Bamagujiya Hausa NovelHausa Novels

Bamagujiya 21-22

Sponsored Links

21-22*

★★★~~~★★★~~~★★★

 

Miƙewa yayi ya kalli Habeebah yayi ƙwafa ya fice ransa na suya itama duk sai taji babu daɗi amma bata isa nunawa ko a fuska ba hakance ta sanyata miƙewa tana ninke kayan dake saman gadon tace “Hajiya Barka da rana” juyawa tayi ta fice tana cewa “kudai kiyayeni kawai bansan wauta idan kika sake ya kaiki ya baro kece a ruwa shi namiji komansa ado ne mace kuwa tambari ne me wuyar gogewa”
Taɓe baki tayi taci gaba da abinda takeyi tayi wanka ta fito suka nufi kasuwa sukayo siyayyar tafiyarsu Umrah sunata shirye-shirye cike da shauƙi har wajen biyar sannan suka dawo suka baje a parlour suna shan iska Rasheedah Turaki ta shigo da sallamarta suka rungume juna suna dariya Beebah tace “Kayy amma naji daɗin ganinki dama zakizo yau ɗin baki sanar dani ba” murmushi tayi tace “Wlh ba zuwan kaina bane Captain ne ya takura sai na rakosa gdanku nace masa ya bari sai gobe yace shi yau bazai samu nutsuwa ba indai baizo ya gaisheki ba”
Haɗe rai tayi tare da cewa “Waye kuma Captain?” Kama hannunta tayi suka zauna Hudah na cewa “Ni dama tun jiya a gurin party na fahimceshi kawai dai azarɓaɓi ne banyi ba” taɓe baki Beebah tayi gabanta na faɗuwa tace “Hmm Allah ya kyauta haka kuwa zaija tsumman ƙafafunsa ya koma inda ya fito ba Captain ba ko Canal ne” kallonta sukayi Khaly tace “Amma ke kam kinada matsala haka Farooq ya rinƙa nacin binki da zuwa gdannan kikaƙi sauraronsa kuma Kilishi ta wani ɗaure Miki gindi har tana cewa tayi Miki miji to nikam bansan me ake nufi ba in da wata a ƙasa a sanar damu mu rinƙa sanarwa suma jarababbun mazan da basu gani sai sun tanka mana”

 

Harararta tayi tace “Meye a ƙasa bayan abinda kika sani nikam banason wannan abin kawai duk wanda yace muku Ni kuce masa Habeebatullah Habeeb matar aure ce Shikenan kun kar Zomo me kafar gudu sai kuma abi wani burtalin” kama hannunta tayi tace “shikenan kawai dai kinaso kicemin Yaya Mufeed baiyi Miki ba ko?” Sake daure fuska tayi tace “Inma hakan kikayi tunani to hakan ne wai badama mutum ya fadi muku gaskiya saukun sauya masa fassara Ni na faɗa muku matar aure ce ni” harara Hudah ta watsa mata lkcn da Najeeb da Habeeb suke shigowa idanunsu akanta Najeeb har yanzu babu wata jituwa tsakaninsu da ita inda shi kuma Habeeb yanayinsa ya nuna yana cikin bayyanannen tashin hankali, Hudah tace “To wai da anyi mgn sai kice ke matar aure ce to koma dai tattabara kike Sarkin aure ai kyaje ki saurareshi tunda ya tako yazo takanas don ke….”
Cak Habeeb ya tsaya zuciyarsa ta buga da ƙarfi yayi kamar ya juya ya tambaye su gurin wa akazo amma miskilancinsa ya hanashi musamman dake baya cikin nutsuwa haka yaja ƙafarsa baiji wace ta bada amsa ba ya shiga hanyar da zata kaishi ɗakinsa ya haye sama ya buɗe window ya zubawa ƙasan gidan idanu yana kallon tsuntsayen ɗawisun da suketa zagayawa a gurin zuciyarsa na ƙara ɗaukar zafi tabbas ya fahimci cikin yaran gidan Mai martaba ya tsaneshi.

 

Dukan Borghlar ɗin window yayi ya juyo ya dubi Najeeb yace “Bafa zai yuwu ba kamarni ace za’a zaɓamin matar da zan aura kuma don wulaƙanci da son ƙaskantar dani a rasa wa zaace naje na nema sai wannan ƴar Iskar Yarinyar….” Katseshi Najeeb yayi da cewa “To ya kakeso ayi ne Habeeb komi dai lalacewar goma tafi biyar Wlh nidai a ganina da wannan yarinyar da kake kallo a matsayin mata ƴar maguzawa gara Khausar sau ɗari…..”
Mari ya zabga masa yace “fice ɗan durun uwa ai dama kai nasan ba abokin arziki bane duk wani abu da zai zama maslaha ga rayuwata baka farin ciki dashi damuwata itace abar jin daɗinka to kaje ka faɗawa duk wanda kake ganin ya isa Ni banason Khausar kuma Wlh indai ta kuskura ta shigo da’irata saina keta darajarta da alfarmarta”
Fuuuu ya nufi hanyar ya fice daga ɗakin ya nufi ƙasan ya haura sashin Kilishi tana zaune gefen gado yace “Amma Hajiya kinsan da mgnr yar iskar yarinyar nan baki faɗamin ba to Ni zan rikito sama Wlh inyaso ta rufe kowa bazance bazan auri Khausar ba amma fah zan sanar da ita kuma zan bata zaɓi indai zaman lfy takeso da kwanciyar hankali to kada ta bari ta shigo da’irata don Wlh saina kasheta da baƙin cikina”

 

Tunda ya fara mgnr ta zubansa idanu har Saida yayi shiru tace “To ya kakeso nayine Habeeb mahaifinka tsoron furucinsa nakeyi tunda ya riga ya furta saiya aiwatar kai kuma taka ƙaddarar kenan daga wannan sai wannan”
Juyawa yayi kamar wanda akayiwa allura ya fice ya nufi waje tunda ya fito yaji juwa tana ɗibansa ganinta tsaye ita da Mufeed Kilishi ce tace taje ta basa hkr kada yaga ta wulaƙantashi ta sanar dashi ita matar aure ce, shine dalilin da yasa ta fito koda taje ɗin gaisawa kawai sukayi batakai ga mgn ba Habeeb ya fito idanunsa akansu itama nata akansa ƙirjinta ya buga da ƙarfi daga yanayin kallon da yake yi mata ya tabbatar mata yau ta shiga uku….
Ilai kuwa yana zuwa baiyi wata² ba ya ɗauke ta da marin da Saida ta fasa ƙara saboda azaba ya ɗaga hannu zai ƙara mata Mufeed ya riƙeshi cikin hassalar zuciya irinta sojoji yace “Haba mal me tayi maka da zaka maret….” Fuzge hannunsa yayi yayi kansa sai kuma ya tsaya yace “Kai ɗan akuyan wacce ƙasa ne da zaka tsayamin da mata kake tuhumata kuma akanta?”
Bai jira amsar Mufeed ba ya figi hannunta ya nufi ciki da ita ya cillar da ita a tsakiyar parlourn ta rintse idonta ya nuna ta da yatsa, kuma sai ya juya ya fice Hudah da Khalisa da Rasheedah suka miƙe sukayo kanta jin da tayi an riƙo hannunta yasata buɗe idanunta hawaye ya zubo mata sharrrr tace “Kungani ko shiyasa nace bazanje ba idan yaganni kasheni zai…..”

 

Miƙewa tayi ta nufi ɗaki saboda kukan da yake neman cin ƙarfinta Hudah ta kalli Khalisa tace “Ban gane ba?” Itama kallonta tayi tace “Nima bangane ba Meye alaƙar Bro da Beebah kiga yanda yake neman kashe ƴar mutane” miƙewa Rasheedah tayi tabi bayan Beebah ta bata taddata a ciki ba hakan yasata nufar ɗakin Kilishi ta tararta ta kwantar da kanta a cinyar Kilishi tana kuka tana cewa “Don Allah Kilishi kibashi hƙr kinga Saida na faɗawa Rasheedah kikace naje kar yace na wulaƙantashi Ni tsoro na ma kada Bro yayi masa wani abu….” Share mata hawayen tayi tace “ki daina kukan haka mijinki yana cikin damuwa yau Habeebatullah Wlh Ni kaina bana iya control zuciyar Habeeb idan zuciyarsa tana sama kedai kada ki cika matsarsa a wannan lkcn kada ya hucce a kanki”
Ɗagowa tayi tace “Meye yake damunsa?” Ajiyar zuciya Kilishi tayi tace “Karki damu komai zai wucce” daga haka ta kalli Rasheedah tace “Rasheedah kibashi hkr kinji” cikin sanyin jiki Rasheedah tace “Insha Allahu mun gode Hajiya Habeebatullah saikun dawo kar a manta da abayata” da wannan ta fice ta ishe Mufeed ya haɗe kai da sitiyarin mota ta buɗe ta shiga tayi masa mgn baiji ba Saida ta danna horn sannan ya ɗago firgigit yaja ajiyar zuciya idanunsa sun kaɗa sunyi jawur yace “Da gaske matar aure ce?” Rintse idonta tayi tace “Haka yanzu nakeji gurin Kilishi”

 

Dukan sitiyarin yayi yace “Ƙarya ne Wlh babu wanda ya isa ya auri matata…” Key yayiwa motar ya figeta da mugun gudu ya fice daga gidan sarautar yana huci kamar zaici babu suna zuwa corner gdansu ya tsaya ya kalli Rasheedah ta buɗe ta fice sumsum tasan tana cika matsawa jikinta ka iyayin tsami”

 

12:55am tana zaune gefen gadon ta kasa bacci saboda damuwa gabaɗaya yinin yau ta fahimci kowa dake gidan zuciyarsa babu haske musamman Hero ɗin ta da ko falo ma ya daina fitowa saidai ya kira waya yace da Kilishi ta sanyata ta kai masa abinda yake buƙata Kilishi taƙi yarda da wannan sawarwara musamman yanzu data fahimci abubuwan suna kusa da rikicewa.
Yau tun safe yake kwance bashi lfy zazzaɓi me zafi da ciwon ciki sun kasashi a gaba Beebah tasan bashida lfy shiyasa hankalinta yaƙi kwanciya musamman ɗazu da likitan gidan yazo dubashi taje wuccewa taji yanda yake yi masa fada, batasan faɗan mi yake yi masa ba amma ta fahimci koma Meye yake damunsa to babba ne.
Tun yamma takeson zuwa ta gano jikinsa Kilishi ta kasa ta tsare a parlourn wannan yasa ta hƙr gashi yanzu ta kasa bacci damuwa ta ishe ta so take kawai taji halin da yake ciki, jifa tayi da wayar hannunta ta kira layinsa yakai sau ashirin amma yaki ɗagawa, hijjab ta dauka ta ɗora kan rigar baccin jikinta, zuciyarta ta kasa jurewa itakam bazata iya zama batare da tasan halin da yake ciki ba, buɗe ƙofar tayi a hankali yanda bazaajita ba ta waiwaya ɗakin Kilishi tagansa a rufe ta sauke ajiyar zuciya ta nufi ƙasan da sanɗa tana duba agogo 1:15am.

 

Turus taja ta tsaya cikin tsoro duk da babu wadatar haske a parlourn amma bata kasa gane Kilishi ba, itama Kilishin kallonta takeyi da mamaki tace “Habeebah ina zaki?” Cikin karayar zuciya tayi ƙasa da gwiwarta muryarta na rawa tace “Ki…Ki…li…shi Hero bashida lfy don Allah kibarni naje na gansa kada ubangidana yayi fushi dani inajin tsoron fushinsa ya rabani da rahamar ubangiji tun jiya yaƙi ɗaga wayata….”
Zubanta idanu Kilishi tayi sai taji jikinta yayi sanyi ta lumshe idanunta hawayen tausayinsu ya zubo mata tabbas tsakanin mace da miji sai Allah idanma ka shiga kunya ta tabbata gareka ita tana ganin gata takewa Habeebah ashe ita mijinta kawai take kallo Bama ta duba maslahar kanta daga kalaminta ya nuna mijinta yafi komai muhimmanci a sashin rayuwarta.
Miƙewa Beebah tayi cikin sanyin jiki kukanta na ƙara ƙarfi ta juya ta nufi saman Kilishi tace “Habeebatullah!” Tsayawa tayi kukanta na ƙara ƙarfi batare data juyo ba, takawa Kilishi tayi ta dafata tace “Ubangiji yana fushi da mutumin daya shiga tsakanin ma’aurata Habeebah nasani kinason mijinki Wlh ban hanaki kusantarsa ba saidon abu ɗaya amma Ni da kaina na fahimci lkc yayi da zan bawa mijinki dama akanki domin idan naci gaba da sanya shamaki tsakaninku tabbas zaku cutu, kije gareshi yana buƙatar tallafinki amma kiyi hƙr da yanayin da zaki fuskanta baƙo kowacce mace da haka ta saba”

 

Ajiyar zuciya Beebah ta sauke ta rusuna tace “Na gde Hajiya” murmushi tayi ta nufi saman tace “Jirani” tsayawa tayi tanabin Kilishi da kallo har ta haye saman can ta sauko da wani kwalin magani a hannunta ta balli guda biyu ta bata ta miƙa mata ruwa tace “kisha” babu musu ta karɓa tasha dakanta ta rakata har ƙofar ɗakin dake a buɗe take ta murɗa mata ta shiga gabanta na faɗuwa taji Kilishi taja ƙofar ta rufe ta juya ta kalli ƙofar sannan ta juyo wa gadon da yake kwance bata ganinsa sosai saboda glub na ɗakin bamai haske bane hakan yasata kasa tantance bacci yake ko idanunsa biyu, takawa tayi a hankali ta isa bakin gadon ta tsaya akansa. Tun shigowarta yaganta don ba bacci yake yi ba mararsa keyi masa azabar ciwo, sanin ba mafita zai samu daga gareta ba yasashi lumshe idanunsa, tsugunnawa tayi gabansa tasa hannunta ta dafa goshinsa cikin rawar murya tace “Nasan ba bacci kakeyi ba My Hero domin Kilishi yanzu ta fita anan mun hadu a hanya kawai dai kana fushi da marainiyar baiwarka da batada wani gata bayan naka ne”…..
Kuka ne yaci ƙarfinta ta ɗora kanta a ƙirjinsa tana shafa sumarsa a hankali da wani salo da yake narkar da zuciyarsa tace “Idan har zaka iya fushi dani akan abinda umarnin samanka nabi My Hero ina na kama cikin rayuwar da banida kowa bayan gatank……” Kalmar ta ce ta kashensa jiki yasa hannu ya dafe bayanta yana shafawa a hankali yanajin sautin kukanta na ƙona masa zuciya yaja numfashi yace “stop crying Wyf na daina fushi dake ya isa kukan banaso” ɗagowa tayi ta sanya hannunta ta kama gefen fuskarsa ta shafa sajensa tace “surely?” Murmushi yayi ya buɗe idonsa akanta yace “Aa zandai tabbata idan kin kula dani kinmin maganin ciwo na….”

 

Kwantar dakai tayi tace “Meye shi” yunƙurawa yayi ya tashi ya kama kunnenta ya raɗa mata ta zaro ido tana ƙoƙarin janyewa ya birkitota jikinsa ya janye blanket ɗin daya rufe jikinsa ya shigar da ita tare da janye mata hijjab ɗin a kasalce yace “Sorry baby mutum najin yunwa ki bashi abinci kice kuma zaki ƙwace kema kinsan bazai yiwu ba”
Yanayin ya fara sauyawa sosai takeson jurewa duk abinda yake yi mata amma tsoronta na ɗabi’a yana neman kawo masu cikas wai a haka ma bakin ƙoƙari take na taga ta daurewa abinda yake yi mata, Habeeb ɗan duniya ne na gaske yayi duk me yiwuwa duk wata hanya da yasan zaibi yabi ya cire mata tsoro damuwar ɗaya yanzu tunanin yanda zata wayi gari da safe shine yasa take ƙoƙarin ƙwatar kanta babu dama domin yakai ƙarshe banda Nishi da sakar mata kiss ta ko ina da sarrafa duk wani guri da yasan zataji saƙonsa babu abinda yakeyi.
Idanunta ya fara raina fata ne lkcn da ya sanya yatsansa a HQ ɗinta sai azabar da taji kwanaki ta zame mata me sauƙi saboda wacce a cikin hayyaci yake wannan kuwa alamu duka sun nuna baya tare da duk wani abu nau’in nutsuwa a tare dashi, haɗe bakinsa yayi da nata ya kashe hasken ɗakin gabaɗaya ya cire boxes nasa ya fara nemawa kansa hanyar samun nutsuwa ta rintse idonta da ƙarfin gaske tare da fusge bakinta daga nasa ta saki wata azababbiyar ƙara ta fitar hayyaci yayi saurin toshe mata baki yana ƙara shigarta a burinsa na hudata, ba itaba shima Saida yaji a jikinsa kafin hakansa ya cimma ruwa duk da wahalar da yasha bai hanashi jin wani shauƙin daɗi nutsuwa da wata sihirtacciyar kauna jin ƙai da tausayinta na ratsa ilahirin jikinsa ba burin masoya ya cika yau Habeebatullah ta tabbata ta Habeebullah……….

 

_IDAN KIKA KARANTAMIN LITTAFI BAKI BIYANI BA BAN YAFE BA_

[5/2, 7:32 PM] AM OUM HAIRAN

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button