka gama da Ummi.
Wankeshi Ummi tayi bayan ta yishi tsillk-tsillk kana ta sashi a tukunya, tare ɗan yaryaɗa gishiri, ta rufeshi.
Ta ajiye gefe.
Ita kuwa Shatu cikin kula ta kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi me za’ayi da ganyen?”.
“Miyan da za’aci masar dashi”.
To bata amsa tana komawa cikin Freezer’n fruits ta ɗebo.
Tazo tana wonkesu tare da shiryasu cikin tray mai girma, kana ta shirya wasu kuma a wani ɗan madaidaicin tray mai masifar kyau.
rufesu tayi kana taje tasasu cikin Fridge.

It’s kuwa Shatu can nama ta ɗebo dai-dai misali wonƙeshi tayi tasa a tukunya tare dasa kayan ƙamshi dana ɗanɗano.
ta ɗaura a wuta. Ummi kuwa ruwan tea ta ɗaura a ɗaya murhun dake gas ɗin babbane.

Naman na sulaluwa ta kwasheshi tasa mai saida yayi zafi tasa al’basa,
ya soyu yana ƙamshi kafin tasa jajjagen kayan miyar ta,
Ya soyu kana ta ƙara wonƙe ganyen miyar yazo tasa, ta soyashi da kyau.
kana ta zuba naman da sauran ruwan miyan.
Tasa duk sauran kayan hadin ta rufe tukunyar.
Sosai Ummi tayi mamakin yadda ta haɗa miyar, to sai dai bata damuba sabida sanin ko wacce mace da yadda take sarrafa girkinta, kai yadda kakeyi daban in wani ya gani yayi mamaki, yadda wani keyi da ban in ka gani kayi mamaki.

Cikin ƙanƙanin lokaci dai suka haɗa duk aiyukan da zasu iya ajiyesu ba tare da sun samu matsalaba.
Ita tayi miyar masan, ta kuma ƙarisa ferfesun kayan cikin da Ummi ta fara.
Ummi kuwa ta tafasa musu tea ta ɗuɗɗura a flaks,
Kana ta tafasa Arish ɗin.
Dai-dai lokacin kuma Saratu ta dawo.
Ita Ummi ce ta ɗan amshi ƙullun masar tare da cewa.
“Gskya mun ɗan makara aikin Masar nan gashi ni hannuna baya tashi da wuri”.
Da sauri Shatu ta matso tare da miƙawa Ummi roban markaɗen kunun.
Tace.
“Ba matsala Ummi ni hannuna na tashi da wuri.
Yanzu tace mana marƙaden kunun bari in kwaɓa mana Masar.”
Haka kuwa akayi Ummi ta fara tacewa.
Ita kuwa kulun dafaffiyar ɗanyar shinkafar ta murmusa cikin marƙaden Masar,
Kana tasa fulawa tare da yis kaɗan sannan ta tarfa gishiri kaɗan.
Kana ta rufeshi a robar dan babbace, motso da robar tayi kusa da Gas ɗin yana ɗan jin ɗumin wuta.
Gefen Ummi ta dawo wacce ta gama tace markaɗen
A babbar tukunta ta zuba shi kana ta ɗaura kan wuta tare da dai-dai-ta wutar tanayi tana motsa kunun.
tare da ɗan tarfa wanda ta rage, da surkin lemun tsami.
Cikin Sa’a ɗaya ta dama kunun shinkafar fari ƙal tamkar madara.
Sugar tasa ta juye a a ƙatuwar kula kana tasa a maidaciyar kula, Sannan tasa a flaks ɗaya, sai kuma tasa a Mug mai marfi duk ta kimtsasu gefe.
Tuni Side ɗin ya ɗin ke da ƙamshi miyar masan da ferfesun nan.
Buɗewa tayi ganin miyar tayine ta sauƙe ta maida gefe.
Kana ta kalli Ummi tace.
“Ummi je kiyi salla la’asar tayi, in kin dawo sai inje inyi”.
To Ummi tace ta fita tana mamakin saurin aikin Shatu.
Koda taje tayi sallan ta dawo ta sameta tana sauƙe tukunyar ferfesun.
ganin Ummi yasa tace. “Yauwa Ummi komai yayi dai-dai yanzu kaskon tuya zamu daura kinga kullun ya tashi”.
Cikin mamaki Ummi ta kalli Robar da taga har kullun na shirin zubewa.
Ita kuma ɗiba tayi a wata roba kana duk tasa yankekken al’basane a ciki Sannan tasa sugar ta gauraya,
sannan ta matso da kasko biyu,
juyowa tayi ta kalli Saratu tace.
“Yauwa Sara matso. Ke ki rinƙa yi kina sawa a wannan babban kulan in ya cika kisa a wannan shima.
Ummi ke kuma kisa mana namu anan suyanki mukeson ci”.
Murmushi Ummi tayi kana tace.
“To jekiyi salla”.
To tace kana ta fita.
Ita kuma Ummi ta juya ta kalli Sara tare da cewa.
“Kema kije kiyi salla”.
Cikin ci gaba da aikinta tace.
“Ai nima nayi”.
“To shike nan”. Ummi tace kana sukaci gaba da tuyan.

A falo ta haɗu da Hibba da Jamil, sai dariya yakeyi cikin dariyar yace.
“Yauwa Aunty Shatu dama idonki nazo in gani, dan ga Hibba kam ta kusa kasawa”.
Murmushi tayi dan bata da sauran ƙarfin yin dariya.
Cikin ɗan fito da idanunta da suka ɗan faɗa tace.
“Gani ras dani”.
Dariyar ƙeta mai cike da alamun yunwa da ƙishi yayi tare da cewa.
“Inafa ras kalli yadda idonki ya fito kamar kinyi azumi goma”.
Murmushi tayi kana tace.
“Um bari inje inyi salla”.
Sai ta kuma kalli Hibba dake lankwabe tace.
“Sannu Hibba kwanta ki huta”.
Jalal da yanzu ya shigone ya ɗan taɓe baki tare da cewa.
“To me tayi da zata huta tunda fa gari ya waya in anga ta tashi dai yin salla ne, tun tuni birgima take a tayis wai sanyi take nema”.
Dariya sukayi mata baki ɗayansu,
Ita dai Shatu ciki ta wuce.
Salla tayi kana ta fito. Koda tazo kitchen ta samu Hibba na suya musu Arish ɗin, tayi mamaki.
Cikin wasa tace.
“Kawo in karɓeki jeki kwanta”.
Cikin sanyi tace.
“Ai Hamma Jabeer ne yace min in ina aiki bazanji wuya ba, zanfi ganin lokaci ya gudu”.
Dariya sukayi mata kana kowa yaci gaba da aikinshi.
Ita Shatu miyar sahur na asuba ta ɗaura musu.

Cikin ikon Allah shida dai-dai suka gam kan aikinsu.
Bayan Shatu’n ta taya Hibba suya kwai daban, ta jerasu a Foodflaks, in ta ajiye fefeyin soyayyan ƙwai da yaji haɗi da diddigin kifi, sai ta zuba soyayyan Arish a kai kana ta kuma rufeshi da fefeyin kwai haka ta rinƙa jerasu saida ta cika kulan.

Ummi kuwa ta sawa Saratu komai nata.

Sannan suka kimtsa wurin fes suka fito da komai suka jera a dinning table.

Nan duk suka wuce ɗauki.
Wanka sukayi, kana sukayi al’wala sannan suka fito falo. A nan suka samu Imran, Jalal, Jamil, Sulaiman.
Cikin gajiya Ummi tace.
“Yauwa Jalal ku ɗauki manyan kulolin nan ku kai masallaci.
Sauran madaidaitan kuma ku ajiyewa sarkin bayi.
A bawa bayi da hadimai”.
Murmushi Jamil yayi tare da cewa.
“Eh lallai bana bayi sun samu uwar gijiyar data tuna dasu, bayan kuma anayi musu nasu na daban”.
Cikin lumshe ido Shatu tace.
“Eh suma suci abinda muke dafawa da kanmu, ba sai na gandun nasuba”.

Miƙewa sukayi suka ɗauki kulolin sun zo falon kenan Sheykh na shigowa, wani hadimi na biye dashi da manyan ledodi cike da ƴaƴan itatuwa.
Kusan a tare suke mishi sannu da dawowa.
Murya a bushe alamun ƙishi yake amsa musu kana ya nunawa Ummi leda ɗaya yace.
“Ummi a wonke wannan a haɗa da dabino mudu uku a basu su kai masallaci”.
Ya ƙarishe mgnar yana wucewa.
Da sauri Ummi tace to.
Ta miƙe kenan Shatu tace.
“Ummi zauna bari in wanke sun”.
To tace kana ta koma ta zauna.
Ita kuma taje ta wonke ta zubasu a tray kana ta ɗauko plates and cups masu yawa, tazo ta miƙawa Imran.
Da sauri suka amsa suka tafi.

Jim kaɗan suka dawo, cikin gajiya Jamil yace.
“Ummi ansha ruwafa mun samu Ladan na cin dabino”.
Da sauri Hibba ta miƙa tare da cewa.
“Su ladanannan haka suke basa kiran salla sai sun sha ruwa.”
Dariya sukayi mata kana suma suka miƙe sukabi bayanta.

Zama sukayi bisa kujerun kowa da abin yake hari.
Sai dai kab ɗibsu da dabino suka fara.
Ummi ce ta kalli Shatu tare da nuna mata babban tray’n da aka shirya komai na buɗa cikin Foodflaks guda 3 madaidata masu kyau, sai plate ɗin da aka shirya fruits masu ɗan karen sanyi, tupa, inabi ,kankana, abarba, gwanda, Lemu, ayaba, kana da dabino, da kwakwa,
Sai goran zam-zam madaidaci, kana sai cup da tea spoon a ciki, sai fork and knife a gefe da gefen plate ɗin dake cike da fruits ɗin komai biyu akasa.
Kulolin kuma ɗaya masane a ciki, ɗan namiyar kuma miyar Masar ne, sai ɗayan kuma, soyayyan ƙwai da dankalin, ɗayan kuma ferfesun kayan cikin ne.
Cikin nitsuwa Ummi ta ɗago tray ta miƙa mata tare da cewa.
“Yauwa gashi kai mishi lokacin shan ruwan na tafiya, yanzu zakiga ya fito”.
Cikin sanyi da gajiya ta amshi tray’n kana ta nufi falon nashi, cikin nitsuwa take takun, a hankali tayi sallama tare da kutsa kai cikin falon.
A can bisa Dinning area ta hangoshi yana zaune, kan kujera ɗaya, ya kuma jawo ɗaya kujerar ya ɗaura sawunshi a kai ya miƙesu, System ɗinshi na bisa cinyarshi.
A hankali take takowa saman steps ɗin tare da ratsa cikin jeren ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu darajar sheƙin Daimond sai sunkuyar da kanta tayi sabida ɗauke mata ido da suke.

A hankali ta isa kusa dashi, cikin tura baki tare da ɗan murguɗashi ta ajiye tray’n, a tsakiyar table ɗin.
ɗago kanta tayi da niyar ta ɗan juya, ta fita.
Wani irin buɗe idanin tayi gaba ɗaya tare da zubasu, bisa sharaban ƙafarsa ta dama, wanda sanaɗin zaman da ya ɗan yi ya miƙe ƙafafuwan nashi bisa ɗaya kujerar ne yasa suka ɗan baiyana, wani irin kallo mai cike da ɗimuwa takeyiwa zanen dake bisa ƙafarshi ta dama, da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannun hagun ta kama kanta sabida wani irin sarawa da ya farayi da ƙarfi.
Cikin sauri ta juyo tare da miƙa hannun damanta ta sauƙeshi kan…!

 

 

Akwai kayan gyara na amare da uwar gidaye da masu jego, ga mai buƙatar saya ga number ta 09097853276

r

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button