Hausa NovelsTayi Min Kankanta Hausa Novel

Tayi Min kankanta 24

Sponsored Links

24*

Kuka sosai hammad yakeyi yaƙi ɗago kansa,zahra kasa jure kukan tayi tasa hannu ta ɗago kansa da sauri ya buɗe ido yana kallonta.

Fuskarshi ta riƙe da duka hannayenta,tana hawaye,cikin kukan tace”yaya hammad why?”

Related Articles

“ƙaddara zahra”ya bata amsa bakinshi na rawa,

Kifa kanta tayi a goshinshi ta saki kuka me tsuma zuciya tun bayan da tasan shine soja me ulcer se yau tayi kukan da takeso tayi.

Rungumota jikinshi yayi,ba musu tayi lub a ƙirjinshi tana masa kukan.

Shuru yayi ya kasa rarrashinta,se bayanta da yake shafawa,dan kanta tayi shurun,amma batace komai ba se ajiyar zuciya da take saukewa akai akai.

Ahankali ya furta”kin haƙura zahra ta,?”kai ta ɗaga masa,hannu yasa yana shafa kan nata sannan ya sake faɗin”kin yafewa yayan naki?”

“Na yafe maka yaya,Albarkacin yafiyar da nayima Allah yakai ladan kabarin innata,kuma insha Allahu bazan kuma ɗago da maganar ba Allah yacire min hakan araina amin”ta faɗi cikin muryar kuka.

Janyota yayi gaba ɗaya ta faɗo jikinshi ya rungumeta yana jin kamar wani ze ƙwace masa ita,a kunnenta yake raɗa mata jawabin godiya,lumshe ido tayi tana sauraronsa,

Seda ya tabbatar da bata da sauran damuwa ya dena mata godiyar,

Miƙewa tayi daga jikinshi,sa sauri ya ruƙo hannunta ya marairaice yace “ina zaki ki barni,baby ta?”

Cikin shagwaɓa tace”najima da shigowa kar mummy tajini shuru shine zan tafi”

Miƙewa yayi ya ƙarasa gabanta,yana ƙare mata kallo,son ta na daɗa tasiri a zuciyarshi,hannu yasa ya kamo ƙugunta,ya mannata da jikinshi ya ɗan rankwafo setin fuskarta,yace a sanyaye “to ay baki faɗamin abinda kika faɗamin ba”

Kauda kanta tayi gefe dan yanayin yadda yake maganar sosai yake saukar mata da kasala,hannu yasa ya dawo da fuskarta setin tashi ya sake kashe mata ido gami da ɗaga mata gira yace”oya now talk to me baby”

Kasa jure kallonshi tayi dan haka a sanyaye ta kwantar da kanta a ƙirjinshi tace”makaranta nakeso in koma,shine mummy tace seda izininka”

Ɗago kanta yayi yana kallon bakinta,yatsansa yasa yana shafa lips ɗinta cikin salon siye zuciya,yace,”me isa kike shafa janbaki kullum?”yayi maganar bakinshi dede nata,a kunyace tace”yaya haka bakin yake ni ban sa janbaki ba”tayi maganar kamar zatai kuka.

Sosai ya ƙara matseta ajikinshi yace cikin muryar da ta fi kama da raɗa”in duba in gani dan in tabbatar?”
Wani abune zahra taji ya zubo mata a pant sabida yadda hammad ke shafa lips ɗin nata,da yadda yake magana.

Kai ta gyaɗa masa,ba tare da tace komai ba,ɗan ɗago haɓarta yayi,ya ɗora bakinshi akan nata,da sauri zahra ta lumshe ido,laɓɓanta ya shiga tsotsewa cike da ƙwarewa yana ɗan kamosu yana saki,gamida dan shafasu da harshenshi.sosai zahra ta sauka akan network dan bata taɓa sanin kalar wannan duniyar da suke cikiba.sosai abun ke mata daɗi,
Tsayawa yayi ya ƙare mata kallo,yaga yadda ta runtse ido uwa uba tawul ɗin jikinshi da ta damƙe a hannunta,tana ɗan cije leɓe,ya fahimci in ya ɗorata akan tsarin zata dinga hawa akan lokaci.

Maida bakinshi yayi akan nata yaci gaba da tura mata saƙon.
A haka ya jata zuwa kan gado.

Muje zuwa

Surbajo for life.
[1/6, 10:15 AM] Zahra Surbajo: 🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀
*TAYI MIN ƘANƘANTA*
🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀🎀

*Zahra Surbajo*

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button