Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 27

Sponsored Links

GARKUWAR FULANI* FULANI*Ta kamo hannun Jalal da ya miƙe tsaye da nufin yarfa mata mari.

Cikin wani irin masifeffen tsana, Hajia Mama takalli Shatu.
Kana da sauri ta juya ta nufi hanyar fita.
Sheykh da tunda ya fito yake tsaye tamkar an dashi ne,
yayi saurin bin bayanta tare da cewa.
“Hajia Mama! Mama!! Mama dan Allah kiyi haƙuri, kizo karki fita Please Mama karki fita, babu wata halitta da zata miki iyaka da sashina, in kin tafi kenan kinbi umarninta.”
Cikin tashin hankali yake waɗannan kalaman yana mai binta a baya.

Jamil kuwa miƙewa tsaye yayi ya zubawa Shatu idanu tamkar zasu faɗo ƙasa.

Related Articles

Aunty Juwairiyya kuwa, wani irin kallo mai sarƙafe da ma’anoni takeyiwa Shatu.

Ya Jafar kuwa wani irin kallo mai surke da murmushin jin daɗi yakeyiwa Aysha.

Ummi kuwa tuni jikinta rawa yakeyi da abinda ya faru.

Imran, Ya Hashim, kuwa ido suka zubawa sarautar Allah.
Hibba kuwa kuka takeyi tare da riƙo hannun Shatu tana ja tare da cewa.
“Aunty Aysha ki bari, Mamace fa! Kizo mu tafi ɗaki”.
Tanayi tana jan hannun Shatu da ƙarfin tsiya, dole yasa Shatu ta bita a baya.

Umaymah kuwa wani irin tashin hankali da tafasan zuciyane ya dirar mata lokaci ɗaya.
Da wani irin kallo tabi bayan Aysha dashi.

Duk wanda ya ganta yasan tana cikin tashin hankali.
Gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi.
Sun daɗe a haka, da kyar dai
Cikin wani irin tafasan zuciya ta saki hannun Jalal.
Tare da komawa ta zauna.
Da yatsa ta nuna musu hanyar fita daga falon. Murya a hargitse tace.
“Kul kada ka sake tunanin gigin ɗaga kayi nufin taɓa lfyar Aysha, bana so kul.
Maza Ku tafi masallaci”.
Sai lokacin suka jiyo sautin muryar Jabeer yana Hudba.
Wanda daga jin muryarsa kasan yana cikin baƙin ciki.

Wani irin numfarfashi Jalal ya sabke tare da yin koffa kana ya juya ya nufi hanyar fita shi matsalarsa meyasa Umaymah na mgn Aysha na mgn Umaymah na hanata abu tanayi.
Haka su Jamil da su Imran da ya Hashim da Ya Jafar suka fita.

Ita kuwa Aunty Juwairiyya wani irin tashi tayi ta fita ta nufi Side ɗin ta.

Ya zama Ummi da Umaymah ne kaɗai suka rage a falon.

Shiru sukayi tamkar ruwa ya cin yesu.
“Uhuhhmmmm”. Umaymah ta fesar da wani zazzafan numfashi mai ɗumi.
Hakama Ummi tagwayen numfarfashi masu nauyi ta sauƙe.
Kallon juna sukayi, cikin shiga al’hini wannan al’amari cikin tsoro da karaya Umaymah tace.
“Toh wai meye hakan? Meke faruwa ne? Me hakan yake nufi? Kaina ya kulle. Wani zagon kasan kuma aka shirya tsakanin Shatu da Hajia Mama ko dai dama da zagon ƙasan ne?.
Wake saƙa gadar zare, muna na bi ta kai ya rubta da mu”.
Wani numfashin Ummi ta fesar tare da cewa.
“Tabbas akwai babban al’amarin dake faruwa wanda bamu saniba Ni tsorona ɗaya kada a juya ƙoƙwalwar yar mutane.”

Shiru sukayi cikin ta’ajjudin al’amarin. A hankali suka miƙe a tare suka nufi ɗakinsu jin har an idar da sallan a masallacin.
Al’wala sukayi kana sukayi salla daga bisani suka, fara tattauna wani abu na sirrin masarautar Joɗa.

A cikin ɗakin Shatu kuwa, tunda suka shiga ta kwanta bisa gado.
Bacci tayi bacci, hakama Hibba.
Sai ƙarfe uku dai-dai Shatu ta tashi.
Cikin kasalan baccin da bai gama isarta ba, ta miƙe ta shiga bathroom.
Wonka tayi tare da al’wala.
Bayan ta fitone, ta tada Hibba, ita kuma ta kabbarta sallah.

Kafin ta idarma Hibba ta fito, gefenta tazo itama ta kabbarta sallan.

Basu tashi bisa sallayan ba, sukaji kiran aallan la’asar.
Haka yasa sukayi sallan. Suna idarwa Hibba ta miƙe ta nufi ɗakin Umaymah.
Ita kuwa Shatu ninke sallayar tayi kana ta dawo gaban dreesing mirror.
Mai ta shafa tare da ɗan murza fauda a fuskarta, kama ta shafa man baki.

A cikin sanyi taje gaban drower’nta,
hannu tasa ta buɗe drower’r, wata tattausar doguwar riga mai masifar kyau ta zaro.
Kalar rigar Black blue mai sheƙi, saman rigar a ɗan tsuke daga ƙasan ƙugunta kuma a buɗe,
yanada wasu duwasu kamar na Daimond daga sama har ƙasan gaban rigar.
Hannunta kuma masu faɗi.
Tayi kyau sosai cikin rigar, dogon gashinta ta haɗa ta tubke wuri ɗaya ta kitse jelar kana ta nannaɗe jelar a ƙeyarta,
sannan tayi rolling kanta da mayafin wanda dai dai inda zai zauna a goshin akwai duwatsun.

Turare ta fesa, kana cikin sanyi da kasala ta nufi, falo.

A falon ta samu, Hibba a kwance tayi shiru.
Ganin bata gan fitowarta banema,
Yasa ta nufi inda take gefenta ta zauna tare da cewa.
“Hibba ɗauko mana awaran”.
Cikin sanyi Hibba tace.
“To”. Kana ta miƙe ta nufi falon, jin shiru ba kowa a cikine, yasa ta nufi kitchen a hankali-hankali.
Foodflaks ɗin da suka sa awaran da suka soya ta ɗauko.

Tana dawowa ta zauna kusa da Shatu tare da cewa.
“Gashi”. Kai ta gyaɗa mata tare da nuna mata kitchen ɗin ta, tace.
“Ɗauko mana plate da roban yajin da Gimbiya Aminatu ta aiko mana.
Kizo mana da ruwa”.
Ba tare da tace komaiba ta juya ta tafi.

Bayan ta dawone suka zauna suka fara cin wanda suka zuba.

A can falon Hajia Mama kuwa,
duk mgnar da Umaymah da Ummi keyi, shiru tayi ta zuba musu ido.
cikin sanyi Umaymah tace.
“Addana kiyi haƙuri, kin san yaran sai a hankali, dan Allah kada kisa wani abun a ranki wata ran ko ance tayi miki bazatayi ba”.
Murmushi tayi mai cike da ma’anoni kana tace.
“Uhummm ba komai Khadijah jekici gaba da shirin tafiyarki, karki damu kinji”.
Ido suka zuba mata domin duk basu gamsu da mgnarta ba, to amman ya zasuyi tunda tace ba komai.

Haka suka tashi suka dawo falon.
Yau su Jalal ma basu zoba.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, tunda aka idar da sallan azahar ya dawo, ya wuce su Umaymah a falon ba tare da yace musu ƙalaba.
koda ya shiga ɗakin ya samu yayi bacci tsakanin azahar da la’asar kamar yadda ya saba, hakan bai samuba.
Sabida abubuwan dake ranshi.
Bathroom ya shiga ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, tare da fara yage towel ɗin dake hannunshi.
haka yake tsaye a ƙasan ruwan har saida yaji an kira sallan la’asar. Nanne ya fita ya tafi masallacin.
Bayan an idar da sallan ne ya dawo gida.
Ganin babu kowa a falon ne yasashi zama, bisa kujerarsa.
Ƙafarshi ɗaya ya ɗaura kan ɗaya.

A haka su Umaymah suka sameshi.
Gefenshi Umaymah ta zauna bisa kujerar dake kusa dashi.
Ummi kuwa gabanshi ta zauna bisa carpet.

A hankali ya buɗe kwayar idanunshi.
Cikin tarin ɓacin rai ya kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi ina wannan fitsarerren abun da bai san darajar manya ba!?.”
Cikin sanyi Ummi tace.
“Allah ya huci zuciyarka tuba takeyi, in sha Allah bazata sakeba, Hajia Mama da kanta ta yafe mata”.
Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“Ummi ko dai kece kika bata dama da matsayin yiwa Mama hakane?”.
Cikin sauri tace.
“Wanne ni wlh bani bace”.
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Umaymah da itama shi take kallo cikin ɓacin rai yace.
“Umaymah har akwai wani abun da zai hana mama shigowa sashina? Har yaushe waccar babyn robar ta samu dama da ikon bada izinin shiga da fita cikin sashina da abinda ya shafi rayuwata?
Me take nufi dani da iyayen nawa.”
Kauda ido Umaymah tayi daga kallonshi kana a hankali tace.
“Ba isa bane! Akasi aka samu! Nifa inaga har yau Shatu’n bata gama sanin mutanen masarautar Joɗa da kuma dangantakar makusan tankaba, ayi mata haƙuri a mata uzuri a dai wannan karon”.
Juyowa yayi ya kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi a kira min waccar abar”.
Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa to.

A falon ta samesu, cikin fuskar da babu yabo babu fallasa ta kalli Shatu dake gefen Hibba da alamun ta cire hannunta a cin awarar kanta ta ɗan kauda tare da cewa.
“Kizo Sheykh yana kiranki”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa “Toh”. miƙewa tayi taje Dinning area ta wonke hannunta, kana tazo tabi bayan Ummi.

A gabanshi Ummi ta zauna ganin haka itama ta zauna a gabanshi.
shiru tayi tana kallon yatsun fararen sawunshi. Shi kuwa kanshi na gefe ba tare da ya juyo ya kalleta ba yace.
“Ke ki shiga hankalin ki, kisan abinda kikeyi da wanda zakiyi! Ke har kin kai matakin da isar da zaki ƙaddamar min da iko da isa a cikin gidana? Ko dai ce miki akayi gidan nakine?”.
Kai ta gyaɗa mishi alamun eh ance mata gidan natane!.
Wani irin tsuke fuskarsa yayi tare da ci gaba da mgna dan shi bai ga sanda ta gyaɗa kanba hakama Umaymah, sai Ummi ce kaɗai ta gani, su kuwa sai murmushi sukayi.
Cikin kausasa murya yace.
“In baki san darajar manya da iyayeba, to ki zama kurma bebiya makauniya a cikin giddannan kafin Ubangiji ya zantar da Hukuncin da ikon zamanki da barinshi dan ikone na Allah bana waniba.
Har kin isama Mama tazo ki koreta dan idonki basu da ɗigon kunya.
Ko karen gidannan baki da ikon hanashi abu da sakashi bare Mama.
ke ta bawa abun ne da zakice bakya so.
Kece mai bakin mgn uwar fitsararru ko?”.
Sam abinda bai saniba zuwa yanzu hankalinta, tunaninta nitsuwarta, jinta, da ganinta duk suna kan farar ƙamarshi ta dama, da zanen maciji ke liƙe kamar macijin na tafiya.
Wani irin ba hagun numfashin ta sauƙe a hankali,
tare da rufe manyan idanunta da azaban ƙarfi.
Sabida gani takeyi Tamkar macicijin ne ma da kanshi ke manne a jikinshi yana kuma motsa ɗan bindinshi dake saman babbar yatsarshi.
A hankali ta buɗe idanun kana tabi kan rumfar ƙafar da ido, inda take ganin zanen maciyar yabi.
Kasan cewar a zaune yake ya kuma ɗan tattare al’kyabbar jikinshi.
Shi yasa tana iya ganin har ƙarshen rumfar tafin ƙafar nashi.
Inda iya nan jallabiyar jikinshi ta rufe.
da sauri ta ƙara rusunar da kanta wai ko zata ga ci gaban tafiyar macijiyar.

Umaymah ce ta ɗan kalleta cikin wata iriyar murya tace.
“Ki tashi muje ki bawa Hajia Mama haƙuri, ku nemi yafiyarta ki kuma kiyaye gaba, kinji”.
Cikin sanyi tace.
“Toh”.
Still Bata miƙeba, cikin ɗan ɗaga murya yace.
“Tashi muje yanzu ki bata haƙuri, in ta haƙura kinyi babban Sa’a”.
cikin sanyin jiki ta miƙe tsaye.
Shima miƙewa yayi, Ummi kuwa da sauri ta nufi ɗakin Shatu.
Jim kaɗan ta fito da wata kekyawar al’kyabbar matan masarauta ta zuramata.
Bayan ta gama gyrashi ne, tasaka hular.
Shi yayi gaba ita kuwa.

Tabi bayanshi Umaymah da Ummi suka biyo bayanshi.

Suna isa bakin mashigar farfajiyar Side ɗin Hajia Mama,
ta tsaya gis tare da yin ƙasa da kanta.
Ummi ce tace.
“Muje mana”.
Shiru batayi mgna ba, jin hakane yasashi juyowa, karon forko kenan da ya zubawa tsawonta ido.
cikin ɓacin rai yace.
“Muje ki lashe aman da kikayi da kanki”.
Cikin sanyin sauti tace.
“Ni bazan shigaba”.
Da mamaki Umaymah tace.
“Innalillahi wai ke Ayshs wani irin taurin kaine dake? Menene manufarki?”.
Murya can ƙasa yana rawa alum zatayi kuka ta kalli Umaymah tace.
“Kiyi haƙuri Umaymah ki gafarceni, amman ni bazanje ba, in kuma zanje to ku ku koma, zanje ni ɗaya zan bata haƙuri”.
Cike da al’ajabi Umaymah tace.
“To sabida me bazaki je da muba”.
Cikin faɗa Sheykh yace.
“Sabida muna furci mana, ba zuwa zatayi ba, shiyasa zatace sai dai in ita ɗaya zataje, maza wuce muje a gabana zaki bata haƙuri”.
Cikin sanyi Umaymah tace.
“Jazlaan barta mu tsaya mu jirata anan in dai zataje ita ɗayan”.
Kanshi ya dafe tare da cewa.
“To wai Umaymah mu bayaninta ne da zamu tsaya muna jiranta”.
Ummi ce ta mishi alamun yayi haƙuri ya yarda.
Shiru yayi tare da komawa gefen jerin bishi yoyin namiji kwanɗa ya zauna bisa kujerun silver dake zagaye da wurin wanda ko wani side akwaisu.

Itama Umaymah da Ummi zuwa sukayi suka zauna.
Ita kuwa Shatu a hankali ta fara taku ta nufi cikin farfajiyar, suna hangota har ta isa bakin ƙofar.
turawa tayi ta shiga, kana ta maida ƙofar ta rufe.

Bayan kamar 37 minutes ta fito.
Cikin wani irin tafiya mai baiyana tsantsar jin daɗi, fuska cike da fara’a ta nufosu.
A hankali ta isa gabanshi ciki ɗan ɗaga murya tace.
“Na bata haƙuri ta yafe min, ta samin al’barka. Kaima kayi haƙuri ka yafe min”.
Da mamaki suka kalleta.

Shi kuwa Sheykh Jabeer wari irin kallon tuhuma yayi mata, kana ya miƙe tsaye tare da cewa.
“In ma ƙarya kikayi, ni ba’amin ƙarya”.
Sai ya kuma kalli Umaymah tare da cewa.
“Umaymah kuje ki ƙarisa shirinki bari inje wurin Hajia Mama”.
To tace kana taja hannun Shatu suka tafi. Shi kuwa da Ummi suka nufi cikin Side ɗin Mama.

Bayan sallan isha’i, cike suke a falon. Gaba dayansu, Umaymah zaune a tsakiyarsu da jakarta, Sheykh Jabeer na yi mata addu’o’in isa lfy suna amsawa da Amin Amin.
Bayan sun shafa addu’o’in ne ta miƙe tsaye, tare da kallon su baki ɗaya, murya na rawa tace.
“Jazlaan zan tafi, zan bar hankali na, a nan ko na koma banda nitsuwa, kullum ina cikin taraddadin abubuwanda yake faruwa, Jazlaan na sani kaine GARKUWAR yayanka da ƙanneka. Ga wani sabon nauyi ya ƙarun maka.
Aysha baƙuwace bata san komaiba kam al’amuran Masarautar Joɗa, dan Allah in tayi abinda ba dai-dai ba kuyi mata uzuri.
Ita komai a sabon abu zata ganshi abinda bata taɓa ganiba.
Mun rabata da iyayenta yayunta ƙannenta mun kawota tsakiyarmu, mu kasance mata adalan masu masauƙi.
Na sani Jazlaan ka fini sanin haka da kuma haƙƙoƙinta da suka rataya gareka.”
Sai ta kuma kalli sauran yaran yar uwarta ɗin tace.
“Jalal, Jamil, Aysha matsayin yar uwarku take, yayarku ce, matar yayanku. Bana son raini especially kai Jalal, ban gamsu da irin mu’amalat ɗin ka da itaba.
Babu wanda yake nuna min yadda nakeso a kanta sai Jafar, a duk sanda ya ganta zaiyi mata murmushi kamar yadda yake min, in yaga bata nan zaiyi ta dube-duben da nasan da yanada baki zai tambayeni lfyarta.
Zan bar Hibba saboda itane, bana son taji kanta a matsayin bare.”
Shiru sukayi gaba ɗayansu sabida yadda take kuka da yin mgna tamkar mai bar musu wasiya, ko wacce wani tsohon damuwa ya taso mata.
Sharce hawayenta tayi tare da cewa.
“Ummin Jabeer zan tafi zan barki da sauran aiki, dan Allah ki kula da Shatu da mu’amalarta da Hajia Mama, ki nuna mata uwar miji ba abun rainawa bace”.
Sai kuma ta miƙowa Aysha da taketa kuka hannun ta jawota tsaye ruggume ta tayi cikin zubda hawaye tace.
“I dan akaga damuna ana zaton yabanya zatayi kyau, kallon damuna nakeyi miki a cikin ahlin yar uwata.
Ina jin zaki zamo mana haske mai yaye duhun daya maye ganinmu, tun kafin yau ni na sanki a mafarkina Allah ke nuna min ke a matsayin matar Jazlaan ɗin na, kuma Allah yana nunamin abubuwa da dama a kanki a cikin mafarkaina, wasu kuma sunma tabbata na gansu.
dan Allah ki riƙe min Jazlaan amana, ki lura da ƙannenshi yadda zaki lura da naki ƙannen ki kula da Jafar kada ki tsoraceshi bazai cutar da keba ki ɗaukeshi a
Matsayin wa”.
Cikin zubda hawaye Shatu tace.
“In Sha Allah Umaymah zan kiyaye zan kuma zamo yadda kike zatonta, koda sanadin haka zan rasa jigo biyu na rayuwata rai da lafiya ta”.
Kalaman Umaymah da Aysha kuramen baƙine da su kansu ɗaya bata fahimci abinda ɗaya take nufiba, hakama ɗayar, bare su Jalal dake tsaye.
Jawo Hibba tayi ta haɗa su ta ruggume,
kana ta jawo Juwairiyya tace.
“Ku duk yara nane ku zauna lfy”.
Gaba ɗaya da to suka amsa.
Cikin sauri Umaymah ta sakesu kana ta miƙa wa Ummi hannu sukayi musababa, tare da bar mata sallahun yaran.

Daga nan suka fita, gaba ɗayansu.
Sai Shatu da Hibba da suke kuka, ganin hakane Ummi ta dawo ta zauna dasu.

Jabeer da Jafar da Umaymah kuwa Side ɗin Mama sukaje, tayi sallama da ita, suka rabu suna hawaye.
Daga nan Side ɗin Lamiɗo da Gimbiyar shi sukaje.
Nan sukayi sallama dasu kana suka fito, inda suka samu Jamil da Jalal sun kawo musu motoci. Daga nan suka shiga suka tafi Airport tare da rakiyar motocin fadawa guda uku ya zama motoci biyar ne suka tafi kaita Airport.

A gida kuwa, da kyar Ummi ta samu ta lallashi Shatu da Hibba da cewa in basuyi shiruba, zata, sa akai Hibba Airport ta tafi da Umaymah.
jin hakane yasa Hibba tayi shiru. Ita kuwa Shatu dama ba kuka mai sauti takeyi ba, zubda hawaye takeyi.

Ƙarfe tara dai-dai jirginsu Umaymah ya tashi zuwa jihar Tsinako.

A gida kuwa tuni Shatu da Hibba sun shiga kuma har sunyi bacci sabida kukan da sukayi.

Ita kuwa Ummi tana falo, saida taga dawowarsu sannan taje ta shiga ɗakinta dan yanzu ta dawo da zama a nan kenan ɗakin da Umaymah ke sauƙa in tazo.

Washe gari ranar asabar kuwa,
haka suka wuni gidan shiru ba daɗi gaba e kewar Umaymah ta hanasu jin daɗin gidan.

Ranar ne kuma duban forko na watan Ramadan.

Tunda magriba tayi, al’ummar musulmai keta cekinta labarin ganin wata.
Wannan ya tambayi wancan wancan ya tambayi waccan.
Jira kawai akeyi aji lbri ko gani.
Yayinda duk irin wannan rana duk inda yanki musulmai suke a faɗin duniya suna jimirin da tsumayin lbri.
A wasu wuraren har matasa maza da dattawan kanyi dandazon da fuskanta yamma dan ganin watan

Har dai akayi sallan magriba babu ƙaƙƙarfan lbrin ganin wata.

Bayan anyi sallan isha’i ne, Sarki Nuruddeen Lamiɗo kenan ya tara hakima shi a fada suna jiran ko akwai ta inda labari zai riskesu.
Kasan cewar ana yanayin damuna ne yasa ba ko ina keda yaƙinin ganin watarba.

Sheykh Jabeer kuwa, wanda ranar bai samu yayi salla a masallacin Masarautar Joɗa ba.
Sabida wata ƴar tafiyar da yayi, sai bayan Isha’i ya dawo.
Kai tsaye Side ɗinsa ya wuce.
Yana shiga falon wayarshi dake cikin al’jihunsa ta fara suwa a hankali.
Gefen Ummi ya iso tare dayi mata sallama.
cikin kula tace.
“Sai yanzu?”.
Kai ya gyaɗa mata yana mai amsa wayar.
Sannu da hanya tace mishi.
Cikin sauƙe numfashin alamun gajiya yace.
“Yauwa Ummi sannu da aiki”.
Sai kuma ya kara wayar akunnen shi cikin nitsuwa yace.
“Wa alaikassalam”.
Ɗan jim yayi kana yace.
“Alhamdulillah”.
ya ƙarshe mgnar yana shiga cikin falonshi.

Shatu kuwa dake gefen Ummi shiru tayi tare da binshi da ido.

A can falon shi kuwa zama yayi bisa kujera tare da fara zare al’kyabbar daka hannunshi, wayar na kunnenshi yake cewa.
“Eh Jadda Alhamdulillah rahotanni sun nuna cikin Ɓadamaya al’umma da yawa sunga watan Ramadan.
Kuma nima naga watan Ramadan da idona”.
Cikin jin daɗi Jadda yace.
“Alhamdulillah, ko yanzu mun samu gamsassun hujjoji daga bakin salihan bayi,
Dan jihar Tsinako sarki Abudulfata da kanshi ma yaga watar ya sanarmin.
Hakama jihar Noki, Jaltarba, Magom, Shibb, da dai sauran jihohi mu na arewaci anga wata sosai tako ina.
Kana yanzu kuma munyi mgna da Sheykh Abdulkareem shima yace anga wata.
Mu nan jihar Leddi julɓe kusan kowa yaga wata.”
gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“To Alhamdulillah. Allah ya nuna mana ƙarshen sa lfy, yasa muribantu da watar al’farma Annabi da Alqur’ani”.
Amin Amin Sarki musulmai Jalaluddin, yace.
Kana ya sallameshi.

Daga nan aka bada sanarwan anga wata, inda shi Sarki Jalaluddin ya kira manyan masarautun gargaji yana shaida musu.
Kana manema labarai duk sukayi dandazon zuwa, nan aka sanar tako ina musamman kafafen yaɗa labarai na yanar gizo.

Nan take ko ina ya ɗauka.

Suna zaune a falon suna cikin hira.
Sukaji wani irin ƙara mai firgitarwa da bada tsoro.
darararam-dam sautin ƙarar bindigar toka mai ƙarfin amo.
Wani irin tsalle Shatu tayi tare da motsowa jikin Ummi, tare da toshe kunnuwanta, sabida sake jin ƙaran.
Gaba ɗaya jikinta kerma da kerketa yakeyi,
Cikin tsoro take cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun, hasbunallahiwani’imanwakil!”.
Da sauri Ummi ta riƙon hannunta datasa ta toshe kunnuwanta cikin ɗaga sauti take cewa.
“Shatu ba komaifa, kada ki razana bindigar sanarda ganin watane! Shaidar gobe zamu tashi da azumi”.
Cikin tsinkewar zuciya tace zamo daga kan kujerar ta zauna a ƙasa kusa da sawun Ummi, wani irin duka ƙirjinta keyi didib didib, didib.
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
“Aunty Aysha tsoro haka”.
Cikin yamutsa fuska tace.
“Ya kamata ku gayawa duk wani baƙo wannan bahugawar al’adar taku in ba hakaba wata rana tsoro zai kashe irina”.
Sheykh da tun ihunta na forko yana bakin corridor yana kallon yadda take karkarwa,
wani irin murmushin muguntane ya tsubce mishi.
Sai kuma ya tsuke fuskarsa kamar bashi yayi gajeren murmushi ba, cikin faɗa yace.
“Nifa bana son sakarci sam bafa na son anamin ihu a ka da hargowa a gida”.
Cikin tura baki ta bishi da ido.
Shi kuwa fita yayi yana murmushi a cikin zuciyarshi tare da magar zuci.
“Ga rashin ta ido ga tsoro, ga tsiwa da fitsara ga makirin karaya.
Ai da anyi ta sakin sautin bindigar har sai tayi fitsari a zani”.
Da haka ya wuce ya nufi fada,
nan suka fara tattauna yadda lamuran zasu tafi.

Ummi kuwa murmushi tayi ganin irin kallon harara da Shatu ta raka Sheykh dashi.
Cikin murmushi tace.
“Taso ki zauna muyi mgna”.
A hankali ta miƙa ta hau bisa kujerar da Ummi take ta zauna, Hibba kuwa, tuni ta nufi Side ɗin Aunty Juwairiyya.

Gyara zama Ummi tayi tana fuskantar ta da kyau,
Cikin nitsuwa tace.
“To Alhamdulillah kinga anga wata gobe zamu tashi da azumi in Allah ya kaimu, akwai ƙarin aiyuka a Side ɗin nan wanda ko da can baya ko Sheykh bayanan yana ajiye komai na buƙatar rayuwa akanyi girki a nan kamar akwai mace, sabida anan su Jalal, Jamil, Hashim Sulaiman Imran Affan in yana nan suke shan ruwa.”
To yanzu bana Sheykh ba inda zaije sabida a jerin jadawalin malaman tabsir da ake turawa jihohi bana ba’a turashi ko inaba tunda ya girma ya fara tabsir sau ɗaya yayi azumi a nan shekarar da ciwon Jafar ya tsananta, to anane naga zahirin yadda yake gudanar da al’amuran rayuwarshi cikin Ramadan.
To bana ma. Anan cikin Ɓadamaya zaiyi tabsir ɗin shi.
To aiyukan mu sunada yawa.
Dole kisan yadda tsarin komai ke tafiya.”
Cikin sauƙe numfashin ta gyara zama ta fuskanci Ummi da kyau kana a hankali tace.
“To”.
Itama gyara zama tayi da kyau kana tace.
“Azumi goma sha biyar zaiyi a nan, ƙarishen 15 ɗin a ƙasa mai tsarki zaiyi su.
Ma’ana zai tafi Umrah.
Sannan yanada masallatai uku da yake tabsir a kullum.
Da safe misalin karfe sha ɗaya na safe zai tafi masallacin jumma’a na cikin kasuwa, a can zaiyi tabsir sai ƙarfe shabiyu saura mintuna goma zai taso.
Daga nan kafin ya iso masarautar Joɗa tafiyar mintuna goma ne.
sha biyu dai-dai, zai zauna tabsir masallacin Masarautar Joɗa.
Sai ƙarfe ɗaya na rana zai tashi.
Daga nan bazai dawo gidaba, sai anyi sallan azahar.

To ana idar da salla zai shigo, gida al’adar rayuwarsace tun yana yaro.
Zaiyi baccin awa ɗaya tsakanin azahar da la’asar.
Ƙarfe uku dai-dai na yamma zai tashi zaiyi wonka, ya canza shiga, kafin ya gama an kira salla.
Yana fitowa zai wuce masallacin Masarautar Joɗa, inda yake limanci ana idar da salla zai tafi masallacin jumma’ar dake jami’ar Joɗa. Inda zaiyi tabsir daga ƙarfe huɗu zuwa biyar na yamma zai taso.

Akan hanyar shi ta dawowa yana tsayuwa wurin mashigar laleko zai sayo kayan buɗa baki ƴaƴan itatuwa.
Yana dawowa zai ajiyesu.
Ya wuce Side ɗinsa, wonka zaiyi kana yasa sauƙaƙƙun kaya, ya dawo falonshi ko ya wuce cikin Garden acan zaiyi ta karatun al’ƙur’ani ko kuma wani lokacin ya ɗan konta ya huta.

Kafin lokacin shan ruwa, Ni kuma da hadimar da Gimbiya Aminatu ke bani duk Ramadan ta tayani aiki.
Tuni mun gama aikin buɗa baki. An shirya komai a dinning table, nasu Jalal kenan.
Suma kuma gab da magriba zasu zo.
Shi ma zai fito yakan zauna tsakiyar Jalal da Jamil ko kuma tsakiyar Jalal da Jafar.

Baya cin abu mai nauyi iya karshi dabino da inabi da tuppa, sai ruwan zam-zam wanda dashi yakeyin buɗa baki.
Daga nan zai wuce masallacin Masarautar Joɗa wani lokacin zai fita dasu wani lokacin zai rigasu fita.

Ana shirya mishi abincinsa na musamman a ajiye mishi a dinning table ɗin dake can falonshi a Foodflaks ɗin shi na musamman, wani lokacin Gimbiya Aminatu ke aiko mishi.

In ya fita bazai dawoba sai anyi sallan isha’i Dana asham.
Amman su Jalal su zasu dawo suci abinci kafin isha’i sai su koma masallacin.

Idan ya tashi daga Masallacin kai tsaye zai wuce.
Gidan radiyo ABC Ɓadamaya, inda yake gabatar da shirin.
“Fatawa. Za’a ayi mishi tambaya kan Ramadan dama sauran abinda ya shafi addini yana amsawa, wasu kan tura tambayoyin wasu kuma kira sukeyi a da number da ga suke badawa, suyi tambaya ya bada amsa.
Ƙarfe takwas da rabi ake fara shirin tara dai-dai ake gamawa.
Tara da mintuna ashirin yake isowa gida”.
Ɗan tsagaitawa tayi ta kalli Shatu dake cewa.
“Tab agogo sarkin aiki to shi baya gajiya ne, ga azumi ga zirga-zirga ga kuma duk inda yaje dole ba shiru zaiba mgna zaiyi ai ƙishi zai mishi illa”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“To ai in yaje gidan radiyo tarba ta musamman akeyi mishi, sai dai shi ba ko ina yake cin abinci ba tunma yana yaro.
Ko a gida nan ba abincin kowa yake ciba.
To shiyasa tara da rabin nan zai dawo a gajiye cikin yunwa,
to nan zaici abinci sosai.
Kana yayi wonka zuwa sha ɗaya dai yayi bacci.

To ƙarfe biyu kuma zai tashi, wani lokacin ma biyu bayayi zai tashi yayi ta nafilfilinshi da karatun Alqur’ani.

Daga nan kuma baya komawa bacci.
Har ayi sahur ayi sallan asuba.
In ya dawo yayi Azkar, to nanne yake samun yayi bacci mai tsawo dan tun bakwai da rabi ko takwas na safen zaiyi bacci sai goma zai tashi ya fara shirin tafiya masallacin jumma’a na kasuwa.”
Kallonta ta ɗan yi tare da cewa.
“Kin gane lokutan da yake aiki Dana hutuwa dana bacci ko dana cin abinci ko?”.
Cikin murmushi tace na gane.
“Da safe zai sha bacci son ranshi, daga takwas zuwa goma kafin ya tashi ya shirya.
Yaje masalacin jumma’a na kasuwa sha ɗaya tayi yayi tabsir ɗin awa ɗaya, daga nan ya dawo masallacin Masarautar Joɗa,
shabiyu ya fara tabsir sai ƙarfe ɗaya ya gama, ayi salla ya dawo.
Ya sake shan baccin awa ɗaya.
Kafin kuma ayi la’asar ya tafi masallacin Joɗa state University. Yaje yayi tabsir in ya dawo, kuma ya lokacin hutawane har magriba.
Daga nan kuma ayi buɗa baki a wuce masallacin daga can a wuce ABC.
Sai tara a dawo.
To yaseen wataran yunwa zata kadashi a hanya, ƙattin rigunan nan da yake sawa sune zasu jashi su kaishi ƙasa.
To ma wai Ummi to yaushe yake zuwa aiki kuma?”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“To in baya garin an turashi wani state ɗin yana zuwa aikin ne?”.
Kai ta girgiza alamun a a.
Cikin murmushin Ummi tace.
“Shiyasa ko yana nan in dai a Ramadan ne baida lokacin zuwa Valli Hospital, bare Genaral Hospital ko kuma Asibitin jami’ar Ɓadamaya.
Shine dalilinshi na ƙin yin aiki a asibitin gwamnati sai ƙarshen sati-sati yake zuwa sau ɗaya, duk wanda zai duba kyautane aiki”.
Naɗa hannunta tayi tare da cewa.
“Batun yunwa ta kadashi kuma, yanzu aikin kine, kula da abinda zaici”.
Taɓe baki tayi tare da cewa.
“To shi wannan da tsarabe-tsaraben falsafa nasan irin abinda zai cine ma.
Mutun fuska a haɗe kullum kamar mai damuwar rashin jigo”.
Miƙewa Ummi tayi tare da cewa.
“To kika sani ko hakanne.
Kuma ai gani duk abinda kike son sani a kanshi tambayeni.
Abincin da yafiso kuma yafi son ganyayyaki, fruits and vegetables sai kuma kayan ruwa, kana yana son nama da kifi in an mishi irin sarrafawar da yakeso.
Sannan yana son abincin gargajiya wasu lokutan musamman a wurin yin sahur.

Kai ta jinjina tare da cewa.
“Uhumm lallai kam, wannan ai yafi Lamiɗo ma iya ƙasaita”.
Dariya tayi tare da cewa.
Zo muje store kiga kayayyakin da yasa aka kawo ɗazu.”

To tace tare da miƙewa tabi bayanta.
Suna shiga kitchen ɗin suka ɗan haura suka taka steps ɗin da zai sadasu da ƙofar store wanda wani ƙaton freezer ke konce a wurin sai ma dai daicin Fridge.

Hannu Ummi tasa ta buɗe freezer’n.
Motsowa tayi tare da zaro ido ganin yadda aka cika freezer’n maƙil dasu Kabej Karas kokumba green beans, masu kyau sabbi.
Ɗaya sashin kuma nama ne jibge sai kifi a gefe,

Sai ɗaya Fridge ɗin kuma cike yake da ababen sha na ya’yan itatuwa dana kwalba.

Rufewa tayi kana ta buɗe mata drower’n kitchen cabinets ɗin.
Kiret-kiret ɗin kwaine kusa goma suke jere a wurin ɗaya gefen kuma katon ɗin manyan gongonayen madara da millo ne.
Sai katon ɗin sugar irin mai ƴaƴan nan. Sai katon ɗin Lipton. Da ganyen na’ana. Sai can gefe kuma su maggine da sauran kayan ɗanɗano.
dasu kanan fari citta da dai sauransu.
Cikin yin hamma tace.
“Ummi duk yaushe aka kawosu?”.
Juyawa tayi suka nufi cikin cikin store tace.
“Ɗazu da yamma kina bacci ya dawo, suda Jalal da Jamil”.
Kai ta gyaɗa tare da bin bayan Ummi. store ɗin cike yake da kayan masarufi na buƙatar rayuwa.
Danginsu shinkafa, gero, waken suya, wake ƙosai dasu alale, sugar katon-katon na taliyar manya data yara, da dai sauransu.

Sai kuma doya da dankali dake jibge a gefe, kana sai al’basa da sauransu.

Fitowa sukayi kana suka dawo kitchen.
tukunya Ummi ta ɗaura tare da ɗebo nama tazo ta wonke sabida an yanka wasu dai-dai misalin na miya, wasu kuma anyisu dogo-dogon yanka.
a tukunyar ta zuba shi, kana ta ɗauko al’basa mai girma ta yayyanka a ciki.
Sannan tasa tafarnuwa kaɗan kana tasa garin citta da kanamfari.
Tare da maggi da kori da sauran kayan ɗan-ɗano.

Kana ta kunna Gas ɗin ta ɗaura tukunyar,
ɗanyen kuɓewa ta ɗebo ta miƙawa Shatu tare da cewa.
“Wonke ki yanka min shi”.
To tace tare da amsa ta wonke kana ta fara yankawa, ita kuma Ummi al’basa da tattasai da tatuhu kaɗan ta ɗiba ta wonkesu kana ta markaɗesu dai-dai yadda takeso.

Zuwa lokacin kuma gaba ɗaya kitchen ɗin dama Side ɗin gaba ɗaya ya cika da ƙamshin tafashen naman.

Juyeshi tayi a wani kwano.
Kana tasa mai kaɗan tasa manja kaɗan. Tare da watsa jajjagen kayan miyar,
ta soyasu. Kana tasa naman da sauran ruwan tafashen.
ta kuma ɗauko bandan kifin tarwaɗa bandanshi, ta gyara ta wonƙeshi da ruwan ɗumi.
ta watsa a ciki. Sannan tasa ɗan dakekken yajin daddawa kaɗan.”
sannan ta rufe tukunyar.
ta amshi kuɓewar tana ƙarisa yankan. Tukunyar data ɗaura ruwan tuwo ta ɗan kalla ganin yana tafasane tace.
“Gacan garin semo na tankaɗeshi ɗibi kiyi mana talge.”
To tace tare da juyawa ta ɗebo tayi talgen.
Ita kuwa kuɓewar ta saka, kana ta tsalli ɗan toka ta saka.

Bayan wasu yan daƙiƙu miyar tayi lugub tayi kyau tayi kalar kore mai kyau. sabke tukunyar tayi kana tasa,
man shanu a ciki.
Sannan ta meda tukunyar gefe.
Tuwon ta tuƙa ya ɗan turara kafin ta kwasheshi tana yin mal’mala tana sawa a leda.
Saida ta cika wani madaidaicin Foodflaks mai ɗan girma.
Kana ta ɗauka ruwan zafi.
Ta tafasa tea ta ɗura a flaks tare da tarfa kanumfari da citta sai na’am.
Sannan ta rufe, ta kimtsa komai a kitchen ɗin.
Ganin Shatu nata Hamma ne tace.
“Jeki kwanta tunda mun gama aikin. Sai kuma da asuba.”
Cikin alamun bacci tace.
“To Ummi saida safe”.
Ta fita tana haɗiye minyau dan ƙamshin da miyar keyi.

A falo taci karo da Hibba Aunty Juwairiyya ta rakota, da Foodflaks a hannunsu alamun abincin sahur ne a ciki.
Cikin baccin da takeji tace.
“Mun yi girki ma, Aunty Juwairiyya”.
Kai Juwairiyya ta ɗan gyaɗa tare da cewa.
“A lallai kam sannu da aiki”.
Ta ƙarishe mgnar tana ajiye kulolin bisa dinning table.
Ita kuwa Shatu harara ta watsawa kulolin tare da wucewa tayi ciki.
Hibba ce ta biyo bayanta bayan tayiwa Aunty Juwairiyya Saida safe.

Har sun shiga Ummi ta kira wosu.
Falo suka dawo duk suna hamma alamun bacci, ganin Hamma Jabeer na zaune ne, gasu Jalal gaba ɗaya yasa suma suka ƙarasu cikin falon.
Gyara zanshi yayi tare da kallon Hibba da Aysha da duk alamun bacci ya cikasu, cikin sakekkiyar murya yace.
“T….!

 

 

Uhummm Ramadan da daɗi, Ya Allah ka nuna mana ka kaimu watan lfy ka nuna mana ƙarshensa lfy ka maimata mana.

Rayuwar Masarautar Joɗa a Ramadan yanada tsari da masifar daɗi da burge duk musulmi.

Kabcen Shatu da Sheykh a kwanakin Ramadan da bikin salla yana sani murmushi da shauƙi.😘🥰🤝🏻

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button