Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 24

Sponsored Links

By
*GARKUWAR FULANI*Wata iriyar zuface ke tsastsafo mishi bisa goshinsa,
Kamar an watsa mishi ruwa.
Ya kamo lip ɗin shi na ƙasa yana taunewa.
Hannunshi dake cikin blanket ta zubawa ido.
Dan son gano abinda yakeyi,
shiru tayi sawon 5 minute kana, a hankali ta ɗaura tafin hannunta kan goshinta,
tare goge mishi zufar, daketa tsastsafowa duk da sanyin A/C dake ratsa ɗakin.
Idonshi ya saisaita lumshe su da yayi, ya sani Umaymah ce.
sabida babu mai shigar masa ɗaki kai tsaye sai ita.
Babu kuma mai taɓa mishi goshi haka sai ita.
Cikin kula tace. “Jazlaan!”.
A hankali ya gama buɗe idanunshi da sukayi jazir alamun tarin ƙuna da yakeji a ransa.
A hankali tace.
“Jazlaan!.” Ta kuma kiranshi a karo na biyu.
A hankali ya motsa lips ɗin shi alamun zai amsa mata.
Amman Ina zafin da zuciyarshi keyi ya danne harshensa hafimtar hakane yasata, nuna damuwarta a hankali tace.
“Kaci abinci?”. Ƙarya ba ɗabi’arsa bace ba kuma halittarsa bace, duk ɗacin gsky zai faɗeta, bare a kan kashi.
Kanshi ya girgiza alamun baiciba.
Cikin sanyi tace.
“To Muje kaci koda abu mara nauyi ne!.”
Da ƙarfin ya fizgo mgnar.
“Bazan ci ba”.
Ta sani yadda yayi mgnar, ta kubce masane, dan in ransa a ɓace yake baya mgna, ɓacin ran mai limini kenan babu faɗe-faɗe bare hargowa ko buge-buge.
Sanin ko ya zatayi bazai cin bane, kamar yadda ya faɗa mata yasa,
ta miƙe a hankali kanshi ta shafa tare da cewa.
“Saida safe”.
Kai kawai ya iya gyaɗa mata,
Haka ta fara tafiya, tana kallon yadda yake motsa hannunshi cikin blanket tabbacin. Wani abun yake yagewa.

Yadda ta bar Haroon haka ta sameshi saida safe tayi mishi kana ta wuce ta tafi.

A can Rugar Bani kuwa. Kamar yadda Ba’ana ya ɗaukarwa kanshi al’ƙawari haka ya bar ƙasar ya nufi ƙasar Cameroon Kai tsaye Yahunde ya nufa, cikin rugagen Fulani, yana tafiyarne da ɗan sauran tsafi da sihirin dake jikinsa.

Related Articles

A haka ya nausa cikin ƙasar Cameroon da yake jihar Ɓadamaya tana bakin bodar ƙasar ne.

Fulanin Rugar Bani kuwa, a daren wannan ranar sukayi gangamin ramuwa, suka faɗawa ƙauyukan kafuran ƙabilun ɓacamawa dake cikin Shikan da kewayenta.
Allah ya basu nasarar yaƙan kafuran nan.
Har suka samu damar ƙona ƙauyem Bonon wanda shine zuciyar ƙabilar ɓachama, kamar yadda Abuja take zuciyar Nigeria.
Cikin daren suka ƙona ƙauye dama dodon tsafinsu Bonon da suka ɗauka a matsayin Ubangiji su sun ƙonashi sun ɓadda shi a doron duniya sai dai tarihinsa.

Wannan labarin shine labarin.
Da gidajen rediyo dana tv da jaridu sukayi.
Breakfast dashi yayinda akayita kuzuzuta cewar Fulani sun zama ƴan ta’adda sun farma garuwa da yaƙi.
Uhummm wannan shine halin da Fulani ke rayuwa a ciki. A zalimcesu, kaji cib duniya babu mai yin mgn su kai ƙorafinsu a koresu. Gwamnatin kasar data jiha suyi kamar basujiba. In fulanin sun rama na lokaci ɗaya sai asa musu sunan ƴan ta’adda ko yan tada zaune tsaye, har ana ikirarin korarmu.😭😭😭

Hankalin ƙabilun Ɓacamawa dake cikin Shikan duk suka ari ta kare.
Hausawa da Fulani kuwa kowa ya koma, cikin gidansa.
Domin Allah ne yabi kadunsu.

Sarkin Shikan da kanshi yayi masifar girgiza da yawan da Fulani sukayi cikin garinshi da kewaye.
Gashi an ƙone dodon tsafinsu nasu kuma babu abinda ya samu fulanin.
Hakane yasa shi kanshi ya arce, sai abu ya lafa ya dawo.

Su kuwa Fulani bayan sun gama.
Suka tsaya suka bawa yaransu da tsoffinsu mafaka, domin su basu kashe yara da tsoffi da mataba.
Anyi an gama, kafin hukuma tazo, ta ƙara sai saita Komai.

A cikin masarautar Joɗa kuwa. Washe gari da safe.
Lbrin ya rinski Sarki Nuruddeen, shine ya bada umarnin kada a kama bafulatani ko ɗaya.

Aysha ce zaune gaban Umaymah Aunty Juwairiyya na gefenta ita da Hibba, cikin kula Umaymah tace.
“Yauwa Aysha kinga wannan ki ɗauke ta matsayin yayarki ita ɗin yar babban Yayanmu ne wanda na nuna miki jiya.
Mijinta kuma ya’yan Jabeer ne, Side ɗinta na kusa da naku.
In kinga duk wani abun da baki fahimta ba ki tambayeta, in kin gaji da zaman kaɗaici zaki iya shiga wurinta, da wurin Mamanku, da kuma nan wurin Gimbiya Aminatu”.
A hankali ta ɗan kalli Aunty Juwairiyya, tare da cewa.
“Ina kwana Aunty”. Cikin jin daɗi Aunty Juwairiyya tace.
“Lfy lau ya baƙunta”. A hankali tace.
“Alhamdulillah!”.Hibba ce ta ɗan tsuke baki cikin sanyi tace.
“Shike nan ai, an gabatar mata da kowa sai ni aka ware”.
Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa.
“To Aysha ga Hibba wutar Umaymah, duk family itace auta a jikokin Sitti na nan ƙasar”.
Murmushi ta ɗan yi sabida ganin yadda Hibba tayi sai Junainah ta faɗo mata a rai.
Ita kuwa Hibba motsata tayi tare da cewa.
“My happiness”.
Cikin murmushi Aysha ta nuna kanta, alamun “Nice my happiness?”.
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
“Yes haka Umaymah tace wai kece farin cikin ahlimu da izinin ubangiji”.
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta.
Haka nan taji tana jin sonsu a ranta, Especially Umaymah da Hibba.
Aunty Juwairiyya kuwa da Ummi breakfast Suka gabatar mata, kana suka fita.
Umaymah da kantane ta haɗa mata tea mai kauri ita da Hibba kana ta zuba musu abincin da Aunty Juwairiyya ta kawo musu tare da cewa.
“Bismillah kuci abinci”.
tana faɗin haka ta miƙa ta fita,
Ita kuwa Hibba da tsauri ta gyara zamanta tare da ɗaukan Fork ta matso gaban plate ɗin da aka zuba mata soyyyan dankali da kwai, hannun tasa ta soki guda biyu tare da ɗagowa zata kai bakinta, sai kuma ta tsaya tare da zubawa Aysha ido ganin ta riƙe mata hannunta.
Cikin sanyi da ɗan sakin jiki da Hibba ta girgiza mata kai tare da cewa.
“Kada kici wannan abincin”.
Cikin juya ido Hibba tace.
“Meyasa!?”.
Kai ta jujjuya mata kana ta gyara zamanta, tare da ɗan kallon ƙofar shigowa ta gefen idonta.
Wani kekyawan Foodflaks da aka kawo daga sashin Gimbiya Saudatu ta jawo tare da cewa.
“Ki ɗiba a nan kici”. Cikin mamaki.
Hibba tace.
“Aunty Aysha, ai Bama cin abincin gidan Gimbiya Saudatu, kuma naga Hadimanta ne suka kawoshi”.
Cikin rashin gane manufar zancen Hibba tace.
“Meyasa bakwa ci?”.
Juyawa Hibba tayi ta kalli bayanta kana ta juyo ta kalleta da kyau kana a hankali tace.
“Bata son Hamma Jabeer dama duk ƴan uwanshi, cewa take zata kasheshi in ta samu dama, shiyasa Umaymah take hanamu cin abinci ta”.
Wani irin nannauyan ajiyan zuciya ta sauƙe tare da kallon Hibba cikin cushewar tunani ta kalli jerin kulolin da a ƙalla sun kusa takwas a gabansu.
Cikin sanyi tace.
“Buɗe su mu gani”.
Jin hakane yasa Hibba buɗe su ɗaya bayan ɗaya.
ita kuwa ido take zubawa duk kular da Hibba ta buɗe.
Kular ƙarshe wacce ke ɗauke da Chicken Ball’s mai zafi sai turiri yakeyi da ƙamshi.
ta nunawa Hibba tare da cewa.
“Kici wannan”.
Murmushi Hibba tayi kana tace.
“Yauwa shinema na Gimbiya Aminatu kuma ta iya girki tsohuwar hakana hadimanta, a plate ta zu musu. Kana suka faraci suna ɗan korawa da ruwan tea mai zafi da kauri.
Sunaci Hibba nata janta da hira duk da ita Aysha zuciyarta a cushe yake.

Bayan sun gamane, Hadiman Gimbiya Aminatu suka shigo suka tattare komai suka gyara wurin bisa umarni Jakadiya.

Ganin Aysha ta ɗan saki jiki da Hibba ne yasa, Umaymah ta wuce Side ɗinsa ita da Umminshi.

A falo suka samu Jafar, Jalal, Jamil, Haroon. Suna bisa kujerun Dinning area, Aunty Juwairiyya tana zuzzuba musu abincin.

Murmushi Umaymah tayi cikin jin daɗin ganin su, da wal-wala hatta Jalal fuskarshi a sake take.
Jamil ne ya kalleta lokacin data ƙara so kusa dasu, cikin murmushi yace.
“Umaymah mu sai yaushe za’a nuna mana Amaryar a gabatar mata damu, ta sanmu da kyau”.
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
“Ai ku tun daren jiya nagabatar da sunayenku da matsayinku gareta”.
Haroon ne ya ɗan kurɓi tea tare da cewa.
“Yo ai Ni dai ba sai an gabatar daniba, domin nasanta tun safiyar jiya kafinma a ɗaura auren ko Jalal?”.
Taɓe baki Jalal yayi tare da cewa.
“To ni mamaki nakeyi, ko dai dama ita tazone dan taga wanda za’a aura mata”.
Umaymah ce ta ɗan zauna kusa da Jafar tare da kallonsu kana tace.
“Babu sam ita kanta bata saniba bata zata ba bata tsammaci aurenta a jiyaba.
Sai dai arashi kukayi, Ni tun jiya da kuka gayamin nasan arashi ne kawai ya haɗaku a asibitin. Bata san komaiba akan auren nan hakama iyayenta, basu da zaɓine kawai dan sun san ƙa’idar gasar Shaɗi ne hakan yasa sukayi haƙuri.”
Kai Jalal ya jinjina tare da cewa.
“Uhummm mu dai yanzu yan kallone. Dan na sani tabbas yanzu za’a fara buga Game ɗin yanzu wasan zai soma”.
Cikin yin ƙasa da murya Jamil yace.
“Sosai ma, dan kuwa akwai kitimurmurar da za’ayi a masarautar Joɗa, wannan Ustaz Sheykh Malam akarmakallahu Hamma Jabeer ɗin, salonshi na dabanne a dukkan lamuran yauda kullum wannan auren dai zamuga ya zai kasance!”. Ya ƙarishe mgnar da yin ƙasa da murya sosai, yanayi kuma yana kallon hanyar falon Sheykh Jabeer.
Cikin haɗe fuska na wasa Umaymah tace.
“Al’khairi shine zai wanzu”.
Murmushi Haroon yayi tare da cewa.
“Inafa al’khairi a wannan abun da bashi da tushe, ni kaina naji baƙin cikin wannan al’amari, auren Muhammad Jabeer ya zama kamar a munafuce a ɓoye babu wani shiri bare kimtsi kun bari an auro mishi mace kamar auren ƴar tsana”.
Jafar kam abincinsa yakeci, ba tare da ya kulasuba.
Jamil kuwa sai murmushi yakeyi.
Jalal kuwa shiru yayi alamun nazari.

Ummi kuwa ware wasu kyawawan Foodflaks takeyi gefe.
Tare da abinci a cikinsu.

Bayan ta gamane ta ajiyesu gefe.
Tare da cewa Umaymah.
“Ga breakfast ɗin Sheykh”.
Kai Umaymah ta gyaɗa mata.

Nan sukaci gaba da hira.

A can Side ɗin Mama kuwa,
Tunda batun auren Jabeer ya basu ya riski kunnuwan ahlin masarautar Joɗa,
kowa da abinda ke ransa.

Batool kuwa hankalin Mama in yayi dubu ya tashi, bisa irin kukan da Batool ketayi har cewa takeyi ta gane ai dama Mama bata son ya aureta.
Da kyar ta samu tasha kanta,

Gimbiya Saudatu kuwa, da Baba Nasiru da Baba Basiru da Laminu.
Zaman gaggawa suka tanada.

Suna tattauwana wannan baƙin lbrin da bai musu daɗi ba.

Zaune yake gaban wani ƙasurƙumin boka matsafi.
Cikin tsantsar tashin hankali da kiɗima yace.
“Boka Tsitaka haka mukayi da kai? Yaushe ka fara min ƙarya kan aiyukan da nake baka? Ya za’ayi kwatsam rana tsaka ace wannan shegen yaron da nakeji tamkar in kasheshi yayi aure? Da kai mukayi mgna a nan tsawon shekaru kace min ka, kashe min wutsiyar ɗan iska mai jajayen kunnuwa, babushi ba mace har yaumal ta ƙunun nadi.
Ka bani tabbacin. Har gobe sihirin na bibiyarshi, kace min duk sanda zanen kan macijin ya isa kan tsaitin ƙahon zuciyarshi zai mutu kowama ya huta. Sai kuma jiya kamar sauƙan aradu ace yayi aure!”.
Wata iriyar razanenniyar dariya mara daɗin amo boka Tsitaka ya kece da ita, wanda har saida tsaunuka da kwazazzaban dake wurin suka amsa amonta.
Dariyar mugunta yakeyi babu ƙaƙƙautawa, har saida baƙon nashi ya fara hatsala cikin tashin hankali yace.
“Wannan ai insakanci ne, in bazaka iyaba ina nemo wasu matsafan. Ya zan zo da matsalata da sanyin safiyar nan kai kuma ka kama min dariya, Ni mahaukacin gidanku ne?”.
Cikin dariyar boka Tsitaka yace.
“To ai tashin hankali na banzane, kana kokonto kan aikin da shekaru goma sha biyu yana cinsa yana bin jikinshi. Kana zaton ya karye ne? To bari kaji wannan sihiri yana nan a jikinshi, har kwanan gobe wutsiyarsa bata harbawa, baya jin kanshi a namiji.
Ba kuma zaiji yadda maza kejiba har abadan.
Iya bincikena banga mai mgnin da zai gani aikin da mukayi mushiba.
Auren da akayi mishi, da ya sani tabbas da zai watsa abun. In kuwa kana zaton sihirin yana sauƙa kaje ka dubu, zanen bindin maciciyar da yake tun daga kan ƴar babbar ƴatsar ƙafarshi ta dama, zaka samu kan macijiyar ya ƙetare ƙugunshi.
Na kuma gaya maka duk sanda kan macijiyar ya isa kan ƙirjinshi, saman nononshi, zai mutu, kuma yadda zai bar duniya haka ƙannenshi da wanshi zasubar masarautar Joɗa har abada yadda ba’a tambayi yaushe matacce zai dawo duniyaba haka suma baza’a tambaya ba.”
Cikin ɗan jin daɗi baƙon bokan yace.
“To ai dole hankalina ya tashi, kaida kace min bazai wuce shekaru biyar ba zai rasu gashi yanzu shekaru goma sha biyu bai mutuba”.
Cikin zare ido boka Tsitaka yace.
“Kai ai mun ma yi dacen yin asirin da wurine, tun kafin ya gama girma da yanzune sam bazai kamashiba, mutumin da baya rabuwa da sunan Allah a bakinshi. Yaronda ko yaushe da al’wala yake zama, ai badan hakaba da tuni mun hallakashi”.
Cikin ɗan samun nitsuwa baƙon ya direwa Boka Tsitaka kuɗi kana ya miƙa ya fice.

A can wurinsu Umaymah kuwa.
Suna cikin hira, Umaymah ta ɗan juyo a hankali ta kalli hanyar fitowa falon Sheykh Jabeer, sabida jin ƙamshin turaren shi.
Murmushi mai cike da jin daɗi tayi ganinsa cikin shiga ta al’farma, kamar yadda ya saba.
Wata jallabiya blue color ce mai taushi a jikinshi.
Sai al’kyabbar da ya ɗauka samanta shi kuma peach brawn mai ɗan karen kyau sai sheƙi yakeyi,
kana sai hira minshi shima Peach brown da ɗigo-ɗigon white.
Sai takalmansa sau ciki masu kyau, baƙaƙe kana sai ɗan abun saman hiramin shima baƙi.
Taku yakeyi cikin nitsuwa da haiba da kamala, fuskarshi cike da kwarjini da ƙasaita.
Hannunshi na riƙe da Tab ɗinshi.
Idonshi na kanta yana sarrafata da hannun damanshi yayinda hagunshi ke riƙe da ita.
Sai wani irin ƙamshi yake bazawa a duk inda ya wulga.
A hankali yake taku amman da alamun sauri yakeyi.
A tsakiyar falon ya tsaya, tare da kallon inda suke zaune.
Ganin Umaymah ta nufoshi ne yasashi gyara tsayuwarshi.
Tare da ɗan kallon ta, kana yana mai amsa gaisuwar su. Jalal da Jamil.
Tana isowa inda yake ya ɗan kalleta, cikin yanayin rauninshi dake baiyana in yana gabata, a hankali yace.
“Umaymah ina kwana”.
Cikin kula tace.
“Lfy lau Alhamdulillah Jazlaan ya gajiya da jikin!”.
A taƙaice yace.
“Alhamdulillah”. Sai kuma ya ɗan juya yayi taku uku zuwa biyar ya isa Dinning area, kana Umaymah na biye dashi.
Dafa kujerar da ya Jafar yake a kanshi yayi tare da sunkuyowa ya kalli fuskarshi da kyau, sai kuma ya ɗan kalli Aunty Juwairiyya cikin kauda kanshi a kanta yace.
“Ya jikin nashi?”. Cikin sanyi tace.
“Alhamdulillah jiki kam da sauƙi sosai, dan tunda ka dawo zaiyi baccinsa lfy ba tashin hankali in lokacin tashinsa yayi kuwa ba hargowa zai tashi yayi al’wala yayi ta nafilfilinshi”.
Cikin yanayin jin daɗin zance yace.
“Alhamdulillah. In sha Allah komai zai dai-dai-ta domin babu cutar da bata da waraka sai dai ina ba’a gano mgninshi ba”.
Hannunshi ya gyara da kyau yadda Jafar zaiji daɗin riƙon da yayi mishi.

Umaymah kuwa cikin daƙile fuska tace.
“Zauna kaci abinci”.
Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta, cikin tonƙoshe kai bisa kafaɗunshi ya ɗan taɓe baki kana a hankali yace.
“Sai na dawo”.
Shiru tayi sabida ta lura sauri yakeyi.
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Jakadiya cikin sanyi yace.
“Ummi lfy kuwa na ganki haka ba walwala”.
Nisawa tayi tare da cewa.
“Ina fa zanyi wal-wala bayan Sheykh na cikin yanayin fushi, da rashin jin daɗi alamun na gaza riƙe amanar da uwar ɗakina ta danƙamin kenan”.
Wani ɗan guntun tsaki yaja tare da kallonta da kyau cikin sanyi yace.
“Ba komai Ummi kin riƙe duk amanar da aka baki, ba matsalar komai fa”.
Cikin ɗan sakin fuska tace.
“To Alhamdulillah, yanzu ina zuwa?”.
Bayan Jalal ya ɗan matso tare da cewa.
“Vallai zan je inada zama na musamman da sauran likitocin, domin jaddada musu kula da marasa lfyan da aka kai jiya”.
Kusan a tare sukace to Allah ya taimaka”.
Amin yace a taƙaice kana ya tsare Jalal da ido cikin tuhuma yace.
“Jamil jiya ina ka kwana?.”
Cikin mamakin ya akayi Hammanshi ya gane bai kwana a gidaba ya ɗan sunkuyar da kanshi cikin sanyi yace.
“Club naje to bamu taso da wuriba ne, sai na biya gidansu a bokina Hayatuddeen na kwana a can”.
A hankali yasa hannunshin ya kamo kunnenshi tare da matseshi da yatsu sa biyu.
Da ƙarfi Jamil ya saki ƙara tare da cewa.
“Wayyo Hamma Jabeer bazan sakeba, na tuba”.
Bai sakeba sai ma kauda kanshi da yayi yana kallon Umaymah cikin rauni yace.
“Kinji ba, shi kullum yana Club music sai kace ɗan ma kaɗa ko maroƙa, yaje ya kwana cikin yan iska azo ayi ta musu video ana yaɗawa duniya, ana liƙa sunana a ƙarshen sunayensu a social media kamar nine uban daya haifesu.
Haka kenan zanyi ta fuskar ƙalubale ina rasa yadda zan karesu ko in zagesu.”
Ya ƙarishe mgnar rai a ɓace.
Ita kuwa Umaymah faɗa ta fara yiwa Jamil.
Shi kuwa gaban Jalal ya tsaya tare da kafeshi da ido.
Cikin tura baki Jalal ya fara bayani ba tare da an tambayeshi ba yace.
“Shiya shiga sabgata Ni kuma na dakeshi”.
Cikin nuna ɓacin rai yace.
“Da yake kaine sarkin duka, ko kunyan Baba Kamal bakaji ba, ka kama Salis da duka kawai dan ka wuce da MP kana danna waƙe-waƙe da suɓale wonɗo shine tsokanar?”.
Cikin yin ƙasa da kai yace.
“To ai zaginka yayi wai ilimi ka na banza tunda gamu a lalace bakayi mana wa’azi mun shiryuba, shiyasa Ni kuma na mishi aikin wanda ba shiryayyu ba”.
Kwaffa yayi tare da cewa.
“Zagi kuma na nawa? Ba kune ke jazamin zaginba, kada ka yarda in sake jin ka taɓa shi Uhummm!”.
Ya ƙarishe mgnar da kwaffa.
A hankali Jalal yace.
“Kayi haƙuri in sha Allah bazan sakeba”.
Nan duk suka nufo cikin falon.
Suna isowa Hajia Mama na shigowa Batool na biye da ita a gefe.
Jafar kuwa da sauri ya koma bayan Sheykh tare da riƙe hannunshi ya fara ja alamun su tafi.

Shi kuwa Sheykh ƙara tsuke fuskarsa yayi ganin Batool cikin sauri ya gaida Mama, ta amsa fuska a sake tare da sanya masa al’barka.

Kana ya nufi hanyar fita, da sauri Jafar yabi bayanshi.

Umaymah kuwa da Ummi da Juwairiyya da Batool nan suka zauna suna ɗan hirarsu.

Jalal kuwa da Jamil a tare suka fita, shi kuwa Haroon falon Jabeer ya koma.

Yana shiga ya kira Jannart bayan sun gaisa take tambayarshi yaushe zai je masarautarsu nan yake ce mata.
Yana nan tafe a satin nan.

Shi kuwa Sheykh Jabeer yana fita kai tsaye Valli Hospital ya nufa.

Asibitinshi mai zaman kanshi.
Asibitin da duk nahiyar Ɓadamaya babu kamarshi.
Asibitin da in kana cikinsa zakayi zaton a ƙasashen turawa kake.

Haka lamarin yaci gaba da tafiya.
Babu mai yiwa Sheykh Jabeer batun Aysha.
Itama Aysha gani take kamar ziyara tazo ba aureba.
Tunda ita dai da idonta bata taɓa ganin mijinba, sai dai taji sunanshi.

Sosai ta shaƙu da Hibba da Umaymah, hakama Gimbiya Aminatu da Ummi.

Lokuta da dama takan shiga Bathroom tai ta kuka sabida begen ƴan uwanta.

Yau kwananta uku cur a gidan.
Idonta ma baiga ranaba.

Umaymah kuwa a sashin Jabeer yana fita.
Wata tirela ta iso har bakin Side ɗin shi.
Nan aka fara sauƙo da kayayyakin ɗaki na amare.
Ana shigarwa ciki. Kana masu aiki na ɗaure komai suna kimtsashi.

Sai kusan la’asar suka gama komai kafin.
Suka tafi kana su Umaymah suka taho.

Suna shiga asalin babban falon, Aunty Juwairiyya da Hibba suka haɗa baki wurin cewa.
“Wow masha Allah, Kai Umaymah ƙara so da sauri kiga falon nan yadda ya zama fadar masarauta”.
Da sauri Umaymah da Ummi suka ƙara so.
Masha Allah! Masha Allah!! Masha Allah!!! Shine abinda kawai Umaymah keta mai-mai tawa, sabida kyau da tsaruwan falon yayi masifar kyau.

Kasan cewar falon irin ƙaton nanne mai faɗi da tsawo.
Wasu irin kujeru ne Daimond set masu masifar kyau da tsada, a shirya a cikin tamfatsen falon.masu Golding color mai ɗan karen sheƙi sai surkin Brown color mai sheƙin gaske da ratsin ruwan madara..
Kana haka ma kalan labuyen falon masu tsawo da faɗi da taushin gaske.sai wani table na glass mai Golding color da aka ajiye a tsakiyar falon bisa wani tattausan carpet mai azabar kyau.
Sai wani babban Tv dake liƙe a jikin bongon, kana gefen dama kuwa wani babban majigine manne wanda yake baiyana rubutun Kur’ani reras daki daki.

Can gefen kuwa steps ɗin hawa Dinning area ne,
wanda aka canza Dinning table and chairs ɗin,
Aka zuba wasu masu masifar kyau da tsadan gaske.

Ba’a wani cika falon da tarkace ba, amman yayi matuƙar kyau.

Tafiya kaɗan zakayi ta gefen hakun zaka ratsa cikin wani madaidaicin falo.
Yayinda na Jabeer yake hannun dama.
falon ɗakin da Umaymah ke tsauƙa in tazo kenan.
2 bedroom ne wannan falon yake dashi ko wanne da bathroom a ciki.
Kana sai Dinning area matsakaici daga nan gefen Dinning area kuma akwai ɗan ƙaramin corridor wanda zai sadaka da kitchen da store.
wasu irin datsa-datsan kujeru masu masifar kyau da ɗaukar hankali aka kimtsa a falon wanda komai na ciki.
Peach and white coffee ne mai ɗan karen kyau.
Hakama Dinning table and chairs ɗin.
Still labulayen ma hakane.

Sai kuma cikin bedroom ɗin wanda duk girmansu ɗaya, haka yasa aka shirya wasu tagwayen gadaje masu masifar kyau suma Golding color ne mai sheƙi da ɗaukar ido.

Saɓanin side ɗin Jabeer komai Sky blue and white ne, wanda hakan yasa kana shiga sashinsa sai kayi zaton a sararin samaniya kake rayuwa.

Komai yayi kyau.
Especially kitchen ɗin dake matsakaicin falon.

Domin wancan kitchen ɗin dake babban falon ba’a taɓa shi ba, hakama Side ɗin Sheykh.

Sai kuma sama wanda shi a rufe yakema, sam babu kowa a ciki.

Sosai fa su Umaymah suka yaba da kyan shirin da akayiwa wurin.

Nan suka zauna a falon.
Umaymah ce ta kalli Jakadiya cikin sauƙe numfashin tace.
“Alhamdulillah, gobe kuma zakiyi musu jagora shida matarshi su zaga ta gaida ahlin masarautar Joɗa, ta gansu su ganta su san juna, gudun kada a haɗu a wani wurin ba’a san junaba”.
Wani gwauron numfashin Ummi ta sauke tare da cewa.
“A nan gizo ke tsakar ko ta ya zamu samu, Sheykh yayi wannan al’adar yadda ya dace ake kuma yinta, kinsanshi mutunne mai kunya, koda yana son abunma bare ba wani son abun yakeyi ba”.
Cikin yarda da kai Umaymah tace.
“Kada ki damu yana ɗaya daga cikin dalilin da yasani, na zauna sai naga kamun ludeyin zaman nasu.”

Haka dai suketa tattaunawa,
Suna nan zaune Gimbiya Saudatu ta shigo tare da hadimanta, kana da Laminu da Baba Basiru da Baba Nasiru.
Cikin isa da ƙasaita ta nufi kujerar da duk canjin da akayiwa falon ba’a canzashi ba sabida kujerace ta masarautar Jalaluddin, cikin isa take taku yayinda ta bawa ƙofar shiga baya.
Cikin gatsali ta kalli Umaymah data tsareta da ido. Kallon uku saura tayi mata kana tace.
“Duk mutun muna fuki abin tsorone. Amman munafurcin balaraben Mutun yafi na kowa muni da bada tsoro.
In banda salon munafurci ayi aure yau kwana uku a gaza fito da amarya a nunata ga mutanen masarauta, bare a fanshi idonta.”
Ta ƙarishe mgnar tana kai mazaunanta bisa, Kujerar.
Sai kuma tayi maza ta miƙa, jin muryar Jabeer da yanzu ya shigo, ko mgnar ta, ta ƙarshe baijiba.
Cikin isa da ƙasaita da rashin tsoronta, da kuma tsare fuska alamun Ni bani da lokacin ki, kuma ni ba sa’an yinki bane ya nuna mata hanyar fita da yatsarshi tare da yamutsa fuska cike da ƙarfin zuciya ya kalleta ita da ƙannen Mahaifin nashi yace.
“Fice min daga gida, bacci na dawo zanyi so banda lokacin jin ihunku na kar…!

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button