Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 26

Sponsored Links

GARKUWARTsayuwa tare da kasa kunnuwanta.
Tana jin sautin zazzaƙar muryashi.
Yana kudba.
Akan laduban fuskantar watan Ramadan wanda zuwa yanzu kwanaki ne suka rage.

A hankali ta fara taku tana
Nufo inda Hibba ta shimfiɗa musu sallaya.
Ita kuwa Hibba ido ta zuba mata ganin yadda ta kasa kunne.
Cikin murmushin tace.
“Aunty Aysha me kikeji”.
A hankali tace.
“Wannan me sunan malamin da yake huduban nan. Kamar inada wa’zuzzukanshi amman kuma, ban san sunanshi ba, kamar dai kam nasan wannan Muryar”.
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
“Lallai ma kam Aunty Aysha wai muryar Hamma Jabeer ɗin ne ma kike cewa kamar kin santa, kamafa kikace, lallai kam my Aunty”.
Da sauri ta kalli Hibba domin zuwa yanzu ta gane waye suke cewa Hamma Jabeer, Ko Sheykh, ko Jazlaan, ko Muhammad wani lokacin Umaymah na kiranshi haka.
Ta kuma fahimci wai shine mijin da aka aura mata.
Ta kuma gane sun taɓa haɗuwa sau biyu kafin yau.
ganin tayi nisa a tunnine yasa Hibba cewa.
“Aunty Aysha”.
Murmushi ta ɗan yi tare Dasa hannun ta amshi hijabin da Hibba ke miƙo mata.
Cikin ranta take mgnar zuci.
“Uhumm mutun duk rayuwarsa tana cike da ƙalubale da matsaloli Magauta sun sashi a tsakiya kota ina ya juya suna tare dashi.
Amman bauɗewa ta hanashi ganewa, sai anyi mgn yace wai anayi mishi ihu a kai.
ko shi kunnen macijine dashi da yafi kowa jin sauti.
sai iya lillibka ɗika-ɗikan al’kyabbar yanata ɓoye jiki kamar wani mace”.
Mitsss ta ɗanja gajeren tsaki tare daci gaba da zancen zuci.
“Yana nan jiki duk matsaloli ya bari mutun yaga iya inda abunda ke kan yatsunshi ma, ya gagara, shine kullum cikin al’kyabba har ƙasa uwa shine limamin harami.
Sai an kasheshi a banza yasa ƙannenshi da iyayenshi a matsala.
Danni matsalar rashin yayuna har huɗuma ya isheni damuwar duniya bazan ƙarawa kaina damuwar waniba”.
Da sauri ta juyo ta matso kan sallayar sabida jin har masallacin sun sallame sallar, sabida ta daɗe a tsaye tana zancen zuci.

Nan dai sukayi salla, kana Hibba ta miƙa ta fita
Ita kuwa Shatu, sabuwar wayarda aka saya mata jiya da sabon layi aka haɗa mata komai ne, tasa hannunta,
ta jawo.
tare da komawa ta kwanta bisa sallayar.
Layin Bappa tasa kana ta kira.
Jin bata shiga bane yasata gane, sun tafi kenan.
Cikin sanyi ta kira ɗaya layin na wancan ƙasar tasu.
Cikin sa’a kuwa ya shiga sai dai ba’a ɗagawa.

Related Articles

Sau uku ta kira jin ba’a ɗaga ba, ta haƙura.
Number Rafi’a tasaka ta kira.
Tana ɗagawa tace.
“Rafi’a Garkuwa ce”.
Cikin tsananin jin daɗi Rafi’a tace.
“Alhamdulillah Garkuwa ya kike? Ina kike? Ashe kuma abinda ya faru kenan.
Alhamdulillah mun rabu da matsalar Ba’ana, jiya naje Rugar Bani, wai yau su Bappa zasu tafi Lardi”.
Cikin murmushi tace.
“Kai Rafi’a kimin mgna da ɗaɗɗaya mana zanfi ganewa”.
Cikin dariya tace.
“Eh kyace haka mana kinyi bulunbuƙui a masarautar Joɗa”.
Cikin sanyin jiki taja numfashin tare da cewa.
“MASARAUTAR Joɗa ko matsala, komai a bai-bai yake Rafi’a, bana fahimtar komai, tunda nazo cikin wannan masifeffen masarauta kaina a juye yake. Jina nake kamar a rami”.
Cikin rauni tace.
“Rafi’a abubuwan sunmin yawa, da wanne zanji.
Tabbas nayi farin cikin tsira daga tarkon ya Ba’ana, to amman ƙaddara batayi min adalciba data kawoni wannan wurin.
Kin sani Allah ya sani ina son Ya Salmanu”.
Da Sauri Rafi’a ta katseta da cewa.
“Kice Astagafirullaha kada ki mance da auren wani a kanki kike cewa kina son wani”.
Hawayen da suka cika mata ido ta share tare da cewa.
“Bana sonshi! Bana ko son ganinshi, kuma shima hakane baya sona baya son ganina. sauƙina ɗaya da shima ba sona zaiyiba, kowa zaiyi rayuwarshi babu ruwanshi da wani shiyasa hankalina bai tashi sosaima, sai dai ina cikin tarin damuwa Rafi’a, babu Ya Giɗi,Gaini, Seyo, Lado, Inna. Sannan Junainah,Ummey da bappa da nake gani inji sanyinma wai sun tafi Lardi,
ya zanyi inji farin ciki, ga wannan gida mai mutantani daban-daban wasuma naga tsanar shi wancan mai jajayen kunnuwan zasu ɗora a kaina, ko uwar meye haɗina dashi, da magautanshi zasu haɗa dani a ƙiyayyarsa, suji dashi mana, tunda bansan meya shuka musuba, dan shima na lura ba kanwar lasa bane bakine dashi, kan ace ɗirin yake ce musu konɗi, rashin tsoronshi na bani tsoro.”
Murmushi Rafi’a tayi tare da cewa.
“Yanzu dai ya batun karatunki?”.
Cikin sauƙe numfashi tace.
“Zan gayawa Umaymah”.
Cikin shaƙuwarsu Rafi’a tace.
“To sai na shigo, dan mgnar bazata ƙare a wayaba”.
Da sauri tace yaushe zakizo?”.
Cikin sauƙe numfashi tace.
“In sha Allah dai kafin azumi zan shigo”.
Cikin sauri tace.
“Kafin azumi kuma azuminfa da ɗan saura bama kice gobe ko jibiba, Rafi’a in bakizo minba wa nake dashi da zai zomin?”.
Ta ƙarishe mgnar cikin rauni,
Cikin tausayin Rafi’a tace.
“To gobe ko jibi in sha Allah”.
Cikin jin daɗi tace.
“To sai kinzo.”
Daga nan sukayi sallama.

A ranar da yamma Haroon ya wuce jiharsu Jannart inda nanne masarautar sarkin musulmai take.

A hankali dai kwanakin sukayi ta gungurawa suna cuɗewa Ramadan nata ƙara gaba towa.
Yayinda duk al’ummar Annabi suketa shirye-shiryen tarban watan Ramadan.

Yau dudu saura kwana bakwai ne ake zaton za’a fara azumi, in bai cikaba ma kwana shida.
Tuni Umaymah nata shirin komawa Jihar Tsinako sabida Abban Haroon ya matsa ta dawo sabida shirye-shiryen Ramadan.

Ita kuwa Umaymah tana jiran kayan auren data aika a haɗo mata a Dubai su isone.
wanda ƙawarta ce ta bawa aikin kuma ƴar nan cikin jihar Ɓadamaya ne!

Yau Lahadi ne, ta kama ranar bautar al’jihun baya ne.
Wannan yasa duk manya-manyan Coci na cikin garin Ɓadamaya ya cika maƙil da mabiya bayan addinin Kirista ci.

A hankali motocinsu suka fara fitowa cikin masarautar Joɗa, suna kama babban hanyar da zata sadasu da asibitin taraiya na jihar wato Genaral Hospital Ɓadawaya.
Kamar kullum haka tawagar take, Lamiɗo zaije kai ziyarar dubiyar marasa lfy kamar yadda ya saba duk ƙarshen mako.
A ƙalla motocin sun kai goma.
Suna tafiya a jere a jere.
Har suka iso yankin da asibitin yake, inda nan babbar hanyar hada-hadan cikin garin ne, wanda babbar kasuwar jiharma take kan titin.

Wani tabkeken cocine mai zaman kashi a bakin babban titin LCCN, yana ta hannun hagu.
Kana ta hannun dama kuma wani tsabtaceccen masallacin juma’a ne mai ɗan karen girma, haka ya zama suna fuskantar juna masallacin da cocin.
Kana sai an wuce ta gabansu za’a ratsa konar shiga asibitin.

To kasan cewar duk ranar jumma’a ƴan agaji na toshe hanyoyin daga ƙarfe sha biyu da rabi zuwa kan a idar da sallan jumma’a su buɗe,
sai kafuran nan suma suka tsiri duk ranar Lahadi tun shida na safe zasu,
Toshe hanyoyin nan, sai shida na yamma.
Wanda hakan ke jawo cinkoson ababen hawa ata yankin wuri. Sai ya zama duk masu son yin salla a wannan masallacin jumma’a to ranar a sai tsare musu hanya,
sai dai masu zuwa da ƙafa.

Wannan abun ya damu musulmai, koda aka kai ƙorafi ga gwamnatin jihar sai cewa tayi.
“Ita bata son fitina, a bar kowa yayi addininshi salin alum”.
Haka musulmai suka haƙura dan a zauna lfy. To masarautar Joɗa bata da wannan lbrin sai yau da suka fito ranar lahadi da yake kullum asabar suke zuwa.

A jere a jere motocin ke tafi kasan cewar da sanyin safiya ne,
lokacin sun gama rufe hanyoyin kana sunata tsastsafowa gabas da yamma kudu da Arewa.
Cikin Mamaki motar su Lamiɗo da saura duk suka tsaya, sabida ganin motocin gaba sun tsaya.
da sauri Sallama ya fita, tare da dawowa baya.
zuwa gaban motar Lamiɗo yayinda Motar Sheykh Jabeer kuwa take can bayansu, shi sauri yake zaije Valli Hospital dan yiwa wata mata aiki.

Rusunawa Sallama yayi tare da cewa.
(“Allah rene halkaleru en mabɓi labi mai”.) Allah rene kafurai sun rufe hanyoyin”.
Da sauri sarkin ƙofa ya fito yazo ya buɗewa Lamiɗo marfin yadda zasuji juna da kyau.
Cikin mamaki Lamiɗo yace.
“Lfy meya faru zasu rufe hanyoyin”.
Da sauri dubagari yace.
“Ai haka sukeyi duk ranar Lahadi, su hana mutane sakewa su rufeshi tun safe sai yamma”.
Cike da Mamaki Galadima da yanzu ya iso wurin yace.
“To duk hakan na menene?”.
Cikin sauri Duba gari ya ɗan rusuna tare da cewa.
“Wai sabida musulmai na rufe hanyar duk ranar jumma’a sabida bada tsaro wai suma shine suka tsiri, hakan ankai mgnar wa gwamnatin kuma ta goyi bayansu”.
Cikin ta ajjudi suka kalli juna,
kana cikin bada umarni Lamiɗo yace kaje kace, su buɗe hanyar yanzu nan.
Kuje da sarkin aike”.
Nan take suka juya suka nufi can inda yaransu ƙananan ke tsaye su kakkafa Road closed and stop.
Suna zuwa jim kaɗan suka dawo.
Tare da cewa ai yaran sunƙi sabida sunce Gwamnatin jihar ta amince musu da haka.
Wannan mgnar yayi masifar tasa zuciyar Lamiɗo.
Cikin ɓacin rai ya zaro wayarshi ya danna mai girma Gwamnan kira.

Inda yace maza, ya bawa kafuran nan damar buɗe waɗannan hanyoyin da suka rufe.
Ba kunya gwamnan yace, to ai. Dokace Allah rene da kunbi wata hanyar ai yafi ko.”

Cikin tsananin tarin takaici Lamiɗo yace.
“Muje duk ku shiga mota, mu canza hanya.”

Sun shishiga kenan sai kuma sukaji.
matasa irin wanda suke gefen wurin suna cewa.
“Jahan! Jahan!! Jahan!!!”.
Da Sauri Duk suka fara leƙawa suna kallon wanda ake kira da Jahan, ɗan jarida mai zaman kanshi wanda jihar Ɓadamaya da kewaye ke alfahari dashi. Duk da ya kasance Musulmi mai sunaga ba nasu bane, kafurai kuma suna alfahari dashi a matsayin nasune.

Cikin isa da karsashi yake taku cikin wasu irin zafafan ƙananan kaya masu masifar kyau. Jahan kekyawane aji ƙarshe a kyau, fari ne ƙal hanci har baki shiyasa da yawa kance shi iyamurune, idanunshi farare ƙal-ƙal gashin kansa gwanin kyau sai dai kafurin askin dake kanshi.

Yaran suna hangoshi suka matsa.
Shi kuwa Jahan da kanshi ya buɗe hanyoyin gaba ɗaya.
Kana ya nufi motar fadawa dake gaba.
Haɗe hannunshi yayi wuri ɗaya tare da.
Musu alamar suyi haƙuri kana ya musu alamar su wuce.
Daga nan motar Waziri ya nufa, suma ya basu haƙuri. Haka yayi tayi har gaban motarsu Lamiɗo,
cikin sanyi ya rusuna gaban marfin motar, tare da jinjinawa Lamiɗo kana yace.
“Tuba muke Lamiɗo, ga hanya an buɗe”.
Wani irin sanyi da daɗi Lamiɗo yaji, gashi duk da Gwamnatin ta kasance ta musulmi siyasa ta hanashi adalci.
Gashi wanda ba nasu ba ya zantar da adalci”.
Haka ya rinƙa bawa mutanen cikin motocin haƙuri suna wuce.
a haka har yaje mota ta ƙarshe,
Yana isa yasa hannu ya buɗe marfin motar.
Wani irin kallo mai cike da ma’anoni yakeyi mishi.
sai kuma yayi wani munafukin murmushi.
Ganin hakane ya ja motarshi ya tafi.

 

Washe gari ranar Litinin. Da hantsi Hajia Kubra aminiyar Umaymah ta iso.
da yan rakiyanta.

Kai tsaye har bakin part ɗin Sheykh Jabeer sukayi parking.
Kana ta shiga cikin

Cikin farin ciki suka ruggume juna ita da Umaymah cikin dariya Umaymah tace.
“Hajia Kubra amman kin shamma ceni”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ato ai naga kin zaƙu kina son ki koma Tsinako ne nace bari dai in hamzarta indawo”.
Ta ƙarishe mgnar tana zama tare da miƙa Jalal car key ɗin ta tace.
“Yauwa Jalal Jamil ku shigo da kayayyakin.”
To sukace kana suka amshi key ɗin suka fita.

Nan suka buɗe motoci biyun wanda tazo a ciki da wanda drever’nta yazo a ciki.
Nan suka rinƙa kwatsar akwatunan suna shigarwa.
Set biyune masu fasifar kyau da tsadan gaske.

Umaymah kuwa tuni tasa Juwairiyya ta cika Hajia Kubra kayan kwalam a gabanta.

Robar Inabi ta ɗauka tana buɗewa ta kalli Umaymah cikin raha tace.
“Hajia Khadijah ina ɗiyar tamu”.
Cikin murmushin Umaymah ta ɗan juyo ta kalli ƙofar falon Shatu tare da cewa.

“Hibba! Hibba!!”.

“Na’am”.

Hibba ta amsa tana miƙewa tsaye
Kizo keda Aysha ga Mommy Kubra tazo”.
Cikin jin daɗi Hibba ta miƙe tare da cewa Shatu.
“Wayyo Aunty Aysha tashi muje”.
Cikin nitsuwa ta miƙe tsaye,
mayafin Arabian gawd ɗin dake jikinta ta gyara.
Kasan cewar shi guntu yasa bai ida rufe mata jelan gashin kanta data tubkeba.

Suna fitowa Hibba ta faɗa jikin Hajia Kubra tare da cewa.
“Oyoyo Mommy Kubra”.
Ruggume Hibba tayi tare da cewa.
“Oyoyo My Muhibbat”.
Sai ta kuma kalli Shatu dake ƙoƙarin rusunawa.
da sauri ta riƙo hannunta tare da cewa.
“Zo nan kusa dani kema ɗiyata ce, bakya ganin yadda Hibba tayiin”.
Murmushi tayi sabida fara’ar matar ya burgeta cikin sanyi yace.
“Mommy Ina wuni”.

“Lfya lau ɗiyata ya gida ya baƙun ta?”.
Cikin girmamawa tace.
“Alhamdulillah”.
Hibba ce ta zamo daga jikinta tare da cewa.
“Mommy wannan kayanfa?”.
Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa.
“Na Aunty Shatu ne”.
Da sauri ta zamo tare dasa hannunta zata buɗe akwatin dake gabanta, cikin haɗe fuska Umaymah tace.
“To uwar azarbaɓin, waya saki. Tashi kije ki kira min yar uwata kice mata ga saƙon sun iso”.
Da sauri ta miƙe tare da cewa.
“Aunty Aysha zo muje Side ɗin Hajia Mama mu kirata”.
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
“A a sai kin dawo”.
Tana faɗin haka ta miƙe ta koma falonta.
Ummi Aunty Juwairiyya da Umaymah kuwa kallon junansu sukayi.
Hajia Kubra ce tace
“Kunya ko”. Murmushi Umaymah tayi tare da badda zancen da haka.

Ita kuwa Hibba da sauri taje ta kira Hajia Mama, aiko kusan tare suka taho, da Botool.

Koda sukaje Umaymah ta aika Ummi a matsayin ta na Jakadiyarsu take ta sanarwa Gimbiya Aminatu tazo taga kayan auren da ta haɗa amryar Jazlaan ɗin ta.

Bayan duk sun zone, Suka bubbuɗe akwatunan, goma sha biyun nan duk cike suke maƙil da kayayyakin bukatar amare.
Abun sai wanda ya gani.
Lokacin da aka buɗe akwatunan turaruka gaba ɗaya Side ɗin ya cika da ƙamshi tako ina.
Manyan akwati biyu aka cika da dogayen riguna masu masifar kyau da tsada da taushi.
Sai kuma biyu da aka cikasu da atampopi da shadda da lace.

Sai kuma babba daya da aka cikashi maƙil da laffaya masu azabar kyau da tsada, babu kalan da babu a ƙalla sun kai kala ashirin da huɗu.

Sai biyu daga ciki ƙananan kayane birjik

Sai wani babban bakko, da aka cikashi da takalma a ƙalla kala goma sha biyar, bakwai daga ciki sunada hand bang, hudu daga ciki pase garesu.
hudu kuma masu siffan sayyadane masu kyau.

Sai kuma kayan tarkacen mayuka da sabulai na jiki da kai.

Kai abun dai masha ALLAH.

Da sauri Hibba ta zari takalma uku daga ciki takalmomin ta nufi bedroom ɗin ta da sassarfa tana cewa.
“Aunty Aysha bari inzo ki gwada takalman nan, Ni dai sai inga kamar zasuyi miki kaɗan.”.
Tana shiga ta ajiye mata takalman a gabanta tare da cewa.
“Gwada mu gani”.
Sosai takalman sukayi mata kyau, haka yasa ta zura ƴar kekyawar farar ƙafarta.
Ai kuwa tayi mata cib-cib cikin dariya Hibba tace.
“Ashe dai zai miki dai-dai”.
Murmushi tayi tare da gyaɗa tare da cewa.
“Uhumm ba kin raina ƙafar tawaba”.

Daga nan ta juya, ta koma falo, nan ta samu Hajia Mama na cewa.
“Wannan kaya haka Khadijah kin kashe kuɗinki a banza ƙanwata wannan yarinyar ba matar auren Muhammad bane”.
Cikin yin ƙasa da murya Umaymah tace.
“Karkice haka Hajia Mama”.
Cikin ɓacin rai tace.
“Khadijah ai dole ince haka, ke har yanzu baki gane cewa wannan yarinyar ba matar ahlin masarautar Joɗa bace, a gabanki fa, taƙi shan madarar Barka da zuwa Masarautar Joɗa.
ta kuma kwaɓar dana hannun Jabeer wanda shine na Barka da zama magidanci.
Hakafa zatayi ta kwaɓar da duk wani abun ci gaba ko nasara a rayuwarsa.”
Batool ce ta ɗan gyara zamanta cikin danne baƙin cikinta tace.
“Uhummm a tsallake ƴan uwa jinin sarauta aje a kwaso mishi bagidajiya ba fullatanar daji, ba dole tayi halin dabbobiba tunda cikinsu ta tashi. Tasan menene masarauta bare tasan ƙai dojinshi da kuma, nasabarsa.”
Ta ƙarishe mgnar tana son maida hawayenta.
Allah ya sani tana son Sheykh Amman ta lura, Hajia Mama taƙi sa baki abin yayi gashi har an auro mishi wata.
Cikin murmushin Umaymah tace.
“Batool zaki auri mai matane?”.
Cikin sauri tace.
“In wanine bazan auri mai mataba, amman in Hamma Jabeer ne, wlh ko mata uku gareshi da ƙwar-ƙwara biyar in zai aureni zan yarda in zama ta tara,
Kowa ya iya allonsa ya wonke”.
Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa.
“A lallai kam”.
Ita dai Hajia Mama miƙewa tayi ta fice rai a ɓace.

Gimbiya Aminatu kuwa, murmushi tayi tare da cewa.
“Ji ƙarfin hali ita kafin uban Jabeer ya arota Allah ne kaɗai yasan adadin dukiyar da aka narka.
Sam iyayen mazan yanzu sai a hankali.”
Cikin sauri Hajia Kubra tace.
“Matan ƴaƴan ma na yanzu ba irin na da bane.
Shiyasa aketa samun matsala tako ina kowa kansa ya sani”.

Ita dai Umaymah murmushi tayi tare da cewa Juwairiyya.
“Juwai keda Hibba kuje ku kimtsa mata komai a ɗakinta ku shirya mata drower’nta.
Kana ku kimtsa mata kan dreesing mirror.
Kai kuma Jamil ɗauki bakon takalman nan ka juye takalman.
Juwairiyya kisa Shadda bakwai lace bakwai, atampa bakwai, kampala Bakwai, swiss voile bakwai.
A cikin atamfofin kisa
Super wax biyu English wax biyu, Holand biyu sai swiss atampa ɗaya.
Sai kusa a bakon.

Jamil sai ka kaisu wurin telan Juwairiyya.
Ayi ɗinkunan da wuri.”

Haka kuwa akayi akani komai yadda tace.

Bayan sun gama kimtsa mata komai da jera komai a muhallin shi ne,

Suka fita, sannan Umaymah ta shigo, gefenta ta zauna cikin nitsuwa tace.
“Ɗiyata ga kayan sawarki naso ace sun iso tun kafin yau.
To sha’anin nesa, shiyasa kikaga bai iso da wuriba, duk kayan nakine kisa wanda kikeso a sanda kikeso.
Sabida ke akayi komai.”
Cikin tarin jin daɗi da ganin darajar ta tace.
“Ngd Umaymah Ngd matuƙa, Allah ya saka da al’khairi”.
Amin Amin tace kana ta miƙa tare da cewa.
“Naga kina son dogayen riguna ranar da zan aika kince su kikafi so, gasu an kawo miki su da yawa”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Nagode sosai Umaymah Allah ya ƙara girma”.
Amin Amin tace kana fita.

Ita kanta Shatu tasan babu ƙaranta a duk kayan da aka jinbga mata.
Komai mai kyau ne.

Yau talata da hantsi suna zaune a falon.
Hadimai sukayi sallama da Jakadiyarsu, bayan ta basu izinin shigowane.
Suka fara shigowa suna wucewa kitchen da kayayyakin abinci kamarsu shinkafa ta tuwo buhu biyu ta wara buhu biyu, sai gero ƙaton buhu, wanda a surfe yake, taliyar manya data yara katon biyar-biyar, kiret-kiret na ƙoyaye biyar, jarakunan mai dana manja bibbiyu katon ɗin maggi ɗaya dasu doya da dankalin turawa mai yawa.
Haka suka rinƙa jida suna kaiwa store.
Bayan sun gamane, Umaymah ta kalli Aysha cikin yin ƙasa da hannu ta miƙa mata dubu biyar.
Kana tace.
“Engo basu tukuici, wannan daga store ɗin masarautar Joɗa ne, duk ko wani sashi haka ake kai musu in Ramadan ya kawo kai.”
Cikin jin kunya tasa hannu ta amshi kuɗin kana ta miƙa Hibba tare da cewa.
“Hibba basu”.
Da sauri Umaymah ta girgiza mata kai, sai kuma ta kalli hadiman suna shirin fita tace.
“Kuzo matar Sheykh na kiranku”.
Ɗaya daga cikin sune, ya dawo.
a hankali ya iso ya rusuna gaban Shatu tare dayin ƙasa da kanshi.
Cikin nitsuwa yace.
“Gashi mun gode Allah ya kaimu baɗi lfy”.
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu.
Kana ya amsa ya miƙe ya fita.

Su kuwa sukaje sukaci gaba da hirarnsu.

Washe gari kuma ranar Laraba.
Wanda ana zaton kwana huɗune ya rage Ramadan, koma biyar.

Umaymah ce zaune ita da Sheykh,
ido ya zuba mata har ta gama mgnar da yakeyi na batun ran jumma’a fa zasu koma.
ta jaddada mishi kadafa ya mance yanzu yanada mata.
Kanshi ya jingina jikin kujerar tare da son kauda wannan zancen yace.
“Jadawalin jerin malam da zasuyi tabsirin Ramadan a jahohi mabanbanta ya fito”.
Cikin alfahari da hakan tace.
“Wacce jahar kuma aka turaka bana?”.
Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
“Tun da da nake ta son a barni a jihata, kullum sai a turani wata jihar, sai bana kuma da nake son in tafi wata jihar suka barni a nan”.
murmushin jin daɗin hakan tayi tare da cewa.
“Alhamdulillah kaga darajar aure ko”.
Bai tanka mataba,
itama bata jira ya tanka matanba tace.
“Ya batun tafiya umarah kuma”.
Kanshi ya ɗan ɗago ya kalleta hannunshi yasa ya shafa sajenshi cikin nitsuwa yace.
“Sha biyar ga watan zan tafi”.
Da sauri tace.
“Zaka tafi ko zaku tafi?”.
Kanshi ya ɗan dafe tare da nazarin ya zai yanke mgnar cikin nitsuwa yace.
“Eh zamu tafi”.
Yalwataccen murmushi tayi sabida bata gano manufarsa ba.
Cikin kula yace.
“Kefa yaushe zakuje”.
Tana ƙoƙarin miƙewa tace.
“Shatara ga watan Ramadan zamuje”.
Da sauri yace.
“Umaymah”. Komawa tayi ta zauna tare da cewa.
“Na’am”.
Cikin kwaɓe fuska yace.
“Muna mgna kuma zaki tafi, me zakije kiyi ne a can “.
Cikin murmushin tace.
“Zanje wurin Aysha akwai mgnar da zamuyi”.
Ba tare da ya san waye kuma wacce mai suna Shatu’n ba yace.
“Uhumm shike nan”.
Cikin kula tace.
“Ko akwai wani abu ne?”.
Kai ya girgiza mata, ganin haka yasa ta miƙa ta fita.

Shi kuwa ya miƙa ya shiga bedroom ɗin shi dan yana son yin baccin tsakanin azahar da la’asar, sabida wannan baccin yanada al’fanu.
Dan zai taimakawa mutun wurin tashi da dare.

Ita kuwa Umaymah a falo ta samu.
Shatu da Ummi. Dan Hibba tana can sashin Aunty Juwairiyya.

Gyara zamanta, tayi tare da kallon Ummi cikin nitsuwa da shaƙuwarsu tace.
“To Ummin Jabeer, Ni dai tafiya ta ƙara to in Allah ya kaimu, jibi jumma’a zamu tafi, zan barki da sauran aikin”.
Cikin sauri Ayshs ta ɗago kanta ta kalli Umaymah cike da fargaba tace.
“Umaymah tafiya?”. Ta ƙarishe mgnar cikin sanyi.
Ido Umaymah ta ɗan zuba mata cikin karantar yanayin da take ciki tace.
“Eh Aysha zamu tafi jibi da yamma jirginmu zai tashi zamu tafi Hibbab ya dawo yace yana kewar Hibba”.
Da sauri tace.
“Ayyah Umaymah dan Allah kada ki tafi da Hibba, ayyah Umaymah a bar mana Hibba”.
Ta ƙarishe zance fuska cike da rauni”.

Shiru Umaymah tayi sabida ganin hawaye suna shirin zubo mata,
sai kuma ta miƙa da sauri ta nufi ɗakinta, sabida jin bazata iya danne hawayen nataba, Allah ya sani ta saba da Hibba sosai, itake ɗebe mata kewar Junainah, Umaymah ke meye mata gurbin Ummeynta, sannan wai duk zasu tafi.
Tabbas ta saba da Ummi amman ba kamar Umaymah.
Sam tama kasa yarda da Juwairiyya kam ma.

Koda ta tafi, Umaymah da Ummi murmushi sukayi.
Cikin sanyi Umaymah ta fara mgn da Ummi bisa dukkan alamu mgnace ta sirri domin nima banjisuba.

Na dai ga daga ƙarshe duk suna zubda hawaye.

Bayan sallan isha’i ne Hibba ta nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu.
Dan amsowa Hamma Jabeer ɗinsu aiken da ya mata.

Bayan ta dawone ta ajiye Foodflaks a gaban Umaymah tare da cewa.
“Umaymah gashi, a kai mishi”.

“Jeki gayawa matarshi tazo ta kai mishi.”
To tace tare da juyawa ta nufi falon Shatu.

Ganin bata falone yasa ta wuce bedroom.
A kwance ta sameta bakin gado.
Ta konta rubda ciki, tanayin kuka mai sanyin sauti.
da sauri ta zauna gefenta tare da cewa.
“Aunty Shatu meya faru?”.
da sauri tasa tafin hannunta ta shere hawayen, kana ta miƙe zaune hannun Hibba ta kama ta riƙe tare da zuba mata ido cikin sanyin murya tace.
“Please Hibba mu zauna kada ki koma, ki cewa Umaymah zamuyi azumi a nan.”
Shiru Hibba ta ɗanyi kana ta ɗan yi murmushi tare da cewa.
“To zan gaya mata, kuma kema ki gayawa Hamma Jabeer in shine yace mata ta barni bazata hanani ba.”
Cikin sanyi tayi shiru, alamun nazari, ta ina? kuma ta yaya? yaushe zata mishi mgna? Mutumin da ko kallon inda take bayayi! Anya kuwa yama sanni ne?!.
Tayi mgnar zuci.
Ita kuwa Hibba cikin murmushi tace.
“Allah muwa in kin gaya mishi za’a barni”.
kai ta jinjina tare da komawa zata jingina da kan gado, da sauri Hibba ta kamo hannunta tare da cewa.
“A’ a taso Umaymah tace kizo”.
To tace tare da miƙewa, a tare suka fito falon.
Cikin kulawa Umaymah ta nuna mata Foodflaks ɗin.
“Ɗauki ki kai mishi falonshi”.
da sauri ta zaro ido cike da mamaki, gane hakane yasa Umaymah kauda kanta,
ita kuwa Shatu shiru tayi tare da zubawa kulolin idanu.
Muryar Ummi ce ta kuma ratsa kunnuwanta.
“Ɗauki ki kai mishi in dare ya ɗan yi nisa bazai cibafa”.
Bazata iya musu musu da gardama ba.
haka yasa cikin sanyin jiki ta sunkuyo ta ɗauki Foodflaks ɗin, kana ta juya a hankali ta nufi corridor da zai kaita Side ɗinsa,
tafiya takeyi cikin nitsuwa kanta a sunkuye.

A bakin ƙofar falon ta ɗan tsaya cikin sanyi murya can ƙasa tayi sallama , yadda ita kanta batayi dan wani ko zaton wani yajiba.

Yana can Dinning area, yana zaune bisa ɗaya daga cikin chairs ɗin Dinning table ɗin.
Yasa System nashi a gaba.
hankalinshi duk yana kai, ga woyoyi a ƙalla uhu suna gefenshi.
sai cup mai cike da madarar shanu mai ɗumi.

Murya can ƙasa bisa saman tattausan jajayen laɓɓansa ya amsa sallamar da ya jita raɗau cikin kunneshi sai dai bai fahimci mai muryar kai tsayeba,
asalima ji yayi kamar muryar Umaymah ce.

A hankali ta turo kanta ta yaye labulen kana ta sako ƙafanta cikin, falon da bata son koda kallon ta inda yake, ba don bai mata kyauba sai dan wasu manyan dalililai da abubuwan da take gani tako ina a falon,

A hankali take taku, i zuwa inda ta hangoshi zaune ya bawa ƙofar shigowa baya.
cikin nitsuwa ta take step ɗin forko,
tare da ɗago kai ta kalli ƙeyanshi.
baki ta murguɗa tare da taɓe bakin kana ta manna mishi harara bisa tattausan suman ƙeyan nashi.
A haka ta ƙara motsowa, shi kuwa Sheykh Jabeer tabbas yasan da mutun a bayanshi.
Ya kuma gano wancan abun ne, shiyasa ko ta kanta baiba.

Aikin da yasha mishi kai yakeyi ba kama hannun yaro.
Da sauri ta ajiye Foodflaks ɗin bisa glass ɗin Dinning table ɗin, wanda hakan ya bada wani sautin.
Idonshi ya ɗan rumtse tare da buɗesu, kana yaci gaba da aikinshi ko gefen da take bai kalla ba.
Ita kuwa sai ruwan harara taketa manna mishi tako ina.
kana kuma dai tana tsaye bata juya ba.
a ƙalla 55 second bata tafiba, bata kuma ce mishi komaiba, sai hararan da takeyi mishi har ta fara jin idonta na ciwo,
sabida harara ba ɗani’arta ta yau da kullum bane, sai in tana masifar jin haushin mutun da tsanarsa take mishi wannan abun.

Bai kulataba, ganin ba kulata zaibane yasa ta ɗan ja wani gajeren tsaki can cikin maƙoshinta, a zatonta baijiba.
shi kuwa Sheykh Jabeer kanshi ya ƙara rusunarwa sabida sam ya lura wannan abun ba kunya ne dashiba.
Cikin murhuɗa baki da harara tace.
“Dan Allah ka cewa Umaymah ta bar min Hibba muyi azumi a nan”.
Ta ƙarishe mgnar da ɗan ƙarfi.
Shiru yayi tamkar bai jitaba ko baisan da ita a wurinba,
Sabgogin gabanshi yakeyi tamkar babu wani halittan dake wurin.
cikin kufula ta kuma cewa.
“Dan Allah kace a barta muyi azumi anan”.
Ko gezau baiba. Sai dogayen fararen yatsunshi da yake sarrafawa bisa ma dannin System ɗinsa tamkar shiya ƙirƙirota.
Shi sauƙinshi ɗaya tunda yanzu zuciyarsa ta dena bugawa da tsinkewa in mayyar tana kusa.
A karo na uku ta kuma yin mgna tare da juyawa ta fita.

Bai kulataba bashi kuma da niyar kulata.
Ita kuwa Shatu cikin takaicin sheretan da yayi ta fito.
Ita in ma badon batun Hibba ba mai zai sa tayi wa wannan mutumin mai ɗan karen mannin hauka da ƙasaita mgn.

A falo ta samu su Umaymah dasu Jalal, gefen su ta ratsa ta wuce, da sauri Hibba tabi bayanta.

Tana shiga tace.
“Aunty Aysha me yace?”.
Cikin nuna damuwarta tace.
“Uhum yace Umaymah ce taƙi, sai dai in ita zamuyiwa mgn”.
Ta ƙarishe mgnar da nazarin ta yayama zata cewa Hibba tayi mgna bai ko kalli inda takeba bare ya kullata.
Hibba kuwa da sauri ta juya tare da cewa.
“To bari inje in lallashi Umaymah.”

To tace wanda. Tunima Hibba kam ta fita.

A gaban Umaymah ta zauna cikin sanyi tace.
“Ayyah Umaymah dan Allah a barni inyi azumi anan, kinga Aunty Aysha ta roƙi Hamma Jabeer yace ki barni yace kin yarda ne, gata can tana fushi”.
Cike da mamaki da jin daɗin yadda akayi sukayi mgna dashi, har ya gaya mata yadda sukayi dashi jiya kan ta bar Hibba tace a a.
Jamil ne ya ɗan kalli Umaymah tare da cewa.
“Dan Allah Umaymah ki barta, in anyi salla Ni da kaina zan dawo miki da ita tunda jakar ratayawarki ce ita”.
Cikin dariya Ummi tace.
“Eh dan Allah ki barta in dai mahaifinta zai yarda, kinga tana ɗebewa ɗiyar taki kewa”.
Murmushi Umaymah tayi kana, ta kalli Jalal da bai sa musu bakiba.
Aunty Juwairiyya ma magiya take a bar Hibba, hakane yasa Umaymah tace to ba matsala zata bar musu ita aron wata ɗaya ran salla dai zata koma, cikin jin daɗi sukace sun yarda.

Ai da gudu fa Hibba taje ta gayawa Shatu.
Sosai taji daɗi har ta ɗan saki jiki.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko inda Foodflaks ɗin suke bai kallaba, sabida ba tsarinshi bane cin abu mai nauyi in dare yayi, haka yasa iya madarar yasha,
kana yaci gaba da aikinshi.

Washe gari ranar Alhamis, wuni Umaymah tayi tana shirye-shiryen komawa.

Ta sallami duk mutanen da take mutunci dasu a fadan.
Dama cikin masarautar Joɗa cewa Gobe jumma’a da mangriba zata koma.

Washe gari ranar jumma’a, da misalin karfe sha biyu.

Duk suna zaune a falon harda Jafar, Jalal, Jamil, Imrane, Ya Hashim, duk suna cikin shigar jumma’a.
Dakon fitowar Sheykh suke jira.

Umaymah da Ummi da Aunty Juwairiyya kuwa, suma suna nan, cikinsu ana ɗan hira.

Hibba kuwa da Shatu suna kitchen dan Hibba tace in Shatu ta iya awaran couscous ta koya mata.

Suna nan zaune, Hajia Mama da hadimanta
Suka shigo.

Cikin jin daɗi Umaymah tace.
“Yanzu nake tunanin zanzo Side ɗinki Adda na”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Oh ai bazaki zoba, yadda kike tsakiyar yaranki yar uwa kam an manceta”.
Murmushi sukayi baki ɗayansu,
Batool da yanzu ta shigo da wasu hadiman suna rirriƙe da manyan bokitayen kande tsiraran masu cike da markaɗeɗɗen gyaɗa na kunu da miya sai ƙananan su kuma turaren wutane a ciki da biyu ɗaya dakekken yajin daddawa ɗaya dakekken yajin borkono komai bibbiyu. Sai galullukan man shanu. Da na zuma sai na Humra, kana sai manyan bako guda biyu.
cikin murmushin Umaymah tace.
“Iye Addana me na samu hakane?”.
Cikin sakin fuska tace.
“Abubuwan daɗi nasan kina son kayayyakin gargajiya”.
murmushi tayi tare da cewa.
“Duka wannan ai yamin yawa”.
Kallon kayayyakin tayi tare da cewa.
“Keda su Ummi ne, suma za suyi amfani dashi a Ramadan, Musamman ma da ɗan naki anan zaiyi azumi bana”.
Cikin jin daɗi Umaymah ta kwallawa Hibba kira tare da cewa.
“Kizo keda Aunty naki”.
To sukace kana suka kashe Gas ɗin da yake dama sun gama aikin.

Suna isowa Hibba taje ta zauna kusa da Hajia Mama da sauri tare da cewa.
“Hajia Mama an barni a nan zamuyi azumi”.
Cikin murmushi ta shafa kanta tare da cewa.
“Kai naji daɗi na.”
Sai ta kuma kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa.
“An kai miki naki kayan Side ɗinki”.
Godiya tayi.

Ita kuwa Umaymah hannun tasa ta jawo bako ɗaya ta zuge zib ɗin shi ta fara fiddo ledodin dake ciki wanda dakekken busasshen kayan miya ne kamarsu.
Kuka, kuɓe, daddawa, citta, kanumfari, ganyen na’ana, zogale, da dai ire-iresu ne a ɗaɗɗaure a manyan ledodin masu layin baki da fari.
Cikin jin daɗi kayayyakin Umaymah tace.
“Kai nako gode naji daɗin kayan miyar nan, dan mu wurinmu suna wuyar samuwa.”
Sai kuma ta juyo ta kalli Shatu dake zaune gefenta,
Tayi wani irin kici-kici da fuska babu alamun wal-wala.
Cikin nuna jin daɗi tace.
“Ɗiyata ga kyautan Hajia Mama, komai bibbiyu ne ɗaya naki ɗaya nawa ne, kiyi godiya”.
Cikin wani irin kallo mai cike da ma’anoni da sarƙafe-sarƙafe ta gyara zamanta, tare da komawa ta jingina da kujera, ƙafarta ɗaya ta ɗaura bisa ɗaya tare da fara karkaɗa ƙafar cikin fuska a haɗe kana a daƙile ta nuna kayan tare da cewa.
“Bama so, Umaymah Bama buƙata”.
Cikin tarin mamaki da al’ajabi duk suka juyo gareta suka zuba mata ido.
Ummi da Umaymah kuwa har suna haɗa baki wurin cewa.
“Sabida me? Akanme zakice bakya so?”.
Ba tare da ta kallesu ba tace.
“Ba cewa nai bana soba, cewa nayi bamaso, itama Umaymah bata so.”
Cikin tsananin mamaki suka bushe suna kallonta,
Jalal ne ya zuba mata ido cikin haɗe fuska.
Hajia Mama kuwa wani irin kallo mai cike da tsoro da mamaki da al’hini da jin tsanar Shatu cikin ranta, ta rasa me wannan yarinyar take nufi da ita,
ta kasa gano me take gadara dashi.
Cikin tarin takaici da zafin rai tace.
“To kuma baki isa da gidan ba,
Bare ki zana layi a biki, ke in banda rashin sanin darajar manya har zaki gaya min haka, ko gidanku ba manya ne?.”
Cikin isa da ɗaga murya tace.
“Yesss! Gidanmu babu manya irinka, Bama so bazamu amsaba ki tattara tarukucenki kije ki bawa wasu can ba dai muba”.
Cikin tashin hankali Umaymah ta daka mata tsawa tare da cewa.
“Ke Aysha ki nitsu kisan da waye kike mgna”.
Cikin ɗaga murya tace.
“Na sani Umaymah na sani nasan da wacece nake mgna kece bakisan wacece itaba”.

Cikin mamaki da sauri Sheykh ya ƙarisa fitowa cikin tamfatsen falon shi.
sabida ya gama shirin jummarsa,
jiyo hayani da hargowane yasa ya nufo falon da sauri.
To jiyo muryar Umaymah ne yasashi buɗe ƙofar falon da hamzari ya fito.

Da sassarfa ya nufo falon.
Dai-dai lokacin daya isone,
Aysha ta miƙe tsaye cikin faɗa da tsawa ta nunawa Hajia Mama da hadimanta da Batool hanya tare da cewa.
“Maza ku tattara waɗannan banzayen tarkacen naku ku tafi dashi, ku ɓace min da gani. Ku fita daga nan! Ku fitarmin gidana”.
Ta ƙarishe mgnar da ƙarfi.
Wani irin miƙewa tsaye Umaymah tayi tare da yin sauri tasa hannunta ta….!

 

 

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button