Hausa NovelsIn Bani Hausa Novel

In Bani 19

Sponsored Links

19….

 

_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan ko pay achan_

Related Articles

_in kinason novel dinan zaki turo just 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment to my watsapp number 07012181461_

_you can also send MTN card zuwa watsapp number na 07012181461, sainai adding dinki a group din danake posting_

 

 

Ya wrapping his left hand around her waist yana shesheka kuka sosai yana kissing dinta, da sauri Kaka daharta kai kofar dakinta tasake juyowa tadawo bakin kofarta ta buga kofan cike da masifa tace “wai lafiyan ki Hamida rukuku rukukun menake ji kaman bera na barna?” da sauri ya kabar da hanunta dake kirjinshi tana tureshi cikin hawaye yasake fadawa jikinta yay lamo kirjinshi na bugawa sosai while kissing har lokacin batare daya denaba, runtse ido tayi da kyar ta daddage ta fizge bakinta daga nashi zata tureshi ya riketa sosai yana make mata kafada yana kallonta yana kuka ahankali mara kara, da kyar ta iya saita muryanta gudun kar Kaka ta zargi wani abu tace “Kaka bacci, kidena tashi na” tsaki Kaka tayi tace “kyaji dashi ja’ira kawai, abincin ki na falo dai koda yunwa ta farkar dake cikin dare kije ki dauka” tana maganan tai hanyar dakinta ta shige ta rufo kofa dan itama tagaji yautai aiki da rana, jin karan rufo kofar dakin Kaka yasa ta tureshi daga jikinta da karfi, komawa baya yayi yana turo baki yana share hawayen da yakeyi da bayan hannu, share hawayen daya kasa dena zubo mata tayi ta kalleshi kaman ta zubamai mari dan takaici, yanda yake kallonta ya tsaya a inda ta turashi yana goge idanunshi da bayan hannu kayan jikinshi sunyi daka daka yasa taji yasake bata tausayi dan wanan asibiti yake bukata, ahankali ta saita muryanta ta kalleshi tace “inane gidanku?” dan matsowa yayi kusa da ita da sauri dan kaman jira yake dama tamai magana, da sauri ta matsa takoma kan gado ta zauna, juyowa yasakeyi ya kalleta daga inda yake a tsayen a tsakiyan daki yace “gidan mu?” da sauri ta kallai jin yay mata magana ta gyadamai kai tace “eh gidan ku” kallon yatsunshi yayi yana turo baki yace “gidan mu na chan chan, there’s basketball field in our house, Bid and I use to play basket ball” yay maganan yana mata murmushi yana juya mata manyan idanunshi looking super cute, da sauri ta janye idanunta daga kanshi ganin ayanda yake magana ma baisan inda gidansu yakeba yasa ta shiga damuwa sosai. Innalillahi, ita yanzu yazatayi dashi tabani, tayaya ma zatayi ta fitar dashi daga gidan nan yanda ya shigo dinan batare dawani ya gansu tareba?, cikin tsaka da tunani taji mutum ya zauna kusada ita da sauri ta dagokai ta kalleshi kafin ma tai wani yunkuri ya daura kanshi akan kafadarta yana turo baki yace “am hungry” yay maganan yana lumlumshe ido, tsabagen tsorata yasa ta tura kanshi daga kafadarta ta tashi daga kan gadon da sauri tana nishi tace “bari na daukoma abinci” tai hanyar kofa tashi yayi da sauri ya biyota salati tayi a tsorace tace “innalillahi dan Allah ka zauna abinci zan daukoma” make mata kafada yayi hawaye na sake taruwa a idanunshi, sake rudewa tayi dan dazaran yafara kuka zai tona mata asiri jarumta tayi ta daura hanunta akan bakinshi ta rufemai baki da sauri ya ware manyan idanunshi ya kalleta, murmushi tamai tace “yauwa yayama sunanka?” tai maganan tana jan hanunta daga bakinshi da sauri shima yay mata murmushi daya wani irin karama fuskarshi kyau yamata fari da ido a shagwabe yace “Aadil, but Bid use to call me Dil” yanda yay maganan was damn mesmerizing da sauri ta kawad dakai tace “okay muje ka zauna I will bring food and paracetamol for you ok” tai maganan tana nunamai saman gado, zama yay akan gadon yana rike hijabinta ya turo mata baki tareda mikamata kafarshi ya lankwasar dakai a shagwabe yace “remove this shoe from my leg am tired” kallonshi tadanyi kafin ahankali ta tsugunna ta warware igiyan ta ciremai takalmin ta ijiye, ya miko mata dayan kafan ta ciremai shima ta ijiye duk yana kallonta, yace “will you come back?”

 

Yi tayi kaman batajishi ba ta shareshi ta mike tsaye zata wuce, fizgota yayi da karfi atsorace tajuyo saura kiris tafada kanshi ta cije da kyar ta ta kallai, marmar yay da ido kaman zaiyi kuka yace “will you come back? Don’t leave me again pls” gyadamai kai tayi da sauri ta dauke kai ahankali ya saketa ya washe mata baki yay tafi yace “yay am happy” juyawa tayi tai wajen drawer dakin tajawo dan taga Kaka na yawan zuba makulli a drawowin wajen duk yana binta da kallo kaman zai cinye ta da idanu, wani makkulin kwado ta dauka taboye ta hanyar rufe hanunta ta maida drawer tai hanyar kofan dakin ta cire sakata tadan waigo hada ido sukayi har lokacin kallonta yake ya washe mata baki white teeth dinshi suka fito da sauri tafita daga dakin ta tsaya ta ta rufo kofar dakin ahankali gudun karta tashi Kaka tadau key tasaka sanan tai hanyar falon tadau kulan tuwonta da miya sanan tai hanyar doguwan kujeran Kaka tadau kwalin paracetamol din Kaka dake ajiye awajen tabude taciro sachet guda daya tamaida tarufe ya ijiye takwashi kulan tai ciki, agaban dakinta ta tsaya ta ajiye kulolin akasa sanan tasa key tabude kwado ta bude kofan ta kwashi kulan ta shiga ciki tana kallon fuskar Aadil ganin yanda yake kwance kan gadonta ya lumshe ido, ajiye kulan tayi tarufe kofar tasaka sakata sanan ta dau kulan tai wajen gadon ta ijiye akasa tana kallonshi yanda yake numfashi ahankali ahankali yana bacci, yay wani irin kyau kaman ba shine mara lafiya ba, da sauri tadena kallonshi dan sosai fuskarshi yacika mata ido, ahankali takai hanunta dake rawa sosai ta buga katifar muryanta nadan rawa tace “A..Aadil” ko motsi baiyiba bacci yay gaba dashi sosai, kallonshi tayi ta kafeshi da idanu hakanan taji tanajin wani irin tausayinshi, ahankali ta mike tsaye ganin yay bacci yasa tai wajen sip ta bude sip din tana kallon jerin nikakkun kayan ta dake ciki, wani simple free doguwan rigan atampa ta dauka ta maida sip din tarufe tai hanyar bayi, sake juyawa tayi ta kallai ganin har lokacin baccinshi yake yasa tabude bayin ta shiga ta garkama sakata, ahankali tacire hijabinta dayay duku duku ta saka cikin wani empty bucket, tazare kayan jikinta ma duk tasa a botukin sanan tafara wanka, wankan tayi sanan ta tsane jikinta tadau doguwan rigan data shigo dashi ta saka tai alwala sanan tabude kofan ahankali tafito har lokacin bacci yake sip tabude taciro wani hijabin tahau kan dadduma tafara biyan sallolin da ake binta, saida tagama sanan tacire hijabin sabida zafin datake ji sosai ta ijiye hijabin akan dadduma ta juya ta kalli Aadil dahar lokacin ke bacci sosai, ahankali ta matsar da hijabin saman dadduman ta kwanta ta daura kanta kan hijabin datai filo dashi tana kallonshi zuciyarta na tambayarta yazatayi dashi? Ta ina zata fara neman gidansu? Tayaya zata fitar dashi daga gidansu batare da anganshi ba? Idan aka ganshi mezata cema Abba, Mama, Kaka, da Ya Faruk? Yayama zatayi da wanan babban mutun din? Kodai to takaishi asibiti ne adubashi? To ta ina zata sami kudin? Yaya zatayi ta nemo gidansu yanzu? Takai kusan 10min tana kallonshi tana tunane tunane kafin ahankali tajuya mai baya cikin maganin bacci ta kwanta ta hannun damanta wani wahalallen bacci yay gaba da ita.

Kaman amafarki taji ana mata kuka awuya ana bubbuga mata ciki ana shurinta da kafa ahankali, da kyar ta iya bude idanunta cikin bacci tadan juyo Aadil tagani ya kwanta agefen ta yachusa kanshi awuyanta yana mata kuka sosai gabaki daya hawayen shi nabin wuyanta some nabi har cleavage dinta, hanunshi nakan cikinta yana bubbuga matashi yana kuka, sosai tawani irin tsorata tafara ture kanshi daga wuyanta bakinta har rawa yakeyi tace “d…dagani, menene mekake so? Please dagani, katashi daga jikina I can’t breath” make mata kafada yayi batare daya tashiba cikin kuka sosai yace “a…am hungry, my stomach hurts”
_🌹IN BANI 🌹_

 

Maman Abd Shakur

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button