Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 76

Sponsored Links

*************
Mum Aisha na Jin ASH ya amince ya bawa Abdulhameed din Husnah ta fasa sabon kuka tana cewa Bata yardaba itama bazata iya auren kauyen ba.

Baice komaiba ya Bata kyakkyawan zabi akan ko tayi auren Daya zabar mata ko ta tattara tabar masa gidan harna Abuja harna Yola ta tafiyarta itada Naufal su tafi Babu ruwansa ko hadinsa da ita.

Wani irin kukan baqin cikin rayuwa ta sake fasawa tana barin palon ko Gani batayi jininta na hayewa gaba Daya.

Related Articles

Maamah ya kalla da alaman kema kinada magana ne?
Ta miqe a silale ta fice zuciyarta a nauyaye itama Dan kuwa yau tagama ganin qasqancin rayuwa ga baqin cikin auren kawu bello,
Idan suka ce Basu yarda ba a sake tada Wani rigimar Azo ayita tashin hankali a gabansa sauran mutuncin ya qarasa zubewa.

Tana ficewa Husnah jikinta da qafafunta na rawa ta miqe sedai bama zata iya Kai kanta cikin gida ba sbd barin da jikin keyi sosai Kuma har lokacin hawayenta Basu tsaya ba.

Abdulhameed dinne ya miqe ya kama hannuwanta ta sake qanqamesa tana tsiyayar hawaye suna fice palon aka bar Haydar Se Dad din Mr Jameel ma ficewa yayi ya Basu guri Dan suyi magana sosai.

Suna fita Husnah ta fasa kuka mara sauti tana Neman zubewa qasa Abdul ya riqota da kyau jikinsa tareda tsayawa cak Yana kallanta a natse kafin ya Bude Baki yace

“Kukan Kuma yanzu na Menene tinda bazaki auri uzaifa din ba?

Sake fasa Wani kukan tayi tana fadawa jikinsa ta qanqamesa cikin kuka take cewa

“Nidai kace gobe a daura damu kar abari saika dawo Dad zai iya sake fushi ya auramun mutumin, Dan Allah a daura mana auren muma tareda su mum Aisha gobe
ku tafi dani bazan iya zama anan ba Nima zan Biku”

Numfashi me sanyi ya sauke ahankali tareda Dan dagota daga jikinsa sbd gaba Daya a rude take shiyasa takeda maqalqalesa din.

Cireta daga jikinsa yayi gaban Daya tareda kama hannunta suka qarasa cikin gida sbd ta huta ta nutsu.

Sama yahau da ita har bedroom dinta ya zaunar da ita bakin gadonta tareda daukan tissue Dake gefen gadonta ya share mata hawayenta cikin kulawa yace ta Dena kukan ya Isa haka.

Daqyar ya samu ta dan dawo hayyacinta ya sake kwantar mata da hankali da kalmomin rarrashi da kulawa kafin ya fice ya barta kwance.

Daga dakinta Kai tsaye dakinsa ya wuce sbd nauyi da kansa da zuciyarsa sukai sbd baitaba tinanin yin aure a yanzu ba hakama yanada budurwarsa dayake tinanin aure bayan sun dawo gaba Daya itama acan take karatu tareda su.

Yana Isa daki toilet ya shige da kayan jikinsa ya sakarwa kansa ruwan sanyi sbd harga Allah lissafinsa ya kunce da lamarin duk da Baya Dana sani ko baqin cikin Hakan sbd da gaskiyarsa kaman yanda bazai iya kalla ya bari rayuwar Amatu ta lalace ba zai iya bari rayuwar Husnah ta lalace ba sbd ‘dan uwanta Haydar dayake kaunar Amatu da zuciya Daya bakuma zai iya barin AmatulMaleek ta shiga irin wannan halin ba kota halin yaya,
dakuma Dad dinta ASH dayake yiwa Amatu son da har zai iya hukunta ‘yarsa irin haka akanta Badan zuciyarsa bazata quntata da hukuncin nasa ba shi kansa,
Saikuma mahaifiyarta mum Abeeda datake tsananin kaunar tasu mahaifiyar da zuciya Daya kauna Kuma me tsanani batareda sun hada jini ba tin yarinta,,
Wannan dalilan ne yasa Bazai iya barin rayuwar Husnah ta lalaceba zai aureta Kuma zai kula da ita sbd tana Neman me kulawa da ita ne ya dorata a hanyar dangana da tawakkali bawai so qarara ba da rashin kwaba kaman yanda maamah tayi mata shiyasa duk ta koma batada lissafi ko tinanin daukan abu da sauki.

Gidan tsit ya dauka kusan kowa tasa ta ishesa ta tashin hankali da masifa,
Haydar ko Daya dawo daga gurin Dad dinsa ciwon Kai ne da toshewan zuciya gabaki daya a tareda shi sbd Kai tsaye Dad dinsa ya sanar masa AmatulMaleek shine me aurenta Kuma uban cikin dayake jikinta sbd toshe wata sabuwar hanyar fitinar ko tashin hankalin.

Abdulhameed na fitowa toilet shima ya shiga ya sakarwa kansa ruwan sanyin da kaya a jikinsa Dan samun sanyi da sassaucin zafin Daya rufe jikinsa duk da kusan ba auren ne yafi masa ciwo ba kaman yanda aka boye masa Kuma Amatun yafi Jin zafin boye masan datai Dan kusancinsu kusan yayi karfin da basa fa boyewa juna komai.

Yana fitowa kaya ya Saka na bacci ya hau gado ya kwanta gefen Abdulhameed Wanda Shima ba bacci ko alamansa a idanuwansa sbd daki Daya suke amfani dashi tin zuwansu tinda ba wani dadewa zasuyiba su koma.

Bangaren su kawu bello kuwa farin ciki ne fal a zukatansu sun kasa zaune sun kasa tsaye musamman kawu ashiru da uzaifa sbd shi kawu bello kome ne zaayi duk da komen ne Yana farin cikin Shima Dan maamah din Hutu da Jin dadi ya sauyata hakama ASH TALBA bazai barsu hakanan ba aike da kayan arzuka Akai Akai Sunday auren sirikarsa,da qanwarsa da ‘yarsa tilo a gida Daya,Aiko kayan arzuka sai sun ture duniya sabuwa.

Kawu yusufa da Sam shi aure auren be damesa ba kudi dai kudi dai kawai kallansu yakeyi bakinsa a washe yace

“Kai ashiru sai farin cikin sabon auren jar fata kakeyi kana mantawa da laraba da zafin kishinta da tashin hankalinta kana Kai matar mutane kauye laraba zata iya fasa mata hanci da langa fa,ko sati aurenka bazaiyiba Kila zai mutu Dan wlh Babu me iyawa da haukar laraba sai Kai Saka aurota,
Ga sauran matan ka Nan duk ta Maidasu bayinta Yan wahala ya zakai da matar binnin idan ka Kai??”

Dariya kawu bello ya saki Yana cewa

“Tin anan idan kasan bazaka iya karya laraba akan matar binnin ba wlh kace ka hakura bazakaiba Dan Babu ruwana a lamarin laraba ba mutunci ne da ita ba”

Uzaifa dayaji ana ambatar uwarsa shiru yayi Yana Jin ba dadi wa babansa idan har ya rasa wannan matar binnin datai jajir ta nuna kaman mangwaro.

Kawu ashiru shiru yayi Dan kuwa Shima yasan balain laraba Amma Kuma bayajin zai fasa amsar auren Aishan binnin akan laraba suna Isa zai saketa tabar gidan ya Saka Aishan wajenta tinda Daman baida gurin Saka Aishan binnin.

Kayan jikinsu kawai suka zo dasu gashi akwai daurin auren da safe basuda wasu kayan Dan haka suka cire kayan suka nade suka ajiye da niyar sakawa da safen karsu kwana dasu su yamutsasu,
Sanyin AC Dana garin duk a cikin qashinsu ya shige a Daren sbd kwanan da sukai ba kaya ajikinsu.

*******
Cikin dare sosai Amatu ta Farka daga baccinta jikinta duk yayi mata nauyi Amma dai Bata Jin ciwon komai bayan na nauyin.

Anty Farha Dake waya har lokacin da Mr Jameel ya gama fada mata duk abinda ya faru Dan kawai ta Dan sassauto masa sbd ya lura da ba lafiya ba yanda take masa a kwanakin.

Gama jinsa tayi batareda ta sauko din ba yanata lallabata tana amsa masa a taqaice saiga Amatun ta tashi kashe wayarta kawai tayi ta ajiye gefe tareda miqewa ta nufo Amatun.

Tashi zaune Amatun tayi anty Farha na mata sannu tana cewa

“Kina buqatan wanka dan jikinki ya sake na hada Miki ruwan zafi sosai ko?”

Gyada Kai Amatun tayi tana Bude Baki a ahankali tace

“Amma Ina Jin yunwa sosai anty Farha abinci nakeso”

Murmushi anty Farha tayi tana cewa

“To Abar wankan sai kinci abinci kenan.”

Tea ta hada mata me kauri mara sugar kafin ta zubo mata macaroni da aka dafa tareda potatoes da nama kadan Se carrot a ciki Wanda karima ce Mr Jameel da kansa ya kawota ta kawo musu da magrib.

Sosai Amatu taci abincin tasha tea taji jikinta ya sake samun karfi ta sauko gadon ta nufi toilet Kai tsaya tana tafiya a hankali.

Ruwan zafi sosai ta gasa jikinta dasu kafin ta fito kayan sanyi ta Sanya tayi duk Yan abubuwan da zatai ta koma ta kwanta anty Farha ta rufeta take bacci ya dauketa me dadi.

Qarfe 6 na safe tana bacci Akai knocking kadan tareda budewa Kai tsaye Mr Jameel ne ya budewa ASH din lokacin anty Farha na sallame sallarta ta dago ahankali tareda yiwa ASH din barka da asuba tana miqewa suka shigo.

Amsawa yayi a natse idanuwansa akan L.A dinsa Dake bacci kaman baby kafin ya tambayi jikin nata
Anty Farha ta tabbatar masa da lafiya kalau ne yanzu.

Anty Farha ce tafara ficewa daga dakin Mr Jameel ya bi bayanta Yana Jin kaman ya rungumeta har sai ta sauko daga fushinta gabaki daya.

Suna ficewa ya qaraso bakin gadon ya tsaya Yana sake zuba mata idanuwansa masu kyau tsawon mintina kafin ya Maida idanuwansa kan cikinta duk da Yana rufe da abin rufa Amma tinda yasan da abinsa Yana iya ganin tudinsa.

Hannunsa Daya ya Dora a cikin cikin kulawa kafin ya ranqwafo ahankali ya Dora bakinsa kan lips dinta yayi kissing dinsu Yana Jin Sonta kaman zai faso kirjinsa ya fito.

Tasowa yayi Yana kama hannunta da nasa hannun ya sarkesu tafin hannuwansu na haduwa cikin dumi da sanyi.

Cikin baccinta ahankali taji qamshinsa na shiga hancinta har cikin kanta,
Ajiyar zuciya ta sauke ahankali cikin baccin lokacinda qamshin yaketa sake shigarta sai gashi ta motsa ahankali tana kokarin farkawa.

Numfashi me sanyi ta sake tareda Bude idanuwanta ahankali sbd Jin mutum kusa da ita.

Akan kyakkyawar fuskarsa Dake kallanta nata idanuwan suka sauka ta Dan sake lumshe idanuwanta ta Bude akansa.

Numfashi mara sauti ta sauke a zuciyarta kafin ta dauke idanuwanta daga kansa ahankali batareda ta motsa ba tukuna ta zare hannunta Dayake cikin nasa ahankali tana Dan gyara Kwanciyarta.

Jin yayi jikinsa na Neman mutuwa da yanayin nata Dan haka ya sake kamo hannunta ahankali zaiyi magana ta rigasa da Bude Baki ahankali cikin sanyi da rashin kuzari tace

“Ina kwana”

Mamaki ne ya Dan kamasa sbd gaisuwar kaman daga sama ya jita bayan shi ba gaisuwan yake buqata ba a lokaci Jin lafiyanta Dana babynsa yake buqata.

Amsa gaisuwar yayi a tsanake Yana son yin magana ta lumshe fararen idanuwanta alaman bacci takeson komawa Dan haka dole yayi shiru Dan kada ya hanata baccin Kila tana buqatansa.

Tinda ta Maida idanuwanta ta rufe bacci Bai zo mata na hakama Bata motsa ba bare Bude idanuwan har tsawon lokaci kafin ta Bude ahankali tareda tashi zaune tana kokarin sauka gadon ya kalleta tareda miqa hannu zai riqo hannunta ta Dan dago ta kallesa da idanuwanta a sanyi tace zata iya ta gode.
Toilet ta wuce ahankali ta shige tareda rufo kofar.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

77
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button