Hausa NovelsWata karuwa Hausa Novel

Wata karuwa 43-44

Sponsored Links

43-44*

 

Girgiza kai tayi tare da sakin murmushi me ciwo ta koma ta kwanta zaiyi mgn tace “kaje don Allah kaje amaryarka na nemanka” banson shiga rayuwarta wannan tasa ya fice daga ɗakin bayan ya ɗauki Nafeesah ya zauna a falon yanajin wani nishaɗi yau shine da yara biyu tabbas Allah ya cika abin gdy, yananan zaune Hassy ta fito ta ɗauki wankanta na kyau abinka da dama gwanar kwalliya tana ganinsa da yarinyar taji wani mashin baƙin ciki ya caki ƙirjinta taji zuciyarta na raya mata ta juya haka dai ta ƙarasa ta zauna a gefensa tana shafa kuncinta tace “Bby shine ka gudo ka barni wannan jaririyar fah?” Zuba mata ido yayi yana raya abubuwa da yawa a ransa can tace “kayimin shiru baka bani amsa ba” kawar dakai yayi da cewa “na zaci na faɗa miki matata ta haihu ana gobe ɗaurin aurenmu….”
Saurin zaro ido tayi da sigar mamaki tace “Wow! Abdul baka faɗamin ba ka manta kodai niɗin na manta muga babyn gata kuwa kyakkyawa” yanda ta rungume bbyn tanayi mata wasa yasashi jin nishaɗi ya saki ransa suka rinƙa ƴar hirarsu suna zaune Mother ta shigo ya miƙe da girmamawa kamar yanda suka saba itakuwa Hasina mursisi tayi taƙi tashi Mother ta dubeta ta watsar tare da duban Abdul tace “ka kawomin Nafeesah ɗakin uwarta ba kowanne hannu nakeson yake taɓa ta ba”

Related Articles

 

Ba ƙaramin Girgiza Hassy tayi da jin kalamin uwar mijin nata ba amma batada ta cewa haka ta miƙawa Abdul-Ahad babyn ya karɓeta yabi bayan Mom ya isheta tana aikin rarrashin Aneey data kifa kanta a cinyarta taketa kukanta me ciwo sosai Abdul ya shiga damuwa ya juya ya fice da sauri gabansa saici gaba yakeyi da faɗuwa baibi takan Hassy ba ya fice a gdan Hasina tabisa da kallo tare da taɓe baki tace “yaro man kaza dagakai har matar taka da uwarka saina hanaku rawar gaban hantsi muje zuwa dai tunda kunce zakuja dani nima zan ja daku”
Tana gama faɗin haka ta shige ɗakinta ta ɗauki waya ta kira number Mama ta zayyane mata komai Mama tayi dariya tace “saura ƙiris ki ƙara hƙr nan da kwana biyu komai zai kammala yanzu dai ki turo kuɗi in akwai Mal na kan tsauni kuɗi yake nema kafin yayi aikin nan don yace shaiɗanun da zaisa suyi aikin masu taurin kaine dole sai sunsha jini zasuyisa” babu musu Hasina tace “Ok zan turo yanzu” tana kashe wayar tayima Mama transfer na msnyan kuɗaɗe sannan ta faɗa wanka bayan ta fito tayi shirin kwanciyarta ta haye gado.
Tun bakwai ya shigo gdan ya tafi gurin Aneey yanata janta da hira duk a burinsa na ganin ta saki jiki dashi duk da zuciyarta tana raya mata abubuwa da yawa akansa h
Motsinsa batason gani a sashinta hakan baisa taƙi sauraronsa ba har dariya take tayashi, idanunta takai ga agogo taga 11:30pm ta dubesa da sauri tace “Prince dare yayi fah matarka tanacan tana jiranka” kanne mata idanu yayi yace “ke kuma budurwa tace?” Kawar dakai tayi tace kaje ka kwanta Allah bamu alkhairi”

 

Murmushi yayi yace “kinason ki rinƙa korata ko Wyf meye laifina ne akan abinda ban isa canzawa ba kiyi hƙr dani ki manta da komai ina yawan maimaita miki inasonki bazan taɓa daina sonki ba idan na cika gdannan da mata to kece gwanata kece rayuwata kece zuciyata…..”
Rufe masa baki tayi tana murmushi tace “nasani nima inasonka mijina kaje gurin matarka
Banason shiga haƙƙinta idan muka fara yanzu gaba nima zakuyimin kuma zanji babu daɗi kabarni kaje Please Abdul saida safe” ya zaiyi dole ya miƙe yayi kissing nata ya fice ta share hawaye ta kwanta zuciyarta na kai kawo a ƙirjinta tana kishin mijinta tanajin dama komai ya zame mata ba komai ba tashi ta kumayi zaune ta ɗaga hannunta tayi addu’a me tsayi ta sake kwanciya.
Cikin kwana biyun kulawar da Abdul yake bata ko haihuwarta ta farko bata samu hakan ba har akayi suna riritata yakeyi.

 

Itakam Hassy zuciyarta har neman tarwatsewa takeyi saboda yanda zaman gdan ya zame mata babu daɗi gadai Abdul ta samu ta aura amma ta kasa samun farin ciki dashi bashi da lkcnta ko kaɗan Indai taganshi yana walwala yana dariya to shi da Aneey ne gashi ƙarin tashin hankalinta tunda aka kawota gdan yaƙi haɗa jiki da ita ko taɓashi tayi saiya janye idan ta matsa masa ya rufeta da faɗa wannan tasa dole ta tattarashi ta watsar dashi taci gaba da aikinta ta ƙarƙashin ƙasa.
Bayan suna mutane kowa ya koma gdansa gdan ya rage sai su isu Aneey lfy bata isheta ba bata iya yima yaran komai ita kuma Hassy ko falon bata fitowa ya zamana saidai komai Jimba tayi a gdan wai sunan da mace bayan mara lfyr a gdan, ransa ya ɓaci ya shiga har ɗakinta yayi mata mgn ta kuwa fusata ta kama farfaɗa masa maganganu aikuwa ransa ya ƙara fusata shi dama tun da can a rayuwarsa baya ɗaukar raini aikuwa baisan saida ya ɗauketa da mari ba kuma yace mata dolene tayi ko bataso ita kuma ta rantse akan ba bautar uban wani tazo ba.

 

Baiyi tunanin komai ba yace mata muddin zata zauna dashi to saita cire komai a ranta idan kuwa taƙi to tama haɗe kayanta ta koma inda ta fito, to jin furucin da yayi ne yasata dole take fitowa take ayyukan gdan shi kansa aikin bawai tanayi yana burgesa bane kawai dai tanayine saboda kiyaye aurenta.
Cikin lkcn ne kuma ta samu nasarar abinda take shiryawa komai ya fara jagulewa tsakanin Aneey da Abdul to abin baiyi ƙarfi ba sai ranar da tayi arba’in ya kama zai koma ɗakinta tun yamma yaji gabansa yana faɗuwa tsoro yana shigarsa har zuwa dare ya dawo ya shigo gdan ya ishe Hassy zaune a falon ita da Mutallab tanajin tsayuwar motarsa ta kamo Mutallab ta fara yi masa wasa yanzu salon data ɗauka kenan dake namiji soko ne shikuma wani daɗi yakeji wai tanason ƴaƴansa.
Zama yayi yayima Mutallab wasa ya dubeta yana murmushi yace “Duk kin rame meye yake damunki ne?” Sunkuyar da kanta tayi idanunta ya kawo hawayen kirsa tace “ni bansan meye yasa ka aureni ba kwana arba’in da ɗaura aurenmu amma ko yatsana baka riƙewa don ra’ayin kanka Abdul ya kakeso nayi ne in a baya inada yanda zanyi na samawa kaina sauƙi yanzun wacce hanya ke gareni dubi tun jiya kake rawar ƙafa matar sonka zatayi arba’in zaka samu abinda kakeso Ni kuma ko oho”

 

Miƙewa yayi da Mutallab a hannunsa yayi gaba batare da yabata amsa ba yana taka ƙofar sashin na Aneey yaji kamar an buga masa wata guduma a bayansa ya durƙushe da sauri jikinsa ya ɗauki rawa yace “Innanillahi Wa Innah Ilaihirraji’un…..” Daƙyar yakai saboda bugawar da zuciyarsa takeyi da ƙarfi daidai lokacin da Aneey ta fito sanye da wani blue ɗin leshi ɗinkin doguwar riga tayi kyau sosai ta baza gashinta a kafaɗarta sai walwali yakeyi ta tsaya ta zuba masa ido yayi shima ita yake kallo ya miƙa mata hannu ta miƙa masa ya rike ya miƙe tare da janyota jikinsa ya mannata yanajan wata wahalalliyar ajiyar zuciya yace “Inajin kamar banida lfy Wyf” saurin ɗora hannunta tayi a ƙirjinsa tace “baka addu’a ne baka damuwa da karatun ƙur’ani shiyasa shaiɗanu suke saurin hudaka Prince banso na Barka ka shigo sashin nan ba naso kayi zamanka nazo na sameka”
Ɗago fuskarta yayi yace “For what?” Lumshe idonta tayi tace “ka manta zaka fahimta daga baya karka damu da yanzu kaji” bai sake tambayarta ba tajashi suka fita suka shiga ɗakinsa wani abun mamaki sai yaji kamar an cire masa yanayin da yakeji Aneey ta zage ta cire kunyar komai ta kula da mijinta hatta wanka ita tayi masa yanata haɗiyar yawu yayi matuƙar ƙoƙari tunda ta haihu bai sake kusantar mace ba shi ya rasa meye yasa kawai yanzu yake ƙyanƙyamin Hassina baya ƙaunar haɗa jiki da ita.

 

Mai ta shafeshi dashi ta fita har yanzu Hasina na falon ta haɗiyi takaici kamar ta tarwatse tayi mata murmushi tare dace mata “Sannu” ta wucce cikin kitchen din ta buɗe abincinsa data shirya masa kawai zuciyarta taji bata nutsu da abincin ba ta bude frigde ta ɗauki nono da farar shinkafa ta kaɗa masa ta zuba masa suger da madara ta jefa ƙanƙara ta ɗauka da lemo ta wucce Hassy ta nufi part ɗin nata ta ajiye masa sai binta yakeyi da kallo da wata muguwar mutuwar jiki yace “ni ki ƙyale abincin nan kiyimin maganin matsalata wlh sex kawai nake buƙata”
Girgiza masa kai tayi tace “kasan komai da ƙoshi yafi tafiya idan ka koshi zakafi ganewa wancan ƙoshin ma ina fatan ka gane” turo baki gaba yayi yace “ni ban gane ba….” Dariya tayi taja da baya ya mike ya janyota suka zube a gadon ya kalleta itama shi take kallo suka haɗa idanu suka sakarwa juna murmushi yace “nono zansha abani nasha” rintse idanunta tayi tana dariya ya zuge zip na rigarta ya ɓalle bra ɗin ya kama nononta da suke tsaye kamar ba shayarwa takeyi ba yaja ajiyar zuciya ya ɗora bakinsa akai itama ta sauke me ƙarfi ta tallafe kansa zatayi mgn ya rufe mata baki tare da kai hannu ya kashe musu glub daga nan babu abinda kakeji sai nishinsa da magiyar da takeyi masa Hassy data laɓe jikin ƙofar kamar tayi hauka saboda kishi tanajinsa yanata yiwa Aneey kukan daɗi sai yau ta raina kanta ta yarda iya masifarta bazata iya shiga tsakaninsu da ƙaramin asiri ba dole saidai tsafi ɗakinta ta shiga ta kira wayar ƙawarta Zee ta zayyane mata komai tace “Zee dubu ɗari da hamsin na bayar akan yau ɗin nan ayi komai a gama gayyar ta watse akace nayi turaren a kofar ɗakinta sannan na yayyafa ruwan rubutun ma a ɗakinta Indai yashiga to tarihinta ya goge sai yayi mata korar kare amma shegiyar kamar wadda ta gani duk ta rusamin komai tajashi ɗakinsa acan sukayi komai har laɓewa nayi don naji ya zata kaya amma banda damuwa babu abinda na jiyowa kaina Zee kiyi wani abu Allah ko nawa zan iya kashewa”………

 

*Ki tausaya karki fitar mana dashi in kin siya ,Inkin san siya zakiyi don kiyi sharing don Allah karki siya mun hutashsheki,Haƙƙin mallakar marubutanne su kaɗai,Ki tausaya masu plz ,Inkinga wani pages na yawo to na sata ne ki runtse idonki karki karanta ki biyo ki siya ,Mungode*

 

•┈┈┈••✦✿✦••┈┈┈•
_*WATA KARUWAA* Na kuɗine ,Zafafa ne🔥 Cikin jerin gwanon *TAURARI UKU🔥🔥🔥✨ MASU HASKAWA💡* Da suke zuwa maku daga alƙalumman gwanayen marubutanku,Taurari Uku ✨Masu Tashe ,wanda suka haɗa da:_
_*WATA KARUWA* Daga Alƙalamar OUM HAIRAN_
_*SIYASA TAH* Daga Alƙalamar MAMAN TEDDY_
_*AUREN SHA’AWA* Daga Alƙalamar OUM APHNAN Karku bari a baku labari,zaku samesu cikin sassauƙan farashin da babu kamarsu_
_Regular_
Zaki samu guda *Ɗaya* ₦300
*Biyu* ₦500
*Duka ukun* ₦800

_Manyan mata kuma ƙasaitattu ba’a barku a baya ba,ganaku kaɗan cikin tunjimin aljihunku_
*Ɗaya* ₦1000
*Biyu* ₦1500
*Duka ukun* ₦2000

•┈┈┈••✦✿✦••┈┈┈•

_Zaki biya ta wannan Bank account ɗin_
0255526235
_Fauziyya Tasi’u. GTbank_

Ko katin MTN
_Zaki biya ta wannan number_
08081202932

Ko VTU
_Zaki biya Ta wannan Number_
09065990265

•┈┈┈••✦✿✦••┈┈┈•

*SHAIDAR BIYANKI SAI KI TURA TA NAN*
09065990265

♡♡ “`Sai munjiku Masoyan Amana….Share💃👍Share💃💃👍And Share💃💃💃👍Habibties Allah ka barmu da masu sonmu😍😍😍“`♡♡

 

*OUM HAIRAN*
[12/30, 8:54 PM] Oum Hairan&Affan: *FINALLY*

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button