Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 34

Sponsored Links

*GARKUWAR FULANI*Ta ɗan ja tayi sama da bakin ƙafan wonɗon wanda yake na robane bakin a tsuke yake.
Da sauri cikin tsoro da rawan jiki ta saki robar.
Pat ya fetti a jikinshi.
Ganin ya motsa.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wani sassanyan numfashi ya ja mai tsawo tare da fesoshi a hankali kana, ya mirgina a hankali ya juya ya kifu cikin kasalan nauyin bacci ya ɗaura kanshi bisa cinyarta,
Kana ya ware hannayenshi da sukayi ɗan tsami sabida pillow’n da yayi dasu.
Ware hannayen yayi tare da miƙarar dasu.
Ya zama tana tsakiyar hannunshi kana kanshi na kan cinyoyinta.

Haɗe hannuyen nashi yayi ya sarƙafe yatsunshi wuri ɗaya, ya zama ya zagayeta tako ina yayi mata ƙawanya.
Ya cusa hancinsa cikin mayafinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinta dana kayanta.
A hankali ya kuma gyara kwanciyarshi da kyau kana yaci gaba da sauƙe sassauƙan numfashin.

Ita kuwa Shatu wani masifeffen tsalle da bugu zuciyarta keyi tamkar zaiyi tsalle ya fito woje.
Gaba ɗaya ida nunta kan sumar kanshi ta zubasu.
Tare da kallon tattausan sajenshi dake kwance lib-lib a gefen fuskarshi.

Related Articles

Wani sassanyan numfashi ta sauƙe tare da lumshe idonta cikin zuciyarta tace.
“Allah shi ƙara”.
Sai kuma tayi sauri ta buɗe idonta tana tambayar kanta.
“Allah shi ƙara me ɗin? Ya ƙara ruggumata ko meyeye”.
Cikin kauda zancen a ranta ta ɗan muskuta dan janye jikinta. Amman sai ta ji ya riƙeta gam-gam, yana ƙara cusa kanshi cikin jikinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren jikinta.

Cikin tsoro murya na rawa a hankali tace.
“Yah Sheykh!”.
Karab sautin muryarta ya ratsa kunnuwanshi.
Sai dai ko motsi baiyi ba,
A hankali ta kuma ce.
“Yah Sheykh! Yah Sheykh!!”.
Shiru babu amsa sai numfashin da yake fiddawa a hankali yana kuma shaƙan ƙamshin jikinta.
Cikin sanyi ta ɗan ɗago hannunta a hankali tasa taffin tattausan hannunta, ta ɗan rinƙa buge gefen fuskarshi a hankali a hankali tanayi tana cewa.
“Yah Sheykh! Yah Sheykh! ! Tashi wai Affan dasu Yusuf sunzo, shine Affan yace inzo in tasheka”.
A hankali ya buɗe idonshi,
Yanayin yadda take ɗan marin gefen fuskarshi da hannunta wanda ke ɗaure da agogo.
A hankali ya ɗago hannunshi ya ɗan kan hannunta ya kamoshi ya riƙe, cikin tsoro ta fara kiciniyar kwace hannunta,
Sai kuma tayi zuru, jin ya ja hannun da ɗan ƙarfi ya kawoshi dai-dai saitin fuskarshi.
Idonshi ya zubawa yatsun hannunta da kullum in ya gansu da jan lalle yake tuna mishi baya.
Da sauri tace.
“Wash Allah na”.
Jin ya murɗa hannun ya juyo da fuskar agogon inda zai gani.
Ƙarfe biyu da miti arba’in da ɗaya.
Du-du baccin 40 minutes yayi tazo ta tasheshi.

“Harda zuba min maruka”.
Ya faɗa a ransa.

Ita kuwa kan tattausan suman ta ajiye sinsiyar hannunta.
tana jin kanta na sara Especially in ta kalli saitin ƙasan gadonshi.”

A hankali ya sake hannunta kana ya yunƙura ya juya rigingine,
ya fuskanci sama, ita kuma tana zaune tana kallon ƙasa hakanne yasa suna fuskantar juna, cikin wani irin yanayi ya zuba mata ido na wasu sakanni.

Shigarta tayi masifar mishi kyau. Kodan tasa kalan kayan da yafi sone.
Cikin muryar bacci yace.
“Shine harda dukana? Meyasa ne ku mutanen garincan kuke son dukan mutun da kallon jikinsa?”.
Cikin tura baki tace.
“Cinyana, nagaji kanka nauyi”.
Bai janye idonshi a kantaba ya yunƙura ya tashi zaune tare da juyowa ya fuskanceta.
tanƙwashe sawunshi yayi tare da cewa.
“Me zaki kalla a jikina? Woto Kin zama kamar ɓarauniya ko? Me kike son gani? Wani abu kike sone?”.
Cikin tura baki tace.
“Nifa tada kai a bacci kawai nayi”.
Hannunshi yasa ya riƙo hannunta, yatsunta ya zubawa ido, cikin wata murya mai sanyi yace.
“Masha Allah, kinyi kyau.”
Wani irin sanyi taji kalmar tashi tasa mata a ranta, ido ta ɗan ɗago ta kalleshi.
Shima ita yake kallo, ido ya lumshe jin sautin zazzaƙar muryarta a hankali tace.
“Nagode”.
Tonƙoshe kansa yayi bisa kafaɗa kana hankali ya sake hannun nata.
Fuskarta ya kalla tare da taɓe baki yace.
“Waya koya miki irin sa lalle Mammeyyyyy nah!? Dan tafi ko wacce mace iya lalle”.
Cikin sanyi da nazartar yadda ya kira sunan Mammeyyyyy da yadda lokacin ɗaya idonshi suka fara sheƙin tsastsafo da zafafan hawayen da ba zubowa zasuyiba.
Cikin son gano meke cikin zuciyarsa tace.
“Ummeyy nah ce ta koya min tun ina ƙaramar”.
Yatsunta ya jujjuya kana ya miƙe tsaye.
A hankali ya juya ya nufi bathroom sabida baya son ta hango wutar ƙunar dake ransa.
Ita kuma binshi da ido tayi,
tare da langoɓar da kanta tana kallon sharabansa da gargasa yayi musu ƙawanya.

A haka ta shiga wani nazarin tana mai maimaita sunan da taji ya kira da cikekken so shaƙuwa ƙauna tausayi rauni shogoba *Mammeyyyyy.* Ta maimaita sunan a fili.

Shi kuwa Sheykh Jabeer al’wala yayi kana ya fito.
Yayi mamakin ganinta a zaune bata fita ba.

Hararanta yayi ganin yadda taketa kallonshi. Jallabiyar shi ya zura, kana yasa al’kyabbar, tare da sa Hiraminshi.
Sannan ya fesa turare.

Duk inda yayi tana binshi da ido.
Wayarshi da yafi yawan riƙewa ya ɗauka ya zura a al’jihunsa.

Sannan ya nufi bakin ƙofa inda takalminshi suke yana cewa.
“Wannan kallon maitan fa”.
Da sauri ta janye idonta.
Cikin daƙilewa yace.
“Kada ki cinyeni da ido fa. Bana son kallo, ko kina bina bashine?.”
a hankali ta miƙe tare da lumshe ido ta biyu bayanshi.
Tana gyara mayafinta tare da cewa.
“Ni ban kalleka ba”.
“Uhummm.” yace a taƙaice.
Kusan a tare suka fito.
Yana gaba tana bayanshi,
Suka fito tsakiyar falonshi.
Tsayawa ya ɗanyi ya gyara masaƙalin Al’kyabbar tashi.
Shiyasa ya zama a jere suke tafiya tana gefen damanshi.
A haka suka fito cikin corridor’n.
Suka doshi Falon cikin kwarjini da dacewa da juna sai ƙamshi da sheƙi zallan kyau sukeyi.

Da Sallama a bakinshi suka kutsa kai cikin falon.
Wani irin dariyar jin daɗi Affan da suke can Dinning area yayi, suna cin abinci da Ummi ta matsa suci.
Wani irin murmushi Yusuf da Aryan ma sukayi tare da miƙewa suka nufi inda uban gidan nasu ke tsaye da kekyawar tauraruwarshi mai haskawa.
Affan kuwa wayarshi ya zaro yana kekkebta musu hoto tare da cewa.
“Ga amarya, ga ango, suna carabki da zallan kyau da ƙamshi”.

Murmushi sukayi dukansu, ita kuwa Shatu tana tsaye gefenshi.

A haka su Affan suka iso.
Suna Isa Affan ya ruggumeshi shima Sheykh ruggumeshi yayi tare da make ƙeyarsa.
Da sauri ya janye kanshi tare da cewa.
“Wayyo Allah na yanzu Hamma Jabeer na girma harda yaran nawama ban wuce dukaba”.
Murmushi yayi tare da, Ruggume Yusuf da Aryan Allah ya sani yana masifar son yaran nan har gobe bashi da ɗalibai sama dasu yana sonsu so na musamman, duk sanda ya gansu yakan tuna ƙuruciyarsu tun suna yan shekara goma sha biyar-biyar yake tare dasu shi ya horas dasu.
Yana tura irin tarin ƙalubale da suka fuskanta a gasar Polo da kuma irin nasarorin da suka samu Especially Yusuf nashi yana tuna yadda yaran suke sheƙiyanci in sun haɗu, yana jinsu tamkar su Jamil.

Cikin murmushin ya shafa kansu tare da cewa.
“Sannunku da zuwa”.
Cikin jin daɗi sukace to.

Bisa kujera ya zauna su kuma suka zauna a ƙasa a gabanshi kan carpet.

Ita kuwa Shatu a hankali ta juya ta nufi kitchen ganin Ummi ta nufi can.
Hibba kuwa na gefensu tana gayawa su Jalal ga Ya Affan fa.

Da gefen idonshi ya bita da kallo.
Har ta ɓacewa ganinsa, Allah ya sani yana son abu blue baya iya cire idonshi kan abu mai kalar shiyasa yake jin baya gajiya da ganinta, da zai samu kada tayi nesa dashi, dan tayi mishi kyau sosai farar fatarta ta fito fes kamar balarabiya ji yake tamkar ya bita duk inda tayi.

Cikin murmushin ya kalli Aryan yace.
“Aryan Ina su Yusuf ƙaramin”.

“Alhamdulillah suna lfy Malam”.

Kai ya jinjina tare da cewa.
“Masha Allah”.
Sai ya kuma kalli Yusuf yace.
“Ina mai sunana baka zomin da shiba”.
Murmushi Yusuf yayi tare da cewa.
“Malam baka tambayi Aryan ƙaramin ba da yakeso ya zama kamarka sai ka tambayi mai sunanka”.
Dariya sukayi kana yace.
“Ayyah my Aryan, sun kusa tafiya ai in sha Allah Jami’atul Madina zaiyi karatunshi”.
Da sauri suka juyo suka kalli Jalal da Jamil da suka shigo da sauri.
Ruggume Affan sukayi suna cewa.
“Oyoyo ya Affan”.
Hannu ya basu suka tafa kamar sa’ao’,insa ne su.
Cikin dariya yace.
“Tun ɗazu nake kiranku bakwa ɗagawa.
Nace waɗannan ana can cikin hayani “.
Murmushi Jamil yayi tare da miƙawa Yusuf hannu wanda ke cewa.
“Oh wato Affan kawai kuka gani mu ko oho ko”.
Cikin ɗan sakin fuska Jalal yace.
“Afwan Hamma Yusuf ya Aunty Zahra da Mama”.
“Suna lfy. Sun gaidaku”. yace tare da bashi hannun.

Kana suka gaisa da Aryan.
Sannan suka miƙe sukace bari suje wurin Aunty Mami.
Cikin dariya Affan yace.
“Eh kujema kuzo da ita taga matar babban yaya”.
Da sauri Jamil yace.
“A a ka kawota da kanka dai”.
Ya ƙarshe mgnar suna fita.

Su kuwa cikin yin ƙasa da kai Yusuf yace.
“Uhum dama Malam zamu ɗan shiga wasan daba ne in batsala”.
Murmushi mai faɗin Sheykh yayi tare da cewa.
“Wato ku dai har yanzu baku girma da batun doki ba”.
Shiru sukayi sai Affan ne yace.
“Tab Yusuf kuma da in ya ga doki bai hauba jikinshi har rawa yakeyi”.
Murmushi Sheykh yayi kana yace.
“To muje muyi salla. Tukun tunda sai anyi sallan la’asar za’a fara ko”.
To sukace tare da miƙa ganin ya miƙa dan tuni uku da kwata ta wuce.
Affan ne ya kira Ummi tare da cewa suzo zasu tafi.
A tare suka fito kitchen.
Sabbin kuɗi rafa yan dubu-dubu Yusuf ya miƙawa Hibba ƙulli ɗaya dubu ɗari kenan yace.
“Gashi miƙa wa Ummi ta raba muku.”
Affan ma ya basu.
Hakama Aryan.
Hibba sai tsalle take tana cewa.
“Yessss my brother’s Allah ya ƙara buɗi Amin Amin sukace kana suka juya zasu fita.
Cikin tsare girma Shatu tace.
“Mun gode, a gaida gida”.
Gida zaiji sukace kana suka fita suka tafi.

Suma su Ummi wucewa sukayi yin al’wala.

Ana idar da salla kuwa aka fara hawan daba, hawan sarki dama duk sauran shagulgula na gidajen masarautun gargaji yayin wurin taron bikin salla.
MASARAUTAR Joɗa ta cika tayi maƙil da bani Adam.

Haka dai akayi taron lfy aka tashi lfy sai kuma gobe in Allah ya kai rai.

Washe garin ranar da sassafe.
Sheykh ya tafi asibitinshi.
Ko karyawa baiba.
Sai kusan sha ɗaya ya dawo da alamun yunwa da gajiya tare dashi.
A falon ya zauna suna gaisawa da Ummi dan basu gaisaba ya tafi daga masallacin can ya wuce.
Ummi kuwa tasa Shatu ta kai mishi breakfast ɗin shi da yanzu kam in yacima ya zama lunch ne.

Hibba kuwa na can ɗauki tana ƙenƙesa ado.

Cikin isa da ƙasaita Gimbiya Saudatu ta shigo tsakiyar falon babu ko sallama.
Haɗe fuska Sheykh yayi tare da cewa.
“Wannan banzan ɗabi’a na arnatakun baya, dan ko arna yanzu suna cewa konkon, mutun kamar shanu ko mahaukaciya”.
Cikin isa ta iso tsakiyar falon.
Dai-dai lokacin kuma Shatu ta fito falonshi.
Cikin shigar doguwar riga mai ruɓi biyu.
Kanta ta ɗago ta kalli Shatu kana ta kalleshi cikin yin dariyar mugunta tace.
“Eh kam tabbas tunda ka auro mahaukaciya dole kasan hali da ɗabi’un mahaukata ai.
Zuwa gaba kaɗan kaima zaka fara ihu da kuka da sume-sume irin na wannan al’janar fulanin daji daka auro ɗin”.
Cikin tarin mamaki Ummi ta kalli Shatu ta kuma kalli Hibba da yanzu ta fito, cike da al’hinin ta yaya taji wannan batun ya fasa Masarautar Joɗa yes in dai Gimbiya Saudatu taji to ai shike nan kowa ma zaiji.

Shi kuwa Sheykh ba gane inda soki burutsunta ya nufaba yayi.
Ita kuwa cikin watsa musu kallon ku sakarkaru ne tace.
“Kuna mamakin ta ina naji, cewar ji shekaran jiya iwar haka dai wannan matar tashin tana yashe a sume da ido a wulkice tana ƙarkarwa farfaɗiya kamar mazari ne.
To ai Ni duk wanda yaci tuwo dani miya yasha.
Inada tawa a cikinku duk motsinku ina dashi a tafin hannuna.
Nan gaba kaɗan zamu samu riƙeƙƙiyar mahaukaciya a masarautar Joɗa”.

Cikin tsuke fuskarsa yace.
“Yanzu ma ai muna da su mahauka ta kam, ke ɗin me banbancin ki da zararrun”.
Shiru yayi ganin yadda Shatu keyin taku a hankali cikin isa ta nufi gaban Gimbiya Saudatu.
Ummi da Hibba kuwa miƙewa tsaye sukayi.

Shi kuwa Sheykh gyara zamanshi yayi tare da ɗaura ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya.

Ita kuwa Shatu a hankali ta isa gabanta.
Ido ta zuba mata tare da yi mata kallon tara saura kwata.
Cikin dakkeyar Muryar rashin tsoro tace.
“Toh *Bushiya* mai mugun baya, Bushiya mai bayan ƙayoyi masu kama da allurai, ki buɗe idonki da kyau ki kalleni Ni AYSHA ALIYU GARKUWA ba sa’ar yinki bace uwar mahassadan duniya, in kina cin ƙasa to tabbas ki kiyayi ta curi, ki bar min mijina ya sarara ki far masa rayuwa, ɗan shi ba sa’an yinki bane ki bar min mijina ya huta baya son ihun nan da kikeyi mishi, zan kuma iyan komai dan ganin na kauda dukkan abinda baya so.”
Wani irin daɗi ne ya rufe zuciyar Ummi da Hibba Sheykh kuwa ƙafarshi kawai yake kaɗawa yana mai binta da wani irin kallo mai tarin ma’anoni kalmarta ta *Mijina* yake ji tana sa duk wani hudan gashin jikinsa na amsa amon kalmar yana ratsa jikinshi da zuciyarsa haka yasa bai san sanda wani yalwataccen murmushi ya subce mishiba, tabbas Shatu akwai ƙarfin hali.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu tsuru tai da ido.
Itako Aysha cikin karsashi tace.
“Na lura ke dabbace, sam bakya gane yarukan mgna na bani Adam, kinfi son sai an miki irin yarukanku na dabbobi.
Kina tsaye da farin yawu a bakinki kina zubda jini.
Yayinda wasu ke bayanki da jini a bakinsu suna fidda farin yawu.
Sokuwar rama mai tsami.
Ni nan da kike ganina da idona tar a buɗe na shigo Masarautar Joɗa, kada ki ganni haka Ni ɗan hakine da zaki iya renawa amman tabbas zan tsole idanun magauta ruwanshi ya tsiyaye.
In kin san fullanci to.
*MIN MI KURORI CITTA NFAMƊA NHEYAH* NI “`DAKKEN YAJIN BORKONE INYI KAƊAN IN KUMA ISHI MUTUN“`
Ki tsumayeni tabbas zanyi daka inyi tankaɗe inyi rairaya a masarautar Joɗa!.
Ke ko kallo baki isheni ba domin bata ke akeyi ba da manyan Magauta nakeyi.
Ja mugun bakinki ki fice min a gidana!”.
Rab-Rab.

Jalal da Jamil dake da Jafar shigowa ne, suka tafa mata da hannu bibbiyu.
Hakama Hibba. Ummi kuwa ƙasa tayi da kanta.
Shi kuwa Sheykh ƙanƙance idonsa yayi yana kallonsu yana kaɗa ƙafa ya watsa idanunshi cikin na Gimbiya Saudatu yana mata kallon itama ta isheki.
Aunty Juwairiyya kuma da tun ɗazu tana bakin ƙofar shigowa da sauri ta juya ta koma Side ɗin ta.

Ya Jafar kuwa sai murmushi yake tare da dunƙulawa Shatu hannunshi kamar haka👍🏻

Wani irin juyawa Gimbiya Saudatu tayi tare da jan al’kyabbar ta ta fita.
Har taje bakin ƙofa Shatu tace.
“Ki riƙe kalmar mahaukaciya tabbas zakiga mahaukata a masarautar Joɗa zasu baiyana bila’adadin.”

Daga nan ta juya ta nufi Dinning area ɗin babban falon.

Ita kuwa Gimbiya Saudatu ta juya ta fita.

Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya sauƙe ƙafafunshi kana ya miƙa ya nufi falonshi.
Haka nan yaji murmushi na tsubce mishi.
Tabbas ya gamsu da ƙarfin halin Shatu da rashin tsoronta, sai dai yana jiye mata tuggun mutanen da bata san halinsu ba.
Yana shiga yaci abinci kana ya shiga yayi wonka.
Kana ya ɗauki wayarsa.

Jalal, Jamil, Hibba, Ya Jafar, Shatu kuwa zama sukayi a falon cikin mamaki Ummi tace.
“To wacece yar leƙen asirin Gimbiya Saudatu a wannan sashin?
Ya akayi tasan abinda ya faru da Shatu?
Waya gaya mata?
Bayan in banda muyamu.
Ni Juwairiyya, Hibba, Jalal, Jamil, Jafar. Wanda shi baya mgna, ita kanta Shatu bata san meya faruba batasan ya akayi ba.
To waya fitar da wannan zancen a cikinmu?.”

Cikin gsky da gsky duk suka ce wlh babu wanda suka taɗawa mgnar Hibba harda ƙollarta tace.
“Wlh ita ko Umaymah ma bata gayawa ba”.
To lallai kam akwai buƙatar bincike a tsakanin mu.”
Ummi ta faɗa tana mai cike da al’hinin abin.
Ita kuwa Shatu uhummm. Kawai ta iya cewa tayi shiru bata ce komaiba.

Haka dai suka tashi taron.

Sheykh kuwa, number Umaymah ya kira bayan sun gaisa ne yace.
“Uhumm Umaymah wai me kika sani ne ya faru da wannan yariyar shekaran jiya?”.

Cikin tsoro da son kauda batun Umaymah tace.
“Wacce yarinyar kuma?”.
Fuska ya ɗan tsuke yace.
“Waccar yarinyar dai”.

“To bata da sunane ita”.
Ta kuma ce mishi.

Cikin gajiya da batun yace.
“To ni ba sanin sunanta nayiba, baku gaya min sunanta ba.”
Wani irin murmushi Umaymah tayi tare da cewa.
“Ban gane bafa Jazlaan”.
Hannunshi yasa ya ɗan shafi sajenshi.
Yana mai son yasan meya sameta, meya faru da ita, shiyasa a hankali yace.
“Yarinyar dai da kike cewa ɗiyarki!.”
Kai Umaymah ta jinjina tare da cewa.
“Laah ni nama mance bamuyi mgnarba, ran sallane tayi aiki ta gaji tunda safe bataci komaiba to ashe tanada olsa shine fa, ta shiga ɗakinka zatayi maka shara ta faɗi ta suma, da kyar aka samu ta farfaɗo suanta kuma Aysha”.
Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
“Shirme in banda sakarci da raki mutun ya bar kansa da yunwa da gajiyan aiki mutun har ya suma”. Ya ƙarashe mgnar yana jinjina darajar sunanta a ranshi.
Cikin jin daɗin bai tsananta bincike ba tace.
“Akwai wani abune?”.
Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“Wannan mahaukaciyar Gimbiya Saudatunce tazo take cewa wai taji lbrin ta haukace”.
Daga nan ya kauda zancen.
A hankali ya miƙe yana riƙe da wayar a kunne shi.
Dinning area ya nufa.
Murmushi yayi gano tabbas akwai abinda Umaymah ke ɓoye mishi.
Hannunshi yasa cikin zirin zirin igiyoyi masu duwatsu masu daraja sheƙin Daimond da sukayi Dinning area ɗinshi a madadin labule.
A hankali yasa hannunshin kan na’urar CCTV camera dake liƙe a gefen inda yake ajiye key, wanda duk abinda za’ayi a falon zai gani.
Cikin sanyi yace.
“Uhummm Umaymah kiyi mata faɗafa, ta dena hawan ƙawara kan mutanen masarautar Joɗa, ta kiyayi kanta da faɗa da magautana zasu ilatata.
Bata san komaiba a kaina ta tsaya matsayin baƙuwa Umaymah zafa suyi mata illa”.
Ya ƙare mgnar a hankali.
System ɗinshi dake kan Dinning table ɗin ya jawo.
kana yaja kujera ya zauna ya fara haɗa na’urar.
Ita kuwa Umaymah a hankali tace.
“To ya zatayi tunda ƙaddara ta kasantar da ita matsayin matarka, ko ita kurmace dole sai sun nemi yi mata illa sun sabautata.
Dole kasata cikin jerin mutanen da ka zame musu GARKUWA a masarautar Joɗa, tunda ita dai matarka ce, amanarka kuma”.
Shiru yayi yana jinta yana mai kallon fuskar System ɗinshi date ɗin shekaran jiya ya shiga.
ai kuwa Shatu ya fara cin karo da ita tana share falon da goge ko ina.
Sai kuma lokacin da suka shigo ita da Jamil da Hibba suka nufi bedroom ɗin sa.
A hankali yace.
“Uhmmm Umaymah sai anjima zan kiraki”.
To tace kana ya katse kiran.
Ido ya zuwa System ɗinshi.
tsaki yaja karo na forko da yaji da ya haɗa na’urar da cikin ɗakinshi.
Gashi yanzu baya ganinsu sai dai ihun Hibba, da fitowa da tayi da gudu ta kira Ummi da yadda suka shigo da Aunty Juwairiyya.
Kanshi ya gyaɗa lokacin da yaga sun fito a hankali ya rufe System ɗinshi.
Dafe kanshi yayi yana nazari.
Ya dade a nan sosai kana ya koma ɗakin shi.

Da dare misalin karfe sha ɗaya na dare saura.
Shatu ta kalli Hibba dake konce tuni tayi bacci.
Yasa ta miƙa a hankali ta nufi ɗakin Ummi.

A bakin ƙofar ta tsaya a hankali tayi sallama.
Cikin mamaki Ummi dake zaune bisa sallaya ta idar da shafa’i da wutri kenan taji sallamarta.
Juyowa tayi tare da amsawa tace.
“Shatu”.
A hankali tace.
“Na’am Ummi”.
Cikin mamaki tace.
“Lfy kuwa shigo mana”.
A hankali ta shigo tare da cewa.
“Lfy lau Ummi, nazo wurinki ne.”
“To”.
tace tare da nuna mata wurin zama bakin gadonta.

A hankali ta ƙaraso kusa da ita,
Gabanta ta zauna kan sallayan cikin nitsuwa tace.
“Ummi kiyi haƙuri ko zakiyi bacci na hanaki”.
Da sauri ta girgiza mata kai alamar a a.
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa.
“To Alhamdulillah”.
Sai kuma tayi shiru.
A hankali Ummi tace.
“Kina buƙatar wani abune?”.
Cikin nitsuwa tace.
“Uhum Ummi dama tambayarki nake son yi”.
Gyara zama Ummi tayi kana tace.
“Ina jinki”.
Itama zamanta ta gyara a hankali tace.
“Dan Allah Ummi in ba damuwa, dan Allah da Manzonsa ki sanar dani abinda Allah ya sanar dake a kan masarautar Joɗa mana.
Ummi kaina na kullewa da mutanen masarautar Joɗa, ban gane banbanci su da dankantakarsu da kuma. Alaƙarsu ba”.
Wani irin dogon ajiyan zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“To Shatu ai kin gama komai tunda kika haɗani da Allah da Manzonsa.
Kuma dama nace miki ki tambayeni duk abinda baki gane ba, zan gaya miki. To amman akwai wani abun sirrine garesu masarautar in na faɗa kamar cin amarsu ne, wani abun kuma nima kaina ban sanshi ba.
Hannun Ummi ta riƙe tare da zubda hawaye tace.
“Ummi gaya min yadda masarautar Joɗa take ko zan san irin zama da takun da zanyi da mutane da ɗaukar mataki kan abinda ke faruwa”.

A hankali Ummi ta gyara zamanta.
Ta jingina da jikin gado.
Kana itama Shatu ta gyara zamanta ya zama suna fuskantar juna da kyau.
Cikin sanyi Ummi ta fara bata lbrin.

*Masarautar Joɗa*
tsohuwar masarautace.
wacce tun kafin zuwan Shehu Usmanu Ɗanfodiyo ƙasashen Afrika tana kafe da ƙafanta.
Kuma masarautar Fulɓe ce tun a wancan lokacin.

Lokacin da Shehu Usman Ɗanfodiyi ya iso nan ƙasashen hausa ya basu musulunci ya kafa tutocinsa tako ina tako wacce masarauta.
A lokacin Masarautar Joɗa sunanta masarautar Fulɓe.

Kuma lokacin Sarki Sule ne a kan karagar mulki. Baban Joɗa kenan wanda yake shi Joɗa shine kakan sarkinmu na yanzu wato Lamiɗo.

A lokacin sarki Sule yanada ƙarfin mulki yana da mata huɗu ƙwar-ƙwara biyar.
Allah ya azurtashi da arzikin yara a ƙalla sunfi hamsin a cikin matansa huɗu na aure.
Akwai wata ɗaya da ake kira Gimbiya sumaye ƴar sarkin kal’anace.

Gimbiya Sumaye inrin matannane da Allah ke jarabta da haihuwar wabi.
Bima’ana tana haihuwa kuma yaran na rasuwa.
A haka har ta haifi yara kusa goma kuma bata da rayeyye ko ɗaya.
Cikin ƙwar-ƙwaran sarki Sule ne ɗaya ta ɗauki ɗanta na miji ta bata halak malak kwanan yaron uku a hannunta ya rasu.
Wata cikinsu ta kuma bata still shima kwananshi uku ya rasu.
A haka duk ƙwar-ƙwaran sarki Sule saida suka bata yara suna rasuwa.
Daga nan uwar gidan Sarki Sule wacce take babarbariya ce.
Tasa mata suna cikin wasa na tsakanin Fulani da bare-bari amman a zahiri da gaske takeyi.
Gsky mai tafiya da wasa kenan.
Sai ta sawa Gimbiya Sumaye suna da fillanci wai
*Ɓadamaya* ma’ana wai duk wanda ya matso kusa da ita zai mutu, ko wanda ya bata riƙon ɗa kowa kwana uku ne mutuwa zaiyi.
Kamar da wasa sunanta ya zama Gimbiya Ɓadamaya.
Mutanen masarautar akayi ta mata izgili da habaici.
Takan zauna tayi ta kuka.
babu mai rarrashi dan ita masarautarsu nada nisa a lokacin kuma babu ko Radio bare waya.

Anan Allah ya bata wani ciki ta haifi ɗan ta namiji.
Akasa mishi suna Umar faruq.
Sai Gimbiya Sumaye take kiranshi da Joɗa ma’anar Joɗa shine zauna.
Da haka sai aka maida abun ba’a aka rinƙa kiran yaro da Joɗa.
Allah cikin ikonsa ta yaye yaro lfy lau.
Ta kuma haihuwa na goma sha biyu.
Yariyar watanta biyar ta rasu, sai aka rinƙa mata dariya ana cewa saura *Joɗa* shima ya *Dilli.*
Wato wai saura Joɗa shima ya *tafi.*
Cikin ikon Allah kuwa ya raya Joɗa ya girma.
Ya zama shine ƙarami cikin ƴaƴan sarki Sule kenan.

Bayan wasu shekaru, sai Sarki Sule yace to shi zaiyi murabus, a cikin yayanshi yace zai naɗa babban ɗanshi Madu.
Ɗan Gimbiya Falmata.
Sai ko sauran ƴan uba duk suka tashi akece to sai ayi zaɓen manyan.

To akwai ɗan Madu wanda yake mai ilimin addini dana zamani sunanshi Bala, sai ya shiga cikin masu neman mulkin ya kafa hujja da cewa.
“Babanshi Madu jahiline dan haka a bashi shine ya dace da mulkar garin.
Haka kuwa akayi aka ba Bala mulkin masarautar Fulɓe.
Dole babanshi Madu wanda shine Magajin gari ya ƙaura ya bar garin.
Tunda kinga bazai yiwuba ace yana mahaifinshi ya rinƙa serving ɗan shiba da baƙinsa ba.

Haka dai Bala yayi mulki tsawon shekaru arba’in inda Joɗa kuma yake matsayin Galadima tunda ɗan tsohon sarki ne.
To shi kuma Sarki Bala sai Allah ya azirtashi da tarin ya’ya mata ɗan shi na miji daya ne,
Sadik.
Ya bawa Sadik sarautan Sardaun.
Bayan wani lokacin sai tsoro ke rufe Sarki Bala kada fa abinda ya samu babanshi ya sameshi.
Wato kar ɗanshi bai gaji mulkiba kamar yadda sarautar ta tsallake babanshi ta dawo kanshi.
To shinefa ya tura ɗan shi Sadik wuraren sauran sarakunan ƙasar, cewa zaiyi murabus zai bawa Sadik mulkin.
To dama bisa ƙaida dole sai sarakunan sun yarda.
Cikin Sa’a kuwa duk sarakunan suka yarda sukasa hatimin amincewa a takardun.
To a kan hanyar dawowanshi ne kuma Allah yayi mishi rasuwa.
Wannan abu yayi masifar tada hankalin Sarki Bala.
Da mahaifiyarsa Gimbiya Salame, da kakarsa Gimbiya Falmata.
Saboda wannan pain ɗin mutuwar ɗan nasa, shene ya tattara yaranshi mata kab ya Aurar dasu.
Harda ƴar shekara takwas duk ya kwashesu ya aurar.
Sabida wai baya son ya mutu baiga aurensu ba.
Ya musu aure ya kuma basu sarauta.
Suka zama hakimai.”

Cikin sanyi Shatu tace.
“Tirƙashi duk wannan don son mulki ne?”.

Kai Ummi ta jinjina tare da cewa.
“Uhum ai akan sarauta babu abinda ba’ayi sabida matsalar sai kowa yace shi ɗan sarkine zai gada.
Sabida in basu gadaba sarautar tabar hannunsu, Shatu Sarauta masiface a zuciyar masoyansa da zasu iya komai a kanta.”
Kai Shatu ta gyaɗa tare da cewa.
“To Ummi ina jinki”.
Gyara zama tayi tare daci gaba da cewa.
“To in takai ce miki a ƙarshe dai Joɗa shiya zama sarki wanda shine ɗan ƙaramin a ahlin Sule.

A lokacin ne kuma sunan jihar nan ya dawo Ɓadawaya sabida.
Nunawa duniya ba haka bane duniya Allah zai iya baka zai iya hanaka.
Masarautar Fulɓe kuma ta zama masarautar *JOƊA.*
Sabida sunan sarkin kenan.
Kuna ya zama adalin sarki mai son baƙi duk inda baƙo yazo zai wuce.
Sai Sarki Joɗa ya bashi wurin zama yace mushi Joɗa wato zauna ga wurin zama kayi kasuwanci kayi kiwo ki ciya ka ciyar kasha ka shayar.”
Shiyasa Jihar Ɓadamaya tayi zarra da tarin ƙabilu sabida son baƙi da basu muhallin zama a wancan lokacin kawai fili za’a yanka a baka ka zauna in Kai baƙone

To babban ɗan Joɗa shine Bubayero wato kakan Lamiɗo.
Bayan Joɗa ya rasune Bubayero ya hau kan karagar mulki masarautar Joɗa.
Ahlin Gimbiya Falmata kuma suna yaɗuwa suma buri da kwaɗayin sarauta na jiƙa a ransu duk burinsu suga yadda sarauta zata dawo ɗakinsu.
To koda Bubayero zaiyi murabus ya bawa ɗansa Nuruddeen mulki sai ya aurawa ɗansa yar bappan shi jikar Madu ɗanshi.
Sukayi aure aka naɗa Sarki Nuruddeen da matarsa yakura.
Bayan anyi aurene da shekara biyu.
Ya auro wata ƴar masarautar su Gimbiya Sumaye.
To itace tazo ta haifi Lamiɗo.
Ita waccar bata taɓa haihuwa ba.
To shima Lamiɗo sai ya auro yar masarautarsun Gimbiya Sumaye, wato Gimbiya Aminatu a matsayin matarsa ta biyu.
To Galadima da kike gani yanzu bappan Lamiɗo ne ɗan autan su marigayi sarki Nuruddeen.

To shi kuma Lamiɗo da aka bashi mulki sai aka aura mishi yar zuriyar Gimbiya Falmata itace uwar gida.
Ta haifi Baba Basiru da Baba Nasiru da kuma Baba Kamal da kuma babban yayansu Marigayi Auwalu. Sai Dr Aliyu shi kuwa mamanshi daban itama ta rasu su biyu ta haifa da Gimbiya Surayyah.

To Mamansu Baba Nasiru.
Yanzu haka tana raye amman ta haukace babu mai shiga Side ɗinta, sai Lamiɗo da yaranta. Duk wanda yaje sai tace zatayi duka, ita da bakinta take bayanin Abbansu Sheykh da Gimbiya Aminatu da Gimbiya Aisha tayiwa asiri ya dawo kanta.

Galadima da yaga ya tsufane kuma baida ɗa namiji da zai gajeshi shine.
Yacewa Lamiɗo ya naɗan babban ɗan shi Auwalu mijin Gimbiya Saudatu a matsayin Galadima.

To bayan ya naɗa shi da shekara biyu ne, ya rasu.
To sai ya naɗa Ya Jafar ɗin nan da kike gani a matsayin Galadiman Masarautar Joɗa.
Lokacin lafiyarsa lau yadda kikaga Sheykh haka yake da ibada addini ilimi nitsuwa tausayi.

Kwananshi goma a kan mulkin washe gari za’a naɗa shi ne, ya dawo haka babu mgna sabida wani babban ibtila’i da tashin hankalin ɗaya samemu.
Kuma a lokacin an kusa amishi aure sabida sarautar da za’a bashi.
To wannan shine babban mafarin hargitsi da kitimurmurar dake masarautar Joɗa a yanzu.
Dan ranar da Jafar ya zama haka akwai babbar masifar data fi wannan muni daya faru a masarautar Joɗa.
Shine abunda yayi masifar girgiza mutane.

Lokacin Sheykh yana saudia yana karatu a jami’atul Madina.
Hankalin Hajia Mama yayi masifar tashi tayi ta suma tana sakewa Umaymah kuwa da Sitti mutuwace kawai da basuyi ba, dan baƙin ciki da tashin hankalin ɗaya samemu.

To kuma tun daga nan sai duk magautan suka dena kiyayyarsu kansu Jafar da ƙannensa.
Koda Jabeer yayi karatunshi a can yayi digirinsa na biyu da PHD dinsa duk a can.
Wani sabon tashin hankalin da Jabeer ya dawo Lamiɗo yabashi mulkin GARKUWAn FULANI, nanfa Magauta sukace zasu mutu.
Dan ma mulkin na gefen yaya mata aka bashi shine abin ya ɗanyi sanyi.
To kuma ingiza gabar sunga ɗawisun masarautar Joɗa tayiwa Jabeer abinda sai sarki takeyiwa.

To kinji lbrin a taƙaice sai a hankali zaki gane komai in kina bin komai a hankali.”
Numfashi mai sanyi Shatu ta sauƙe tare da cewa.
“Ummi wacece Gimbiya Aisha?”.
Da sauri Ummi tace.
“Baki santaba”.
Da sauri Shatu tace.
“Toh ina take?”.
“Bata nan”. Ummi ta bata amsa a gajarce.
Da sauri Shatu tace.
“Ta rasu ne?”.
Cikin zubda hawaye Ummi tace.
“Bamu san halin da take cikiba shine babban burin Sheykh a duniya, sanin inda take”.
Cikin sanyi Shatu ta kauda waccar tambayar dan ko Ummi bata amsa mataba ita ta gane matsayin Gimbiya Aisha. Haka yasa a hankali tace.
“Allah ya baiyana ta. Ya cika mishi burinsa.”
Amin Amin Ummi tace tana sharce hawaye.
Cikin nitsuwa Shatu tace.
“To Ummi mene kuma banbancin mulkin gefen yaya mata dana maza”.

Cikin jin bacci tace.
“Da safe ki tambayi Hibba ko Jamil zasu gaya miki, yanzu jeki shiga dare yayi bacci nakeji”.
Da haka tatashi taje ta shiga ta fahimci a duddunƙule Ummi ta bata lbrin Sarkin yanzu da matsalar dake faruwa.

Washe gari da safe, bayan sunci abinci.
Ummi ta miƙe dan taje tayi walaha, Hibba kuma ta tafi sashin Juwairiyya da tun jiya da safe bata sake shigowa ba.
Jamil ne ya shigo neman Jalal da sauri tace.
“Uhum yauwa Jamil zo mana”.
To yace kana ya dawo ya zauna.
Cikin nitsuwa tace.
“Dan Allah in ɗan tambayeka mana”.
Jingina yayi da jikin kujera tare da cewa.
“To ba matsala Allah yasa na sani”.
Wayarta ta ajiye kana tace.
“In sha Allah ka sanima.
Wai menene banbanci sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata, dana gefen ƴaƴan ƴaƴa maza”.

Dariya yayi mai sauti tare da cewa.
“Uhumm kema kin shiga Masarautar Joɗa cikin kitimurmuran yanayi ko kin ratso cikin ahlin da ba’a sonmu, kin fara fuskantar ƙalubale ko”.

Tashi yayi yaje ya sha ruwa kana ya dawo ya zauna ya fuskanceta da kyau a hankali yace.
“Banbancin tsakanin sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa maza da gefen ƴaƴan ƴaƴa mata.
Shine kamar haka.
1 Galadima (must be a prince )
2 Chiroma (crown prince)first born to the king
3 Tafida ( most be a prince )
4 Santuraki (must be a prince )
5 Sarkin dawaki ( prince)
6 Ɗan buram
7 Ɗan isa
8 Ɗan lawan
9 Durbi
10 Wambai
11 Turaki
12 Ɗan maje
13 Yarima
14 Ɗan iya
15 Majidadi.
Dan ɗagowa yayi ya kalleta tare da saƙe yatsunshi da yake naɗewa yana irga mata yace.
“Wannan duk royal family ne mostly biological sons din sarki ne wasu kuma jikokin sarki kuma kunne biyu sukeyi a rawunansu sabida su ƴaƴan sarki ne ko kuma iyayensu ƴaƴan sarki ne.
Kanta ta jinjina mishi alamun ta gamsu tana kuma ganewa.
Shi kuwa a nitse yaci ga da ce mata.
“Anan ake samin chief of staff da kuma senior councillor kamar galadima mostly shine senior councillor shine elders in royal bloodline ana samun galadima yapi sarki a shekaru kuma shi ake bama riqon gari in sarki bayanan.

Sannan duka anan sunayen dana irga miki da fari kowa zai iya yin sarki tunda daga ɗan sarki sai jikokinsa na gegen ƴaƴa maza, shiyasa su kunne biyu sukeyi a rawanunsu.

A hankali ya kalli Ummi data fito da Hijabi a jikinta ta zauna kusa da Shatu.
Tare da cewa.
“To kinji bayanin ƴaƴan ƴaƴa maza na sarki.”
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Na gane kuwa Ummi, yanzu gaya min na ƴaƴan yaran sarki mata kuma inji”.

Gyara zama Jamil yayi tare da cewa.
“To sukuma sarautar gefen yaya mata sune.

1 Madawaki
2 Garkuwa
3 Makama
4 Majidadi
4 Waziri
5 Matawalle
6 Sarkin yaki
7 Magayaki
8 Jarma
9 Talba
10 Shatima
11 Ubandoma
12 Ɗan kadai
13 Magajin gari
14 Ɗan masani
15 Barma.
Ɗan sauƙe numfashi yayi tare da ci gaba da cewa.
All of these hakimai ne wanda sukeyin kunne daya a rawunansu.
Kuma wasu a cikinsu jikokin sarki ne ta bangaren mamansu, mum dinsu ce yar sarki kamar dai mu a Masarautar su Sitti ko za’a bamu mulki iya waɗannan za’a bamu kinga baza suyi kunne biyu ba shiyasa suke kunne daya amma suma hakimai ne manya kuma yan majalissar sarki also akwai kin makers a cikinsu.
Sai dai su cikin jerinsu babu wanda zai gaji sarautar sarki kamar dai mu yanzu bazamu gaji Jadda ba da masarautar gargajiyace sai dai da yake nasu na musulcine, in Kuma a masarautar Joɗa ne sunayen da na ƙirga miki na forko cikinsu za’a iya bamu, domin yanzu GARKUWA da aka bawa Hamma Jabeer matsayinsa yafi ƙarfin hakan shiyasa Magauta basu damuba.”

Ya ƙarishe mgnar da cewa kin gane ko Aunty Shatu,
Kinga shiyasa da aka bawa Ya Jafar Galadima cikin kwana goma aka sabauta manashi.
Ana tsoron kada tarihin Sarki Bala da mahaifinshi Madu ɗan Sarki Sule ya maimaita kanshi a kan ƴaƴan ɗakinmu.
Shiyasa da aka bawa Hamma Jabeer Garkuwa mu bamu soba.
To sauƙin abin ma ɗaya ne da suga sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata aka bashi duk da shi jikan ɗan ɗan ɗansa namiji ne”.

Ajiyan numfashin tayi kana a hankali tasa hannunta ta tallaɓe habarta, cikin alamun nisan zango na tunani da nazari.

A hankali Ummi ta matso kusa da ita cikin sanyi da kuma yin ƙasa da murya tace.
“Shatu ni kuma in tambayeki wani abu mana”.
Kanta ta jujjuya a hankali ta buɗe baki tace.
“Na sani! Ummi nasan abinda zaki tambayeni! Zakimin tambaya ne kan menene yasa da na shiga ɗakin Yah Sheykh na suma na fita haiyacina, ko?”.
Ta ƙarishe mgnar wasu hawaye masu ɗumi suna kwaranyo mata a fuskarta.
Cikin sanyin jiki ganin Ummi ta gyaɗa mata kai alamar eh.
Jamil ma jiki a mace ya zuba mata ido.
Tafin hannunta tasa ta sharce hawayenta murya na rawa alamun tana son danne kukanta tace.
“Ummi ɗakin Yan Sheykh ɗakine mai cike da hatsara a rayuwarshi.
Tabbas dan Allah yayi shi mutun ne mai ibada da imani da kekyawar zuciya, da yawan ambaton sunan Allah da zama da al’wala wlh da badan wannan nagartar da Addu’o’in da suka zame mishi abokan rayuwa suka zame mishi GARKUWA ba, kamar yadda Manzon Allah yace.
“Addu’a’u saiful muminin da tuni sun kasheshi sun sabauta rayuwarshi.
Ummi ban san komai ba kan masarautar Joɗa.
Amman dan al’farma Annabi da darajar Umaymah.
Zan taimaki Yah Sheykh iyakar iyawata.
Zan taimake shi akan abinda Allah ya bani ikon gani”.
A hankali Jamil ya zamo ya zauna a ƙasa.
Yana mai jin tsikar jikinshi na tashi.
Itama Ummi zamowa tayi ta zauna ƙasa.
Hakama Shatu a hankali ta zauna gaban Ummi hannunta tasa.
Ta kamo hannun Ummi cikin muryar kuka tace.
“Ummi ku yarda dani, ku bani haɗin kai, zan tone duk abun cutarwa dake ɗakin Yah Sheykh. Bazan cutar dashi ba, zan taimake shi kamar yadda Bappa na yake bani umarni duk sanda mukayi mgn dashi.
Ummi keda Jamil ina buƙatar taimakon ku.
Amman kafin nan ki gayawa Umaymah in ta amince,
sai inyi aikin amman kada a gayawa Yah Sheykh dan bazai yarda ba.”
Cikin tsoro ido cike da hawaye Ummi tace.
“To Shatu me zancewa Umaymah, me kika gani a ɗakin har ya firgitaki yasaki suma?”.
Cikin kuka tace.
“Ummi kada ku tsaya bincike a kaina.
Ni dai ku yarda dani bazan cutar da kowaba na cikin Masarautar Joɗa sai wanda ya cutar da kanshi Ummi bamu da sauran lokaci mai tsawo fa, komai zai iya faruwa da Yah Sheykh”.
Cikin tsoro da firgici Jamil yace.
“Ba matsala mun yarda dake, ni yanzu taimakon me zan miki?”.
Cikin sauri ta share hawayenta tare da juyowa ta kalli shi kana tace.
“Yauwa Jamilu zaka samo mana mai saka tayis, yazo da katon ɗaya na tayis ɗin irin na bedroom ɗin Yah Sheykh sak da sak.

Sai kuma kayi ƙoƙarin mu samu ya Sheykh in ya fita ya wuni sai dare zai dawo”.
Cikin sauri yace.
“Tayis da mai sawa ba matsala, batun in ya fita sai dare ya dawo kuma inaga.
Sai zuwa jibi ranar ne zaije asibitin gwamnatin Genaral Hospital.
To in yaje can wuni yakeyi wani lokacin sai dare zai dawo”.
Cikin gamsuwa da hakan tace.
“To ba matsala.
Ummi ke kuma ki kira mana Umaymah ki sanar mata, muyi abun da saninta.”

To Ummi tace kana a wurin ta kira Umaymah tayi mata bayani.
Ba wani neman ba’asi tace.
“A barta Ummin Jabeer na amince, tayi duk abinda ya dace a kan mijinta da yayanshi da ƙannenshi dama duk wani abu nashi”.

Cikin jin daɗi ta jinjina kai lokacin da take jin mgnar Umaymah.

Wani irin dogon numfashi taja mai ƙarfi sai gata ta tafi luuuh kan…!

 

Wasa farin girki? Shatu kadafa allura ta tono garma.

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button