Hausa NovelsIn Bani Hausa Novel

In Bani 20

Sponsored Links

20….

_This novel is for sale, karki karanta in baki biyaba, in kika karanta ina binki bashi, pay anan ko acahn_

_in kinason novel dinan zaki turo 300 access fee to 3107021073 first bank aisha Muhammad, saiki turo evidence of payment to my watsapp number 07012181461_

Related Articles

_you can also send MTN card to watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting_

 

Tureshi tayi da karfi tace “na shiga uku dan Allah ka dagani, ga abincin ka chan” sake make mata kafada yayi cikinshi na murdawa dan har kukan cikin tanaji, dan kwantar da murya tayi tace “look at your food there, pls dagani” ahankali ya dagata ya kalli fuskarta jin yanda tai maganan muryanta na rawa sosai kaman tana kuka, hawaye yaga tana shareware, ware ido yayi sosai kaman dan yaro saikuma yafashe da kuka maidan kara yace “you are crying whyyy?” da sauri ta tashi daga kwancen gudun kar Kaka tajishi ta share fuskarta da bayan hannu ta kakalo murmushi tamai tace “kagani niba kuka nakeyi ba” hadiye kukan yayi ya kalleta irim kallon da gaske mugani, murmushi ta sakar mai hakan yasa shima yasakin mata murmushi mai kyau sosai yana kara kama cikinshi dayaji ya murdamai da sauri ta tashi ta dauko mai abincin ganin yanda yayi takawo gabanshi ta bude kulan tuwon shinkafa ne da miyan dry kubewa ta kalleshi yanda yake binta da kallo ta nunamai kulan tace “eat” kallon abincin yayi yasake kallo sanan ya yatsine fuska kaman yanda yara keyi yace “wat is this? I want rice with meat balls, i want yam fritata, i want smoked prawns” zaro ido tayi ta kalleshi dan wlh wasu abincin ma daya kira batasan suba hakan yasa tabuga uban tagumi ta lankwashe kafa tana kallonshi inda ace za’a gwada jinin ta yanzu sai anga yahau dan wlh fargaban gobe take, kukan shi ne yasa ta dago kai da sauri ta kalleshi sosai yabata tausayi dan ayanda yayi gaskiya baisan abincin bane, da sauri tace “zakaci biscuit to?” gyadamata kai yayi yana neman fadowa jikinta da sauri ta tashi tabude sip dinta, chan saman kayan ta taboye biscuit din sabida kar Ihsan tagani ko Zainab ta dauko guda biyu ne short bread biscuit tadawo ta zauna agabanshi ta mikamai, karba yayi da sauri yana murmushi yana kallonta sanan yabude daya ya ijiye daya agefe yasa hannu yaciro biscuit daya ya dago kai da sauri ya kalleta kaimata dayan bakinta yayi da sauri ta kalleshi, murmushi yamata yana wani irin kallonta kaman wani mai lafiya ya ware manta manyan idanunshi dake cike da bacci gashin idon duk sun tattare sabida lema leman ruwan hawaye yace “eat my wife yay” zaro ido tayi ta kallai, fari yamata da ido yana goga mata biscuit din a lips kaman yana shafa mata jan baki yace “eat, haaa, haaa, hamm” yay maganan yana bude mata baki kaman yanda akema small baby yaci abinci, dan murmushi tayi ganin yanda yake bude mata baki bama tasan lokacin data saki murmushin ba sabida yanda yay maganan dan har yasa ta manta da fargaban datake ciki na gobe, ahankali tasa hanunta ta karbi biscuit din daga hanunshi takai bakinshi tai murmushi tace “kaika ci kaine kejin yunwa, eat” bude bakin yayi da sauri kaman jira yake ya balli kadan yanaci yana kallonta lumshe ido yayi yana taunawa saikuma yabude idon ya kalleta suka hada ido yace “is very sweet” ya fizge rogowan daya rage daga hanunta yakai bakinta yace “eat my wife” dan kallonshi tayi dan duk idan yace my wife”sai gabanta yafadi tadan balli kadan da sauri yatura sauran bakinshi yataso yadawo kusada ita kaman an jehoshi ya kwanta ya daura kanshi kan cinyarta yanacin biscuit din yana kallonta yana mata murmushi sosai wani irin farin ciki yakeji idan ya kalleta fiye da misali dan ko damuwa dasu Mami ma baiyiba shi kawai bayason ta barshi konan da chan, tagumi tabuga itama tana kallonshi tana tunani sosai, maganan shine yadawo da ita daga duniyar tunani yace “water” pure water daya ta dauko ta mikamai, tashi yayi ya zauna ya karba yana kallon ruwan yana juyawa dan bai taba shan irin wanan ba, ganin haka yasa ta karbi ruwan tabude mai takai bakinshi da sauri ya kafa baki tareda daura hannayenshi kan nata yakara rike ruwan da kyau yanasha, wani irin sanyi taji har brain dinta da sauri ta lumshe ido saida yakusa shanye ruwan sanan ya janye kai yana murmushi yana kallonta, dan murmushi tayi itama ta dauke kai tadau marfin kulolin abincin tana rudewa tace “jeka kwanta akan gado” make mata kafada yayi ya nuna mata kan dadduman data kwanta akai dazu yana turo mata baki yace “lets sleep there” kallonshi tayi saikuma ta chusa kanta kan kafarta tai shiru abin duniya yay mata yawa, wanan wani irin kaddara ne tahadu dashi, shima shiru yana kallonta duk sai yaji wani iri kaman baida lafiya sabida yanda ta kifa kai taki kallonshi, ahankali ya share hawayen daya zubomai kaman maraya ya kwanta akasa a gefenta ya jefar da ragowan biscuit din dake hanunshi yana kallonta yana lumshe ido yana goge hawaye, ahankali kaman matsoraci ya dafa kafadarta yakira sunanta “my wife” ture hanunshi tayi cikeda masifa data dade batai irinshi ba dan tagaji da yanda yake tabata yace”leave me alone” ta turemai hanun tasake maida kanta kan guwiwa, matsawa baya yayi atsorace yana kallonta yasaki kuka ahankali yana share ido da bayan hannu, ahankali ya kwanta akasa awurin yana kuka sosai yana kallonta so kawai yake tadago kai ta kalleshi, haka bacci yasake daukan shi kaman zaiyi ihu ya dukunkune gwanin ban tausayi.
🌹IN BANI 🌹

 

Maman Abd Shakur

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button