Daurin Boye Hausa NovelHausa Novels

Daurin Boye 14

Sponsored Links

14

 

Tun basu shiga bangaren nasu ba ta saki hannunta tana dubanta
“Gata nayi miki fa….ruwanki kibar batun a haka ruwanki ki warware,amma ina tabbatar miki koda kin warware kece a ciki” tana gama fadar haka tayi gaba abinta ta barta a tsaye a wajen tana qoqarin gayawa kanta abinda ke faruwa,sam ta kasa tabuka koma

Related Articles

Wai meye haka ke shirin faruwa da rayuwarta?,ya ilahi wanne laifi ta yiwa asma’u haka?.

????????????????

Tun yana toilet yana brush yake jiyo sautin qarar wayarshi,mutum daya ce ke kiransa ta layi asma’u,cire wayar yayi daga chargy ya koma saman sofa ya zauna sannan yabi kiran,plashing ya mata kamar yadda ya saba sannan ya aje wayar gefanshi yana ci gaba da tura saqonnin da suka hanashi kowamawa bacci bayan sallar asuba ta cikin system dinsa,ba’a rufa minti guda ba cikakke ta biyo kiran.

“Yallabiya kin tashi lafiya”
“Lafiya yaron oga”ta amsa kaman yadda ta saba masa,duk da yau akwai sakewa sosai cikin muryarta babu cunkushewa
“Yasu daddy?”
“Shi yakeson ganinka ma” sam bai tsammaci jin maganar ba daga bakinta
“Allah yasa ba laifi nayi ba” ya furta yana maida wayar handsfree ya ajeta kusa da system din nashi yana ci gaba da aikinsa
“Lafiya qalau….zaka sameshi da daddare ne bayan sallar isha’i”
“To Allah ya kaimu” bata amsa ba ta katse kiran kawai.

Aikinsa yaci gaba da yi jifa jifa yana tambayar kansa dalilin kiran,sai ya tsaida aikin nashi ya lalubi wayarsa yana neman wata lamba,bugu hudu aka daga bayan sun gaisa ya bada sautun kayan gwanjo riga da wando da takalmi mai sauqin kudi,a ladabce ya amsa masa sukayi sallama,ya sauka ya masa transfer din kudin daya gaya masa.

Knocking din qofarshi aka soma yi,da fari yayi shuru yana zaton zeenart ko amal ne,daga bisani ya fara jiyo tashin muryar al’amin
“Boss….kar kace min bacci kake har yanzu” miqewa yayi ya isa bakin qofar ya bude al’amin ya biyo bayanshi
“Tun asuba nake zaune aikin nan nakeson qarasawa….kawai nayi zaton cikin yaran can ne banason takura” ya qarasa fada yana miqawa al’amin din hannu suka cafke
“Mtsweew…..yara na binka komai yaji,zuqa zuqa da su amma kana musu haka….i swear da nine hadasu zanyi na auresu” harara khalipha ya watsa masa sannan yace
“Allah ya sawwaqe…an gaya maka kowa ma na mamajo ne irinka” dariya al’amin ya saki bayan ya gama hada coffe ya dawo gefan gadon khaliphan ya zauna suna facing juna
“Ba zancan na mamajo….dama ce Allah ya baka ba sai ka dama ba”
“To basuyimin ba….kai ba wannan ba…..na samu kira fa”
“Kai boss….duwatsun sun samu kenan?”
“Ba maganar wannan kamfanin ba….asma’u dazu ta kirani babanta yana son ganina,ina tsammanin na cimma gaci fa” kai al’amin yake kadawa yana dariya
“Kai mutumi na…zanso ganin qarshen wannan game din”
“Tare zamuje ka shirya anjima….but karka sakamin manyan kaya ina fata ka gane”
“Kana nufin….har baban nata a haka zamu je masa?”
“Qwarai kuwa…inason in samu ‘yar gidan dattawa ne wadanda mutunci da addini suke duba ba dukiya ba” ya furta yana miqe qafafunshi saman center din dake gabanshi bayan ya ture system din gefe guda
“Yes!,Allah ya nuna mana anjima” daga nan suka fada batun harkokin kasuwancinsu.

????????????????

Tunda suka taho a mota al’amin ke kallonshi yana diban dariya,kayan gwanjonsa abinsa sunsha wanki da guga,duk da araharsu da suka nuna amma basu kasa yi masa kyau ba,sun fito da ainihin xatinsa
“Ango….ango” al’amin kawai ke fada,shima dariyar yake yana cewa
“Ka fadi da kyau….ban taba zaton yarinyar zata ci wannan gwajin ba al’amin”
“Eh….ai ba daga nan take ba”

Kusan a qalla sun kusa mintina goma tsaye bakin gate mai gadi ya hanasu shigowa,suna tsaye daddy ya dawo daga masallaci sallar isha’i,yana shirin wucewa ya lura da su saidai bai zaci gidan suka zo ba,zai shige mai gadi ya masa bayani ya bashi umarnin ya shigo da su falon baqi.

Dukansu shida al’amin din na zaune saman carfet din suna dakon shigowar daddy,sallamarshi ita ta sanya khalipha sake gyata zamanshi tare da duqar da kanshi qasa har daddy ya qaraso,cikin girmamawa suka soma gaidashi kan khalipha a qasa
“A’ah….ku taso muyi musabaha ai tafi lada ko” al’amin shi ya soma zuwa sannan khalipha,sai a sannan ya dubi daddy
“Alhaji!” Khalipha ya furta cikin tsantsar mamaki tare da maida hannunshi da yake niyyar miqawa daddyn
“Alhaji dama kana nan?”
“Muhammadu…kaine?” Daddy shima ya furta cikin fara’a yana mamaki,gaisuwa ta musamman sukayi kowanne fuskarsa qunshe da fara’a kafin khalipha yace
“Na jima alhaji ina nemanka,har na gaji na haqura”
“Allah sarki muhammadu…ya bayan saduwa?,ya jikin maman naka?”
“Anni tana nan lafiya alhaji,tana raye tana kuma cikin qoshin lafiya sanadiyyar taimakonka”
“Ma sha Allah…ma sha Allah…naji dadi qwarai….kaine ko abokinka ke neman auren diya ta?” Kunya ta saka khalipha duqar da kanshi yana murmushi,al’amin ya fansheshi
“Shine alhaji” ya fada cikin sigar zolaya yana dariya,shima daddyn dariyar ya danyi,a zahiri yaji dadi sosai,koba komai yasan aysha zata shiga hannu na gari,yasan khalipha tun kafin ya kai haka,sanin farko daya masa a rayuwarshi nagartarsa da kyakkyawar halayyarsa ita ya soma gani tattare da shi”
“Ma sha Allah….ma sha Allah,lallai aysha indo ta dace….ta dace da miji da yayi dai dai da irin halayyarta” a hankali ya daga kai suka hada idanu da al’amin cikin mamaki,yana son yaga ko shi kadai yaji daddy yace aysha indo,kamar ko daddyn yasan tantamar da yakeyi sai yace
“Khalipha…ga indo nan na baka don bani da wani sauran neman shaida game da halayenka,ni kadai na ishi kaina shaida,ka dauka amana na baka saboda haka ka riqeta amana,Allah yasa albarka a rayuwarku….banason wasu dogayen bidi’o’i,magabanta kawai nakeso ka turomin”
“Madalla daddy…mun gode Allah ya saka da alkhairi” al’amin ya fada ganin khaliphan ya kasa cewa komai
“Shikenan khalipha…..sauran hira sai komai ya kammala mun samu zama sosai ni da kai ko?,amma ina fata zuwa yanzu kana da sana’ar da zaka iya riqe aysha”
“Alhamdulillah…Allah ya kawo duk wani wani rufin asiri cikin taimakonsa”cewar khalipha wanda qwaqwalwarsa tayi nauyi saboda tunanin daya cuno kai ya cunkusheta lokaci guda kamar qiftawar walqiya,tambayoyi fal kansa
“to ma sha Allah..masha Allah”da taimakon al’amin sukaiwa daddy sallama,suka rabu cikin karamci da mutunci yana tsokanarsa bazai tsaya yaga ayshan tasa ba ko kunyarsa yake ji,shidai yaqe kawai yake kusan al’amin shi ya karbi ragamar tafi da komai.

A sanda suke takawa zasu fice daga harabar gidan lokacin asma’u da nata gwanin hamid ke shigowa cikin gidan,shima yazo ne don amsa kiran daddy,dauke kanta tayi tamkar bata taba sanin wani mai kama da khalipha,da yake hakan kusan halayyarta ce sai ta karbeta,hakan ya sanyawa khalipha yaji har cikin ranshi cewa akwai wata a qasa,yana kuma buqatar qarin bayani,shin wace aysha?,wace ayshan da ake cewa an bashi ita,a ina take?,ya take?,ita din ta sanshi?,ko kuma itace tace tana sonshi,ko duka ma ba haka bane asma’u ce mai suna biyu?,kusan wadan nan sune maganganun da yake gayawa al’amin sanda suke cikin mota a hanyarsu ta komawa gida
” khalipha….inaga wannan al’amarin fa sam bazaiyuwu ba,tayaya zaka iya kunce DAURIN BOYE?,ka koma ka yiwa dattijon nan bayanin bakasan kan wace aysha yake magana ba kai asma’u kake neman aure”
“Al’amin kafin komai ina buqatar jin ta bakin asma’u”
“Eh hakan nada kyau” hannunsa ya saka cikin aljihun kayanshi ya zaro vivo dinsa ya soma neman layin asma’u,dai dai lokacin da take kitchen ta tasa aysha a gaba tana hadawa hamid kayan motsa baki,kallo daya zaka mata ka karanci ramar data qara bayan wadda take da ita,maganar nata cinta zuciya da ruhi saidai bata da wanda zata gayawa damuwarta,bata da abokin shawara bata sa abokin magana,bata da wanda zata gayawa matsalarta sai ita kadai a karan kanta,ba wanda ya damu da ita,ba wanda ya damu da rayuwarta,aliya ce bata nan ta mata nisa,nisan da batasan ranar dawowarta ba,bata samunta ko a waya,tunda suka kammala jarrabawa tayi sallama da ita ta wuce nijer can wajen dangin mahaifiyarta,ta sanar mata idan taje ta sayi layi zata kirata,saidai har yau shiru bata kira tan ba.

Tana ganin khalipha ne ta daga wayar ta kara a kunnenta tana dariya gami da cewa
“Yaron oga how far?”
“Asma’u…ban fahimci dukan abinda ke faruwa ba” ya fada cikin muryarsa da yau daya taji ta sauya mata,
“Ohk…kana buqatar qarin bayani kenan?”
“Haka nake son nace miki” ya maimaita cikin amon data ji ya mata kwarjini
“Ba wani abu bane,mata nayi maka”
“Ni na gaya miki ina da buqatar hakan?” Ya fada cikin zafin da ya fara bayyana har cikin muryarsa,hakan ya karya lagonta,ya kuma rage kaifin tsiwarta
“Karka damu fa….yar uwata ce” ta fadi tana duban aysha gami da tabe baki
“Koma wace bana so….sannan ki tanadi abinda zaki gayawa mahaifinki a yammacin gobe idan na sanar masa cewa bansan da maganar ba,saboda haka….get ready” ya kashe wayar yana jin zafinta irin zafin da bai taba jin irinsa ba daga gareta
“Man…ka shirya kawai gobe ka koma ka gaya masa komai…fine an wuce wajen” shuru khalipha yayi ranshi na dada baci,batasan wayeshi ba,dama da siffar daya zo mata da ita yasa ta rainashi tayi zaton wani gaula ne,batasan waye khalipha na asalin ba ba wannan fake khalipha ba,tana zaton ita din wata abace ko wata tsiyar ce ita,amma yaci alwashin gobe zai nuna mata real muhammad khalipha.

Tsaki tayi tana yatsina bayan ta kashe wayartata,bata jin komai hakanan bata jin ta aikata ba dai dai ba ko sau daya,bata saurari aysha ba ta kira daya daga cikin ma’aikatan gidan ta daukar mata kayan don tuni ayshan ta fice sanda take amsa wayar.

Da maganar ya kwana ya tashi,saidai a safiyar ranar tafiya ta sameshi wanda babbar qaruwa ce sa samuwa a gareshi da kamfaninsu baki daya,a qalla tafiyar zata daukeshi tsahon satittika biyu zuwa uku,hakanan ya shirya ya tafi ba tare daya samu isa zuwa ga daddy ba.

Cikin kwanakin gaba daya zaman gidan taji ya fice mata a kai,sam bata jin dadinsa duk da a baya ma ba dadin take ji ba,saidai abun ya sake sauya salo,a wancan lokacin idan zasu hadu da asma’u idan taga dama ta mata kallon banza,idan bata ga dama bama bata kallon nata,sai bada umarni ko hani,amma a yanzun da wuya su hadu bata bita da dariya ba,dariyar da batasan meye musabbabin yinta ba,yanayin yadda take jin gidan ya sanyata shirya kayanta ta nufi takai,a hakan tana zaton zata samu dan sassauci komai qanqantarsa,duk da tasan cewa yaudarar kanta kawai takeyi,hakan ce kuwa ta kasance,a can dinma ba wanda ya damu da tambayarta meye damuwarta ko meye matsalarra,hatta da karatunta data gaya musu ta kammala bata samu wani daga cikin gidansu mahaifinta ko na mahaifiyarta daya tayata murna ba koda na washe haqora ne idan ka dauke qawarta guda daya tak mero,qwarai tayi qoqarin yakice damuwar dake ranta saidai hakan ya faskara,wannan itace damuwa ta farko data jita da girma cikin ranta baya data mahaifiyarta tun bayan data fice saga qangin rayuwar data taba tsintar kanta,sati biyi cur data diba cikin garin tana fama da damuwarta ita kadai,daga qarshe ta tuqe gaban mero ta sanar mata da komai tare da neman shawararta.

Qwarai ran mero ya baci sosai,fada ta dinga tana jin inama itace,shawara ta qarshe da take ganin itace taje ta yiwa daddy bayani kai tsaye,ta amsa mata ne kawai don bata jin tana da qwarin gwiwar zuwa ta fuskanci daddy da maganar,tana tsodon dukan tambayoyi da bacin ran da zai biyo baya cikin gidan,ta sani sarai bacin rai kowa za fuskanta ba qarami ba,yana da sauqin kai saidai fushinsa baida dadi,baya kuma tafiya cikin sauqi.

Sati hudu tayi ta tattara ta dawo gida ba tare data samu wani sauyi ko ci gaba na yanayin da take ciki ba.

Daren data dawo mummy tayi kiranta
“Aisha…gobe da wuri nakeso ki tashi zamuyi baqi kaman sha daya na safe,a hada musu breakfast da dan sauran abun tabawa,duka kayan snacks na gidan nan sun qare tun tafiyarki,su lantana ba iyawa sukai ba haka freezer din ke zaune babu komai ciki….amma dai a soma wannan din daga baya kyayi na gidan baki daya”
“Toh” kawai tace ta miqe ta fice,tana mamakin yadda ko a fuska bata ga alamun mummy tasan meke faruwa ba,hutunta ba damuwarta bane bare tace ta huta tunda a yau yau din ta dawo daga tafiya,baqinta na gobe sune kawai damuwarta,zata iga ba zata iya ba,yata baro qauyen duka ba’a gabanta yake ba.

***************

Goma na safe ta kammala dukkan abinda ya kamata tare da taimakon lantana,a bakinta taji cewa magabatan hamid ne zasu zo neman auren asma’u,sun gama komai sun killace waje daya,tana shirin barin kitchen din asma’u ta shigo,sanye take da kayan bacci tana amsa waya murya qasa qasa,ko ba’a gaya mata ba tasan da hamid take wayar,a haka ta qaraso inda kayan suke killace ta soma bubbudawa tana gani daya bayan daya,kashe wayar tayi sannan ta dauki plate daya cikin ma’ajiyar farantai ta soma diban duk abinda taga yayi mata,aysha bata tanka ba tunda tasan ta gama nata,sai ta saka kai kawai ta fice ta bar mata kitchen din,a nan asma’u ta zauna ta cika cikinta,cikin ranta tana yaba dadi da tsaruwar girkin,saidai koda wasa ko sau daya bata taba daga baki ta furtawa wadda ke bautar ba.

Daga nan dakinta ta koma ta fesa wanka sa kwalliya,yau jinta take kamar mai yawo cikin duniyar sama,ji take duk duniya a yau babu wata halitta data kaita farinciki,mallakar hamid shine cikar mafarkin rayuwarta,ita kanta batasan irin son da take masa ba,bata kuma tsammaci zata so wani namiji irin haka ba.

Sha daya na safiya da minti bakwai motocin gidansu hamid suka soma jerin gwano a harabar gidan daddy,a sannan aysha na tsaka da karyawa,duk sa cewa ba wani abun arziqi take iya ci ba tub da can ma bare yanzu da maganar ta mata karan tsaye cikin rayuwarta,take kwana ta tashi da ita,kullum kwanan duniya maimaita shawarar mero take cikin zuciyarta,ko yaushe gwada yadda zata doshi daddy take,saidai har yanzu ta kasa samun qwarin gwiwa,dalili kenan da ya sanyata ta duqufa da yin istihara,don bata fatan ko dai dai da sau daya a rayuwarta ta biyewa son zuciyarta da zai sanyata nadama a gaba.

Iya motocin da suka jere kawai ya isa ya gaya maka lallai ba qananun mutane bane,irin buri da mafarkin asma’unne.

Kiran da mummy ke qwala mata ya sanyata aje cup din tea da tun dazun take qoqarin tursasa kanta taga ta shanyeshi kosa bata ci komai ba saidai yaqi tafiya,a hanzarce ta sauko ta tadda mummyn cikin kitchen tana duban kayan da asma’u ta bubbude ta diba
“Wanne irin abu ne haka?” Mummyn ta fada fana hade rai
“Anty asma’u ce ta diba” ta fada cikin sassanyar muryarta dai dai sanda asma’un ta sake dawowa tana naeman mummy cikina adon da tasha tamkar yaune bikin nata
“Wanne irin shashanci ne wannan,ayiwa baqi abu ki bude ki diba?,ce miki akai su qananun mutane ne…..lantana….ku dauka ku kai musu hakan tunda raini kikeson siya mana” a shagwabe ta dira qafa tana hade hannayenta waje guda
“Am sorry mummy….wallahi sha’awa suka bani shi yasa na diba”
“Ja’irar yarinya” ta fada tana jifanta da harara ita kuma tana dariya
“Aysha ku gyara kayan su lantana su dauka su miqa” ta fada tana juyawa ta wuce asma’u tabi bayanta,tsayawa tayi ta sake gyarawar kamar yadda ta umarceta sannan ta koma dakinta ta bar su lantana suna kwashe kayan zuwa babban falon baqi na gidan.

Zuwa azahar tana iya jiyo maganganun asma’u cikin farinciki,jifa jifa da maganar mummyn tana ta waya tana sanarwa,an kawo kudin asma’u naira miliyan daya,bakin mummy kam yaqi rufuwa,zallaf farincikinta yaqi ya qare.

*****************

Qarfe bakwai na daren ranar jirginsu ya sauka daga qasar china,ya tsuke yayi kyau sosai cikin suit dinshi baqaqe baki daya,idanunsa saye da sun glases daya sake fitar da hancinsa daga tsakiya,ga kuma sajensa daya kwanta yayi kyau ya sake fidda adon fuskar tashi,sati biyar din da yayi sai yaji kaman ya jima sosai baiga anninsa ba,hakan ya qara masa daukin zuwa ya ganta.

*****************

Tara na dare yana gaban anninsa,daga shi sai ita a parlourn,sau tari idan suna irin wannan zaman baka ganin kowa daga shi sai ita,saika rantse sa Allah shine auta ba sulaiman ba,tsabar shaquwa ce da qauna ta musamman da Allah ya sanya tsakaninsa sa ita fiye da duka sauran yaranta.

Abinci yake ci yana bata labarin yadda tafiyar tasu ta kasance har ya kammala cin abincin nasa wanda yayi dai dai da shigowar sulaiman cikin kwalliya da alamu daga wani waje ya dawo
“Daga ina kake haka?,ya zaku fita ku barta ita kadai cikin gida daga ita sai masu aiki?” Cewar khalipha
“Ban jima da fita ba ma,tunda ka tafi idan muka fita ita kadai take zama”
“Inasu amal din?” Ya tambaya yana dubanshi
“Washegarin tafiyarka suka tafi suma”
“Ohk….ohk…” Ya fada yana kada kai tare da hasashen wani abu,tabbas yasa ba yadda barewa zatayi gudu danta yayi rarrafe,saboda shi kenan suke zaune cikin gidan hakan ya sake tabbata ba domin mahaifiyarsa ba kaman yadda zeenart tasha nunawa
“Yanzun daga ina kake?” Khalipha ya fadabyana kurban tataccen ruwan inibi
“Ni yaya?” Ya fada yana shafa kanshi,murmushi anni tayi
“Kai din ga,nima so nake insan ina kaje” ta fada cikin salon zolaya
“Anni…kinfa sani…wata ‘yar unguwa ce”
“Kadai fadi gaskiya….muhammadu idan bakai da gaske bafa ‘yan uwanka zasu rigaka tashi….ya kamata dai ka maida kai,shekaru jaa suke,hakanan lokaci baya jira”.maganarta ita ta sake tuna masa da case din daya tafi ya bari bai kashe ba
“Kwanan nan in sha Allahu anni….kici gaba da yimin addu’a” ya fada cikin sanyin murya,yana jin ya kamata ya kawo qarshen komai matuqar ya kashe wannan matsalar yana jin dama kawai zai bata ta zaba masa matar aure,yana da yaqinin ba zata zaba masa baragurbi ba,yana kuma saka ran cewa zaiyi dace.

*mrs muhammad ce*??
[3/6, 8:49 PM] Binta Mustapha: *_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*

*DB*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button