Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 66

Sponsored Links

***************
Mummunan halin da Amatu ta shiga ya Sanya anty Farha hadiye nata damuwan maganganun su maamah da mum Aisha dasuka ringa gasa mata masu zafi da ‘daci ta janye AmatulMaleek suka fito dakin jiki a sanyaye ta dawo da ita dakinsu.

Suna shiga dakin zaunar da Amatun tayi ita Kuma ta nufi toilet ta shige sbd maganganunsu sun Sosa ranta matiqar gaske musamman mum Aisha datake fadan nata cikin cin zarafi da quntatawa,
Ko Mr Jameel bazata iya kiraba a wannan lokacin sbd itama zuciyarta ta sosu matiqa idan ma ta kirasa bazata iya fadan komai ba kuka ne zaizo mata dan haka ta shige toilet ta rufo kofar batareda ta iya kallan Amatu ba da take nata kukan sosai itama.

Bayan ficewansu mum Aisha kan maamah ta dawo da maganganunta masu quntatawa ta qarasa damawa maamah din lissafi
Husnah kuwa takai matakin da idanuwanta Neman bushewa sukeyi qyam ba hawaye sai ja da radadin zuciya sbd ta kasa yarda da itam ace yau din wai Amatu ce da zuwa dakin Dad dinta da daddare bayan tasan mum dinta ance Koda wasa kar abari tasan da zancen auren bare wannan sabuwar tashin hankalin.
Abin baqin ciki da takaicinta shine yanda Dad dinta duk Isa,kamewa da class dinsa da manyan mata ke bibiya zai iya kallan Amatun ma a mace bare iya taba jikinta,
Babban buri,fata da adduarta shine duk rintsi kada Allah yasa Dad dinta ya Maida Amatu cikakkiyar matarsa,Allah yasa iya wannan da suka Gani ne abin ya tsaya yanda kawai gwara mum dinta ta sani Kila Hakan ne zaisa Dad ya bar Amatun ya dawo da dukkanin rayuwa da kulawansa harma da time dinsa gaba Daya kan mum din nata.

Related Articles

Maamah silalewa tayi zaune tana tare hawayenta sake saukowa kan fuskarta kwata kwata qasar ta fita ranta gaba Daya harma da rayuwa a cikin gidan ASH Dan haka Nigeria kawai take buqatan tattara Amatun su koma ta gaji bazata iyaba,
Zuciyarta bazata iya daukan wannan lamarin ba, bazata iya barin Abeeda ta tasan da maganar auren Nan ba tana guri Daya da ita gwara ta tattara Amatun su koma inda suka fito duk ranar Daya gaji da tafiyar tasu ya warware auren Amma tabbas ta gama zaman gidansa da Amatun.

 

****Duk wannan tashin hankalin da masifar baisan anayi ba daga shi har Mr Jameel sbd farha ce jinsa da ganinsa a cikin iyalinsa to itama tana cikin sanyin jiki yau din Dan haka wanka tayi ta shirya ta fice daga gidan gaba Daya ta fita kanta ya sake sbd taso fita da Amatun Amma Amatun bazata iya fita koina ba sbd kukan datasha gaba Daya kamanninta sun sauya ga zazzabi ya rufeta na take.

A asibitin kuwa duk wasu formalities na sallama da transfer din Abeedan zuwa Nigeria ta qarasa warware acan sun gama anso Basu nurse da zata ringa kulawa da ita Amma tinda tafiya zasuyi ha zama ba sai aka barta kawai akan zata ringa zuwa kullum nurse din tana dubata kafin tafiyarsu.

A motar ambulance ta asibitin aka kawo Madame Abeedan gida Dan haka suna Jin isowan motar kowannensu ya aro nutsuwar karfi da yaji ya yafawa kansa tareda fuskewa kada ASH ya gano abinda ya faru a gidan ko kadan.

Dayake Shima kusan hankalinsa gaba Daya Yana kan Abeedan da aka kawo gida sai Bai Wani fahimci komai ba hakama little Abeedan Dayaga Bai ganta ba hakama Farha sai yayi tinanin suna tare.

Husnah da maamah farin cikinsu duk da suna cikin dacin zuciya sun bayyana murnar dawowanta a Fili tareda rasa inama zasu ajeta.

Dakunan na qasa a cike suke sbd guda uku ne,
Mum Aisha Daya Se Husnah da maamah Daya sai anty Farha da Amatu Daya.

A sama Kuma bazai yiyuba sbd Hawa da saukan tinda ko motsi Bata iya yi sosai Se ahankali take Dan motsawa daga kallo sai motsi takeyi ko magana Bata iyawa sbd kaman paralyze ne a tattare da ita bayan ciwonta.

A dakin mum Aisha dole aka ajeta nan suka tare sunata dawainiyar murnar dawowanta.

ASH kuwa fita suka sake yi da Mr Jameel sbd so yake ba delay su koma Nigeria tinda Babu abinda zasu zauna suyi din anan Dan haka zai qarasa abinda zaiyi a qasar a ranar sai su Dan huta na kwana biyu kafin su wuce kawai.

Bayan fitarsa kusan yaqe da karfin halin danne ciwon ransu suka ringa yi a gaban madame Abeeda wadda ko Bata komai sunsan tana ji Kuma tana fahimtar komai din.

Wuni guda Amatu Tay a daki kwance cikin zazzabi me qarfi da ciwon damuwa Amma Babu Wanda ya Kalli dakin datake bare dubata sbd kowa a gidan ta ciki na cikinsa.

Anty Farha ma har dare Bata dawo gidan ba Dan haka daqyar Amatu ta iya tashi ta daddafa ta shiga toilet ta sakarwa kanta ruwan zafi sosai tayi wanka.

Dan karfi ta samu da kuzari na wankan datai Dan haka tayi brush ta fito a sanyaye jiki ba kwari ta zauna dole ta daure ta shafa Mai sbd sanyi ta tashi ta saka Riga da wando masu kauri sosai sbd sanyi ta Saka hijab tayi sallolin da suke kanta harma da ishai da lokacinta yayi.

Tana idarwa fitowa tayi Dan dole da yunwar da cikinta ya kasa riqewa kaman zata mutu.

Babu kowa a palon Dan haka Kai tsaye kitchen ta wuce ta Bude fridge ta dauko Coke me sanyi da biscuits ta zauna a kitchen din ta tura hakanan taci sbd bakin da ranta Babu dadi Sam.

Abincin dayake kitchen din ta duba Taga chicken noodles ce Akai duk da Bata Wani so haka ta daure ta zuba a plate ta tura tana ci tana Jin zuciyarta bataso Amma yunwar Bazata barta ba.
Ruwa Tasha me sanyi bayan tagama ta fito.

Husnah data fito daga dakinsu ce ta ganta ko kallan juna basuyiba Amatu ta wuce dakinta Kai tsaye lokacin kusan 10 ta kusa.

Rashin layin kasar yasaka ta rasa yanda zatai ta nema anty Farha Dan haka dole ta kwanta tana shiga damuwan rashin dawowan anty Farha din itama.

Harya kwanta ta manta Bata shigo da ruwa ba dole ta taso ta fito daidai Husnah ta sake fitowa wannan Karan bin Amatun da kallo tayi zuciyarta na tafasa da qunatata da tinanin Amatun dawowan Dad dinta take Jira waton yauma taje dakinsa ta kwana kenan bayan mum dinta tana gidan.

Wani baqin ciki da kishin Hakan ne ya danne kirjinta Dan haka batai tinanin komaiba ta nufi dakin mum Aisha gurin mum dinta.

Tana shiga har Madame abeeda ta fara bacci Amma ido rufe Husnah tafara kokarin dagata tana kokarin sakawa a kujera Amma ta kasa.

Mum Aisha ce ta fito toilet tana sauri ta gama tazo ta zauna ta qarasa warwarewa Abeeda komai na abinda ta fada mata asibiti kafin zuwan ASH.

Ta fada mata aure yayi Amma Bata fada mata wa yake aurenba jikinta ya birkice Dan haka yau zata qarasa cike aikinta.

Ganin Husnah na kokarin Saka Abeedan kan wheelchair yasata qarasowa tana kallanta da mamaki tana cewa

“Lafiyanki kuwa?
Kodai ciwon haukan ne ya motsa?
Kin dai San mahaifiyarki batasan kina samun juyewar Kai ba Akai Akai shine Zaki nuna mata Dan ta birkice bayan ance a guji birkicewan nata….

Dayake idanuwanta a rufe suke Husnah din Bata tsaya fahimtar tasirin da maganganun mum Aisha keyi ga mum din tata ba sai kawai taci gaba da kokarin Dora Abeedan harta samu zaunar da ita daidai Akai ta tura ta Kai tsaye ta fice dakin tana Jin aranta gwara takai mum din tata sama ta kwana can zata Fi ma samun kulawa da wali a dakin Dad dinta.

Tana fitowa Palo da ita ta nufi hanyar Hawa sama Kai tsaye tana turawa daqyar tana dagawa sedai lamarin Yana Neman gagara sbd bazata iya turata ita kadai ba zuwa sama.

Maamah data fito itama Dan zuwa sake dubo Abeedan kafin ta kwanta tana fitowa akan kokuwan hayewa da Husnah ke kokarin yi da Abeedan idanuwanta suka sauka Dan haka da sauri ta qarasa ta kamata tana kallan Husnah da mamaki da tsoron yanda ta hawo da Abeedan stairs din tace

“Lafiya kika daukota?
Ina Zaki kaita kika hawo stairs dinnan masu tsayi da ita?

Cigaba da kokarin qarasawa da ita Husnah ta fara idanuwanta jajir suna Neman tara hawaye tace

“Zata Fi samun kulawa da sakewa a saman shiyasa zan kaita can kuma ko Dad ya dawo saman zai hawo da ita ma”

Da mamaki sosai maamah ke kallan Husnah din tana riqe Abeedan da kyau sbd sun kusa hayewa ko data fito ga Abeedan na Neman fin karfinsu a tsorace maamah tace

“Wanda baida lafiya irin haka meye zaisa a daukota zuwa Wani sama gaskia Sam wannan ganganci ne Husnah,kamata da kyau fa”

Amatu data fito daga dauko ruwa kitchen Dan bayan shigarta ta tarar Babu sauran ruwan sanyi a fridge sai ta Saka biyu ta Dan Jira suyi sanyi kadan ta dauko ta dawo.

Tana fitowa kitchen Taga abinda yake faruwa Madame abeeda da batama San andawo da ita ba Taga tana Neman gagararsu ta fado Dan haka ruwan hannunta ta jiye da sauri itama cikin mamaki me tsanani ta Isa Takai hannu zata kama musu Husnah tayi saurin tareta da hannunta Daya cikin zafin zuciya da baqin cikin yanda suke fama sun kasa qarasa hayewa da Abeedan tace

“Karki taba mum mahaifiya sbd kece silan wannan kakanikayi din da mukeyi da ita.

Mum Aisha ce ta fito tana kallansu da sauri ta hawo tana cewa

“Meye haka ne wai Husnah kikeyi,Sam ke bakyajin maganar kowa ne”

Hannu ta Saka suka qarasa cira wheelchair din zuwa stairs din sama na karshen gaba Daya suka ajeta sai alokacin maamah ta Kalli Husnah fuska ba wasa ko walwala ko kadan tace

“Banason Jin komai anan yanzu”

Tana fadar Hakan ta juya ta kalli Amatu zatace mata ta tafi kawai sai mum Aisha ta katse maamah din da cewa

“AmatulMaleek matar ASH ce Banga abin damuwa da daga hankalinda zaisa a dauko Abeeda tana fama da lafiyarta ku hawo da ita wannan tsaunin wahalar ba…….

Cikin Wani irin mugun shock dukkaninsu suka kalli mum Aisha din hankali tashe kafin suka Maida kallonsu lokaci Daya akan madame Abeeda data rufe idanuwanta ahankali tin kafin su juyo din gareta.

Maamah da Wani mummunan bacin Rai da fushin da basusan tana da shi ba ta kama hannun mum Aishan da qarfi tayi gefe da ita kadan duk da kowa na Jin abinda suke fada fushinta na bayyana cikin zafin tace

“Me kike kokarin yi?
Wace maganar ne wannan??

“Akwai karya ne a abinda na fada Asmau?
‘yar ki Bata aure mijin Aminiyarki ba data tallafi rayuwarki?
Me yasa kika bari auren yazo har yanzu idan da gaske bakyaso?
Ita Amatun da kike ganin kin tsare kin killace akan auren so nawa ta kaiwa ASH din kanta?
Kuka da tashin hankali kuka ringa yi akan Naufal Akai masa sharrin fyade bayan shima ba yin kansa bane Husnah da kike bugun gaba da ita itace ta sirka maganinsa ta turasa yiwa Amatun fyade sbd Faisal,hakama a karo na biyu da gayya ta jaki zuwa porthcrt ta sake turasa yiwa Amatun fyaden da yayi sanadin gobarar tsohon Mansion da Kuma yankewan kafarsa da ASH yayi,
Ashe ba dadi rasa Wanda kakeso ni aka kassaramun ‘da sbd yarki?…

Wani mummunan jiri da zufan tashin hankali ne me tsananin gaske ya fara tsiyayowa maamah Nan take bakinta na rawar masifaffen tashin hankalin abind mum Aisha din ke fadan Husnah tasa ayiw Amatu fyade yasata kallan cikin idon mum Aisha din tace

“Ki maimaita abinda kika fada naji kyau”””

Kafin mum Aisha data shiga mamaki da shakkar fushin datake Gani me tsanani akan fuskar maamah tayi magana Husnah ne tayi kan Amatu zata shaqota sbd tasan shikenan mum dinta jikinta rikicewa zeyi ta rasata gaba Daya hakama maamah dinma rasata zatai Amatu ta zama balai da masifar rayuwarta.

Baya Amatu tayi tareda kaucewa Husnah din
Husnah ta sake yi kanta ido rufe cikin tsananin fushi da rufewan zuciya da ido Wanda yasa maamah da mum Aisha sukayo kan Husnah din sbd qatuwar flower vase data dauka a haukace
Maamah ce ta tareta,mum Aisha kuwa kokarin kaucewa daga gurin tayi tana kokarin tura Husnah take flower vase din ta fada gurin wheelchair din da Madame abeeda take zaune idanuwanta jajir da abinda kunnuwanta ke ji mata take wheelchair din tafara wintsilowa kan stairs din kaman an jefo ball,

Gaba dayansu cikin gigitaccen tashin hankalin da baa Saka masa ranaba suka yo bakin stairs din Babu Wanda qafafunsa da hantarsa Bata tsalle a cikinsu.

Yanda ake gangarowa da kujeran daban madame Abeedan daban a stairs din ba kyan Gani daidai shigowan ASH da Mr Jameel Se anty Farha da itama atare suka shigo.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

67
*MUFEEDA’S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*
Munada kayan turaruka kala kala kama dasu
Turaran wuta
Turaran jiki
Turaran Kaya
Humra milk
Humra black
Kwalacca
Turaran moping
Freshener
Daidai sauran su
Ta a Very affordable price.
Zaku iya tuntubar mu a wannan
07040986690
Muna zaune ne a garin Kano da Abuja (life camp) sannan muna aika kayan mu ko ina a fadin kasar nan har ma da kasashen waje. Akwai tsarin wholesale wato sarı ga duk me bukata sai ya tuntube mu. MUNGODE
*MUFEEDA’S FRAGRANCE*
*GIDAN KAMSHIII*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button