Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 31

Sponsored Links

ittafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276 ko kiyi min TRANSFER din 1k Dan samun Special Group ta asusuna na 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276.

ByTare da cewa.
“Lahh Ummi kalli Hamma Jabeer kusa da Uncle Jabir Ali ɗin can”.
Cikin Murmushin Ummi tace.
“La ai kuwa, Allah sarki masha Allah, tabarakallah. Allah ka ƙarawa Annabi daraja, Allah ka ƙara bamu hasken addini da imani a zuƙatanmu.”
Amin Amin Hibba tace.
Tare da juyowa ta kalli Shatu da tayi kamar bata jisu ba,
Sai tea ɗinta take zuƙa a hankali.
A zahiri zakace idonta kan cup ɗin yake, amman a baɗini kan allon TV’n idonta yake, ta zubawa fuskarshi ido. Duk da bawai kai tsaye shi kaɗai ake ɗaukaba, limamin dake jansu ake ɗauka hakan yasa suma suka fito da yake yana cikin mamun limaman sahun forko.

Sosai take ƙare mishin kallo tare da tsarin shigarsa dana mutanen da yake cikinsu.
Sam bazaka iya bambance shi da suba, Especially ma Sheish Jabir Ali da yake matuƙar kama dashi.
Haka nan taji wasu irin zafafan hawaye masu ɗumi suna tsastsafo mata cikin jijiyoyin idonta.
Ta kuma kasa janye ƙwayar idanunta kanshi. Tana kallon tsarin shigarshi da kullum take ganinshi a matsayin takura.
Lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su.
Ummi ta kalla wacce farin cikin ta ya fito fili.
Hakama Hibba. Sai murnar abun takeyi tamkar tayi tsalle ta shiga cikin TV’n,.

Related Articles

Ganin sun sunkuya kai ruku’uh da zasu tafi sujjada ta biyu ne, kuma an ɗaga camerar an maidata ɗaukar samane.
Yasa ta miƙe a hankali bisa santa table dake tsakiyar falon ta ajiye cup ɗin kana ta kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi kinji masallacin Joɗa ma sun fara sallan kuma muna zaune”.
Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa.
“Farin cikine ya rufeni Shatu,. Muje muyi al’walan mu tafi”.
Uhum tace ta juya ta nufi falonta tana mai share hawayenta da har yanzu suke zubowa, tanajin zuciyarta na amsar wani nannauyan abu a kan Sheykh, ta yarda ta gamsu cewa mutun me ibada da imani da ilimi abin sone a zuciyar kowane mutum na gari.

Bayan sunyi al’wala ne suka fito cikin manyan jihabai ƙatti har ƙasa suka nufi woje.
Ananne Shatu tai mamakin ganin yadda kusufa-kusufa matan masarautar ke fitowa, duk suka nufi hanyar zuwa masallacin ta ƙofar dasu Lamiɗo ke bi.

Suna fitowa jikin masallacin sai ga wani ƙaton rumfa na ƙara an lailayeshi da wani irin yashi fari ƙal-ƙal kana ga hasken wuta a cikinsa.
ko wacce da sallaya a hannunta tuni wasu kuma sunma shimfiɗa sallayunsu sunbi jam’i hakanan matan maƙota da sauran matan bayi da hadimai duk nan suke zuwa.
A jeru gaba ɗaya ananne ga kafaɗar matar sarki gata baiwa.
Babu matsayi ko milki bare isa ko ƙasaita.

Haka dai suka bi jam’i sai ƙarfe uku aka idar akayi addu’o’in kana akashafa aka kai sujjadar ƙarshi ta witirin.

Kana akayi taiya akayi sallama duk kowa ya nufi gidanshi.
Daga nan kuma aka kama aikin sahur.

Suna dawowa Hibba ta kuma kunna TV nan ta samu su tuni su sun idar. Wasu nata ɗawafi ne sai addu’o’in ake jerawa.
wanda sai kaji tsikar jikinka na tashi sabida yadda yake ratsa zuciya da jini.

Washe gari da bayan sallan isha’i da asham, yanzu Jalal da Jamil ne kaɗai ke zuwa dan Imran da Sulaiman ma dasu aka tafi.

Haka yasa yanzu duk suna zama a Dinning table suyi buɗa baki a tare.
Jalal ne ya ɗan kalli Ummi cikin cin Beans salad da Shatu tayi musu.

Hibba ce keta santi tana cewa.
“Alhamdulillah yanzu dai saura mana azumi tara ko takwas”.
Murmushi sukayi, ita kuwa da sauri tace.
“Kai takwas nema in sha Allah”.
Jamil kam tuni yake dariya tare da cewa.
“Tara ne”.
da sauri ta kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi wai haka ne?”.
Cikin dariya tace.
“A a ban saniba Hibbat.”
Plate ɗin data zuba ferfesun jan nama ta jawo tare da fara ci tana lumshe ido tace.
“Takwas ɗin nema in Allah ya yarda”.
Allah yasa haka Shatu tace.
Sai yanzu Jalal ya ɗan kallesu tare da cewa.
“Ashe dai duk kanwar jace”.
Murmushi Ummi tayi kana sukaci gaba da cin abinci.

Yau dai ana zaton salla saura kwana biyar ko shida.

Da hantsi suna zaune dan yau sun tashi da wuri.
Aunty Juwairiyya ce tayi sallama tare da shigowa, Bayan Ummi ta amsa mata.
Gefen Hibba ta zauna tare da cewa.
“Alhamdulillah Ummi ɗinkunan mu sun dawo, yanzu KB ya kawosu ya shigo ko?”.

“Eh ya shigo mana”.

Juyawa tayi ta kalli Hibba tare da cewa.
“Je kice ya shigo Hibba yana nan zaki kanshi cikin baƙar mota”.
To tace tare da miƙewa da sauri.

Jim kaɗan suka shigo tana gaba da jaka a hannunta yana biye da ita a baya da ƙattin jakunkuna guda biyu da wani yaro shi shima da manyan jakukkunan biyu.

A tsakiyar falon bisa carpet suka aniye jakunkunan kana, ɗaya yaron ya juya ya fita.
Shi kuwa Kabir ya zauna a ƙasa bisa carpet ɗin tare da cewa.
“Barka da hantsi Ummi”.

“Barka dai Kabiru, munyi Sa’a an cika mana al’ƙawarin ko”.

Murmushi yayi tare da cewa.
“Sosai ma kuwa Ummi aini telane mai amana”.
Hibba ce ta ɗanyi murmushi tace.
“To ka bari a yebeka mana”.
Cikin dariya ɗan matashin yace.
“A a ai duniyar yanzu kawai ka yabi kanka, dan ba lallai bane wani ya yaba maka”.
Dariya sukayi duka.
Kana ya fara firfito da kayayyakin.
Ko wanne da sunan maishi a jikinshi.

In ya fito dana Ummi sai ya miƙa mata, in ya fito dana Aunty Juwairiyya da yaranta sai ya miƙa mata.

Hakama na Hibba yana fitarwa yana miƙa mata.

Shatu da yanzu ta fitone, ya kalla tare da cewa.
“Barka da safiya Sayyada Shatu”.
Murmushi tayi Allah ya sani in sun ce mata Sayyada dariya suke bata wato irin ita matar Al Sheykh ko.
Cikin nitsuwa da danne dariyarta tace.
“Barka dai”.
Sai kuma ta ƙara so ta kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi waye ne shi?”.

“Telan mune”. Ta bata amsa a taƙaicd.
Cike da mamaki tace.
“To ina ya sanni?”.
Hibba ce ta amshi zancen da cewa.
“A hoto ya sanki, da mukaje kai ɗinkunanki hotonki kawai aka nuna mishi, ya ɗinka kuma kinga komai yayi dai-dai ko”.
Kai ta jinjina tare da cewa.
“Lallai kam yayi ƙoƙari”.

Cikin dariya yace.
“Uhum ai na iya aikina sosai Sayyada”.
Yanzu kam dariya sukayi duka.
Kana ya zaro kayanta a ƙalla kala takwas ya miƙa mata.
Amsa tayi tare da cewa.
“Sannu”.
Hibba kuwa irga kayan tayi tare da cewa.
“Kb saura kala bibbiyu a namu nan gani basu”.
Kanshi ya ɗan sosa tare da cewa.
“Wannan yarinya akwai son kalato laifin mutum to sai jibi zan kawosu ko kuma in bawa Su Jamil in sunje amsar kayansu”.
Cikin murmushin Aunty Juwairiyya tace.
“Yauwa ka bawa su Jalal ɗin ma kawai”.

To yace, kana ya miƙowa Ummi ƙatuwar jakukkuna guda uku tare da cewa.
“To Ummi ga na yaranki”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ka kyauta min Kabiru ngd matuƙa, Allah yayi al’barka”.
Amin Amin yace kana ya sallamesu ya fita.

Ita kuwa Ummi Saratu ta kwaɗawa kira tana zuwa.
Ta tace.
Jeki kira duk sauran hadimai suzo duk wadannan Kabiru yazo ya gansu ranar.”
Da sauri tace.
“To kana ta juya ta fita.
Ita kuwa Ummi. Inda take zaune ta nunawa Shatu.
Tare da cewa.
“Zo nan ki zauna, zasuzo, ko wacce zata gaya miki sunanta, sai ki duba sunan jikin kayan sai kibata, su duk kala ur’uku akayi musu.

Zaki basu da kuɗi dubu biyar-biyar.
Kai ta gyaɗa kana da sauri ta koma ɗalinta.
Sabida. Sai yanzu ta gano me zatayi da wannan kuɗin da ya bata kenan.
Kuɗin ta kwaso kana tazo ta zauna.

Nan suka rinƙa zuwa suna gaidata da gaya mata sunansu. Kana Hibba ta irga dubu biyar, ta ɗaura kan kala bibbiyu sun ta basu.
Ummi kuwa jakan gabanta ta buɗe tana basu takalma.
Aunty Juwairiyya kuwa jakar hijabai ta buɗe tana basu.
Suna godiya suna tafiya.
Haka sukayi tayi har kusan awa biyu kafin suka gama, duk kayan sun ƙare sai kuɗin ne ya rage.

Ganin lokacin salla yayi ne, suka tafi.

Bayan sun idar da salla ne, suka fito.
Nan a falon Shatu suka zauna.
Suna ɗan hira sabida yau aikinsu baida yawa, kuma Saratu nacan na rage musu.

A hankali wayar Ummi ta fara suwa, alamun ana kiranta.
Da sauri ta kalli Hibba tare da cewa.
“Hibba ɗauko min wayata a ɗaki”.

Miƙewa tayi tare da cewa to.
Jim kaɗan ta fito da wayar da sauri ta miƙa wa Ummi wayar a kunne tare da cewa.
“Amshi Ummi kiyi mgna na amsa kiran Hamma Jabeer ne, kin sanshi baya kira biyu.”
Cikin sauri da tarin jin daɗi Ummi tace.
“Assalamu alaikum”.
Shi kuwa Sheykh Jabeer a can saudia yana tsaye ne a gaban dreesing mirror yana gyara igiyoyin al’kyabbar jikinshi.
Tare da saƙala wayar a kunnenshi ya matseta da kafaɗarshi.
Alamun sauri yake yana shirin tafiya haramine.

Cikin sanyi yace.
“Wa alaikissalam. Barka da gida Ummi”.
Fuska a sake tace.
“Barka dai Sheykh, ya ibada?”.

“Alhamdulillah Ummi, yasu Jalal”.

“Suna lfy, kuma basa wasa da ibada, yanzu Jamil ya dena zuwa hirama wata ƙil kuma ya ɓata da Khadijah naji yanzu wata Maryam yake kira, Jalal ne dai yake ɗan fita shima ba sosai ba”.
Gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa.
“To Alhamdulillah, eh shi Jalal ba matsala fitanshi, nasan dashi.
Ya Hibba kuma tana azumi ko batayi?”.
Cikin murmushin da kallon inda Hibba take tace.
“A a Hibba ai an girma yanzu ta rage rakinma”.

Ɗan karamin mataji ya ɗauka yana kontar da sajenshi yace.
“To Ummi na gaisheku, na kira Aunty Juwairiyya kam nani jikin ya Jafar da sauƙi sosai mun gaisa da Hajia Mama, har take cemin Affan ɗina zai dawo a salla”.
Da sauri tace.
“Uhum Sheykh”.
Ajiye kum ɗin yayi tare da cewa.
“Na’am Ummi”.
Cikin sanyi tace.
“Ga Shatu”.
Shiru yayi baiyi magana ba, kuma bai katse kiranba,
jin haka yasa ta kuma cewa.
“Sheykh”.

“Na’am Ummi”.
Ya kuma cewa.
A hankali tace.
“Ga Shatu”.
Still baiyi mgn ba, hakanne yasa a hankali ta mannawa Shatu wayar a kunne ta.
Kana ta sa hannunta ta kamo hannun Hibba suka fita babban falon.

Shi kuwa Sheykh Jabeer shiru yayi tsaye gaban dreesing mirror, yana kallon gemunshi.
A hankali yake jiyo sautin sauƙar numfashin can ƙasa-ƙasa, ɗis ɗas haka yaji ƙasan zuciyarshi na harbawa.

Ita kuwa shiru tayi tanajin sautin tasbihi da yakeyi can ƙasan-ƙasan maƙoshinsa,
Lips ɗin shi na motsawa a hankali suna fidda sautin can ƙasa.
Jin shirun yayi yawane yasa a hankali ta buɗe bakinta tare da cewa.
“Assalamu alaikum”.
Sai kuma tayi shiru ta kasa kunnen dan jiran amsarshi.
Gyara zamanta tayi tare da ƙara riƙe wayar, numfashi ta sauƙe a hankali.
Hakan yasa yaji sautin iskar.
Har ta cire tsammanin zai amsa sai kuma taji muryarshi can ƙasa yana cewa.
“Wa alaikissalam. Ashe kin iya sallama?”.
Ya jefo mata tambayar a gajarce.
Cikin juya ido tace.
“Ba’a koya min da wuri bane!.”
Shine mgnar da tayi niyar gaya mishi, sai kuma tayi mgnar a zuci, ta danne abun.
Sabida tana son ta nemi al’farman addu’o’in a kaba, aka yayunta da suka bace, shiyasa cikin sanyi tace.
“Eh, Ummi ta koya min”.
Shiru yayi kamar bai jitaba,
ita kuwa a hankali tace.
“Ina kwana”.
Kanshi ya ɗan kalla a madubi tare da cewa.
“To Kifin rijiya su nan yanzu wunine”.
Cikin sanyi da sassauta Muryar son isar da buƙatar ta tace.
“To ina wuni”.

“Alhamdulillah”.
Ya bata amsa.

Miƙewa tsaye tayi ta nufi bedroom ɗinta.
Tare da cewa.

“Ya ibada?”.

“Alhamdulillah”. ya kuma cewa.
“Har ya kai hannunshi zai janye wayar sai kuma ya tsaya jin tana cewa.
“Uhmm, Ayyah Yah Sheykh..”.
Sai kuma tayi shiru. Cikin saurin jin an kira salla murya a nitse yace.
“Uhumm Ayyah, me ɗin?”.

Da sauri tace.
“Dama.. dama!!…”.
Gajeren tsaki yaja tare da cewa.
“Sauri nakeyi zan tafi masallaci, kada kisa na rasa damata”.
Cikin rauni da muryar dake nuna cewa tana zubda ƙwalla tace.
“Ayyah dan Allah da Manzonsa.
In kaje kayi min addu’a a harami mana”.
Juyowa yayi yana kallon Haroon da Ya Hashim da suka shigo yanzu alamun kiranshi zasuyi.
Cikin wata iriyar murya a hankali yace.
“Addu’ar me zan miki?”.
Murya na rawa tace.
“Allah ya dawo min dasu Yayana lfy, ya kare minsu a duk inda suke, ya baiyana sucikin gaggawa”.
Cikin rashin fahimtar zancen nata yace.
“To zan miki saboda Allah da Manzonsa da kikace”.
Cikin jin daɗi tace.
“Ngd matuƙa Allah ya biya maka buƙatunka.”
Wani irin sassanyan numfashi ya sauƙe tare da lumshe ido a hankali yace.
“Amin ya rabbil izzati, kema kuma kiyita addu’a ki dage da ambaton Allah zai cika mana dukkan burinmu”.
Yana faɗin haka ya katse kiran.

Ita kuma murmushi tayi tare da share hawayenta.
Cikin sanyi tace.
“Ya Allah ka dubemu da idon rahama”.
Hibba dake shigowane tace.
“Amin Amin.”

Daga nan suka fito falo suka kama sabgoginsu.

A kwana a tashi asarar mai rai.
Yau da gobe kayan Allah.
Kamar yau aka kama azumi gashi yau an kai azumi na ashirin da tara.
Wanda ake tsammanin tsalla gobe ko jibi.

Irinsu Hibba duk sunfi fatan wata ta dawo yau.

Gaba ɗaya wunin yau aiki Ummi da Shatu da Saratu suka wuni yi, wanda aikin salla ne.
Zabbin da Jalal ya kawo bisa umarnin Hammansun.
Da kuma kajin da Lamiɗo yasa aka rabawa al’ummar masarautar Joɗa.
Ko wani Side in dai akwai mace kaji goma ake kaiwa.
Da tarin kayan miya komi da komi, wanda shi cikin lambun masarautar ake cirewa.
Kajin kuma daga gidan Gidan gonar MJ aka kawo, kana zabbin da aka kawo manyan sashin Masarautar Joɗa ma daga gidan gonar MJ aka kwasosu. Haka ƙoyayen kaji.
Duk an rarraba ko ina.
kuma duk saida aka yanka su aka gyarasu aka rarrabusu, dan haka aiki kawai aka fara babu kama hannun yaro.
Hadimai da bayi sunata aiki.

Duk sauran ɗinku nan suma sun dawo.

Kasan cewar kusan a kitchen ɗin suka wuni ne, yasa Shatu ta ɗauki zabbi uku tun da azahar tayi musu gyara na musamman.
Hibba kuwa tana Side ɗin Aunty Juwairiyya anayi mata zanen lalle.

Akan sai dare za’ayiwa Shatu shiyasa taketa kimtsa aiyu kanta da wuri.
Dama sunje da sassafe an wonke musu kai an gyara musu.

Ummi kuwa tayi lallenta na gargajiya tana kwance a falo.
Hakane yasa Shatu ta kira Gimbiya Aminatu.
Cikin wasa tace.
“Gimbiya a ƙaro min mai taya aiki yau Ummi na tasa lalle, Hibba ma tana can ana zana mata, nida Sara ce kaɗai a kitchen.”
Dariya Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa.
“To Sayyadar Sheykh bari Larai tazo”.
Cikin jin daɗi tace.
“To Gimbiyar Lamiɗo”.
Dariya sukayi duka kana sukayi sallama.

Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa.
“Tace zata turo Larai, Ummi ta iya aiki ko?”.
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
“Sosai ma kuwa”.
Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa kana ta miƙa wa Ummi wayarta tare da cewa.
“Ummi sai mun nitsu ki bani number Gimbiya Aminatu”.
To tace kana ta koma kitchen ɗin.

Wanke zabbin tayi fes tare da ɗan matsa lemun tsami kaɗan a ciki.
Kana ƙara lallaɓeshi.
A tukunyar ƙirar ƙasar Cameroon ta zubasu.
Kana tasa al’basa, Curry, Maggi, kanamfari, citta, tafarnuwa kaɗan, da gishiri ɗan ƙanƙani.
Ta rufe tukunyar da zabbin uku suka cikashi.

Bisa gas ta ɗaurashi kana tasa wutan dai-dai.

Saratu kuwa sa sauran tayi a babbar tukunta tasa kayan ƙamshi da ɗanɗano.
Sannan ta ɗaura.

Dai-dai lokacin Larai ta shigo.
Bayan sun gaisa ne, ta ɗauki markaɗen waken ƙosan da zasuyi na kaiwa masallaci.

Da markaɗen tattasan da taruhu da al’basan.

Ita kuwa Shatu yau kunun basise ta dama mai kyau, ta cika kulolin.
Kana
Ta daura ruwan tea
Yana tafasa ta ɗura a flaks.

Duk wannan zabbin sunata sulaluwa suna bararraka sai wani irin masifeffen ƙamshi da yake tashi.
Har yawunsu na tsinkewa.

Fruits ta ɗebo a Fridge ta gyarasu ta shiryasu a tray biyu shiri mai kyau.
Kana ta medasu cikin ƙaramin Fridge ɗin data kashe dan sanyi su ya daidaita.

Larai na dawowa, suka fara suya.

Ita kuma ƙullun waken kaɗan ta ɗiba.

Kana tasa dafaffan ƙan data ɓare.
Da al’basan da kifin data tafasa ta murmusa a cikin ƙullun ta sa mai da Maggi curry da dai sauran kayan haɗi ta kulla alala.
Ta ɗaura a gefen tukunyar zabbin.

A ƙalla awa ɗaya zabbin na ɓararraka kana tazo.
Tasa jajjagen taruhu da al’basan,
A ciki.
Sai ta ɗan tarfa soyayyan mai kaɗan a ciki ganin kamar man jikin zabbin bazai mata yadda takeso ba.
Kayan ɗanɗano ta kuma sawa, da yankekken al’basa mai yawa ta zuwa a ciki.
Kana ta maida marfin tukunyar ta rufe. A hankali danderun zabbin ya fara taushi yana lugub cewa,
Ƙasusuwan suna saɓulewa daga jikin naman.

Tuni su Sara kuma sun gama soya ƙosan, nan ta ciccika kulolin da za’a fidda kana ta ɗiba musu nasu, daban.
Sannan suka tattare mata wurin suka tafi sabida ita ta kusa gama nata aikin.

Koda alalan ya nuna ta kwashe tasa a kuloli biyu.
Sai kuma ƙaramar kula daya.

Ya rage zabbin ne kawai a wuta.
Rage wutan tayi sosai yadda zasuke jin wutar na ratsasu da kyau.

Tattare wurin tayi ta kimtsa komai.
Kana ta fito falo.
Ƙarfe biyar da rabi.
Tace lokacin data zauna ta ɗauki wayarta Ummi kuwa na cire lallenta.
Ya kuwa yi baƙi yayi kyau.
Hibba ce ta shigo cikin
Langwaɓe kai tace.
“Aunty Shatu me ake dafa mana yau tun waje can ake jiyo ƙamshin na fitowa a gidanki”.
Cikin gajiya tace.
“Tuwone miyar taushe”.
Cikin zumbura baki tace.
“Tab wlh bazanci ba, inyi azumi a bani tuwo ta yaya zan haɗiyeshi, yaseen zan koma wurin Aunty Juwairiyya nagama tayi awara, ƙamshin gidanki na jiyo na gudo”.
Dariya Ummi tayi tare da cewa.
“Hibba dai cokali a saki a daɗi ko?”.
Murmushi sukayi dukansu kana suka konta
A kan kujerun.
Ganin Ummi ta miƙene yasa Shatu cewa.
“Yauwa Ummi duba mana kitchen ɗin kiga ko Danderun yayi”.
To tace kana ta shiga ta duba.
Sannan ta fito tare da cewa.
“Yayi sosaima, kai gskyar Hibba nima da bana jin ƙamshi yau naji ƙamshin girkin.
Jeki sauƙe kawai kiyi wonka kuzo ki huta kafin a kira salla”.
To tace kana.
Ta miƙa taje ta sauƙe. Binta a baya Hibba tayi tare da cewa.
“Wai Aunty Shatu bakuga lallena bane banji kunce yayi kyau ba”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Kayya Hibba ai yanzu kam idanunmu basa gani”.
Ta ƙarshe mgnar tana sauƙe tukunyar,
Kana ta ɗauki Foodflaks guda uku biyu manya ɗaya karami.
Gaba ɗaya ƙasusuwan sun saɓule.
Romon yayi kaurin diddigin nama.
Rabin zabuwa ta sawa Sara da Larai a ƙaramar kular.
Kana tasawa Gimbiya Aminatu gudar.
Su kuma tasa musu ɗaya da rabin a kularsu.
Kular datasa alala data kosai ta jere a babban tray’n.
Da tray’n fruits, ɗin a gefe.
sannan da flaks ɗin kunu ta bawa Hibba tare da cewa.
“Ki kawai Gimbiya Aminatu.
Na ƙaramar kular nasu Sara ne”.
Amsa tayi kana ta fita.

A can ta samu Ya Jafar shida Lamiɗo bisa alamu yau tare zasuyi buɗa baki.

Ita kuwa Shatu Hibba na fita.
Ta sauƙe babbar tukunyar tafashen naman kajin ta ajiye gefe.
Dama zabbin duk a freezer’n suka sasu.

Ɗan buɗe bakin tukunyar tayi yadda zasu sha iska su kama jikinsu. Jajjageggen Attaruhu da al’basan kuma ta sashi a Fridge.

Kana ta fito da komai ta jere musu a dinning table.

Sannan ta wuce ɗakinta. Wonka tayi da ruwan sanyi duk da bata son sanyi
To amman duk jikinta huruwa yake tamkar wuta.
Haka yasa tayi da ruwan sanyi.
Tana fitowa ko mai bata shafa ba.
Wata atamta mai taushi riga da zani, ɗinkin Borno sitayel
yayi masifar yi mata kyau.
Ɗan kwalin ta ɗaura a sauƙaƙe sabida duk jikinta rawan yunwa da azaba yakeyi.

Cikin falon ta fito nan ta samu Hibba ta dawo.
Jalal, Jamil, suma sun zo.
Ummi ma ta fito da alamun tayi wonka.

Tana isa ana kiran salla.
Nan sukayi buɗe baki da fruits kawai sai kunun suka ɗansha, kana kowa yaje yayi sallan.
Sannan sukazo sukaci sauran kayan kwalamarsun.

Suna tashi sukayi sallan isha.
Zuwa lokacin kuma anata raɗe-raɗin ba’aga wata bafa.
Wannan lbrin shiya tada hankalin Hibba da sauran mutane irinta, a gefe harma da Jamil
Sabida azumi ɗayan nan da za’a ƙara wasu ganinshi suke kamar shekara ɗaya za’ayi ana azumin sai kaji anata gunaguni da cewa wai anƙi a faɗa ne.
Shatu kuwa murna tayi dan ita bata samu tayi lalle ba.
haka yasa gobe zata ƙarisa aikinta a nitse.
Jin an kira salla za’ayi Asham ne yasa Hibba zubda hawaye tare da cewa.
“Wlh zan kira Umaymah da Hamma Jabeer ina dai saudi sunyi salla Ni babu ruwana salla zanyi”.
Ta ƙarishe mgnar tana kiran layin Umaymah yanata ringin ba’a ɗagawa.
Hamma Jabeer kuwa data kira baya shiga ma gaba ɗaya. Haroon kuma shima yana shiga baya ɗagawa.
Dariya Shatu tayi tare da kunna tv tace.
“kalli Hibba suma asham sukeyi”.
Da sauri tace.
“A a kam Isha’i ne”.
Ganinfa da gaske Hibba keyi yasa suka sherata sukaje sukayi asham kana suka dawo.
Kitchen suka shiga, soya kajin sukayi suya mai kyau kana suka ajiye.
A gefe.
Jalal ne ya leƙo kitchen yace.
“Ummi azumi talatin zamuyi bana”.
Dariya tayi tare da cewa.
“Aiko gacan Hibba nata fushi.”
Shigowa yayi plate ya ɗauka ya miƙawa Shatu tare da cewa.
“Aunty a samin nan”.
Amsa tayi tare da saka mishi soyayyen naman kazan.
Dakekken yaji ta saminshi a gefen
Fridge ya buɗe ya ɗauki Du-du tare da cewa.
“Wannan fa yaushe aka fara kawoshi”.
Ummi ce ta kalleshi tare da cewa.
“Naga Shatu tafi sonshi ne yasa nace akawoshi”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“To nima bari in taɓa shi”.
Nan ya fita falon.

Su kuwa suka ƙarisa aikin.
Suna ƙoƙarin fitowa ne.
Jamil ya leƙo tare da cewa.
“To yau kuma meye za’ayi mana na sahur ne”.
Jalal dake bayanshi ne yace.
“Yo azumi ɗaya ai ko tazarce zamuyi”.
Hararan Jalal yayi tare da cewa.
“Hege daka ci kaji kayi tak ba, mutun kamar kura”.
Murmushi Jalal yayi tare da cewa.
“Yes naci in kuma ƙara”.
Hararanshi Jamil yayi tare da cewa.
“Mutun sai son nama kamar ba bafulatani ba sai kace babarbare”.
Da sauri
Jalal yace.
“Yo dama aini Arbabarbare ne”.
Dariya Ummi tayi,
Ita kuwa Shatu Jalal ta kalla tare da cewa.
“Me zan dafa mana to?”.
Tsaki ya ɗan ja tare da cewa.
“Kiyi mana Coucous da miyar hanta kawai”.
To tace kana ta juya ta fara aiyin.
Cikin sa’a ɗaya ta gama ta fito.

A falo ta samesu suna.
Waya da Sheykh yana ce musu kadafa suyi sakaci suyi sallan, dan babu lbrin ganin wata.

Hakan dai suka haƙura.
Bayan yaga waya da sune.
Umaymah ta shigo ta sameshi zaune yanacin inabi.
Gefenshi ta zauna da wata jakar.
Miƙa mishi tayi tare da cewa.
“Kace ranar salla da safe in an sauƙo idi dai zaku tafi ko?”.
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
“Haka dai Wannan tsohon Galadiman ya buwayeni da zancen komawar”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Abbanka ma yace min ranar sallan zaku tafi”.
Kai ya gyaɗa.
Ita kuwa gyara zama tayi tare da cewa.
“Tsarabar me ka sayawa Shatu da ƴar ɗakinta Hibba”.
Da sauri ya kalleta tare da cewa.
“Umaymah tsaraba kuma.
“Yo tsarabar me zanyi sai kace wani sabon zuwa, Ni ibada nazo yi ba tsaraba ba”.
Jakar ta nuna mishi tare da cewa.
“To ni kam ga tsaraba ka kai musu, wannan na Shatune Hibba gobe zan dawo da nata.
Kai kuma in kaso ka koma hannu rabbana”.
Kanshi ya sunkuyar kamar baijiba.
Sai kuma tace.
“Jazrah tace in gaidaka, wai tunda kazo bata ganka ba”.
Cikin sanyi yace.
“Yoh dama ya zanyi in bari ta ganni yarinya sai kallon masifa”.
Miƙewa Umaymah tayi ta fita.
Tana fita Haroon da Ya Hashim suka shigo. Nan suka ɗanyi hira kafin suka tashi suka tafi masallacin dan shabiyu ta kusa a fara tuhajjudin.

Nan suka tafi.
Washe gari aka tashi da azumi na talatin.
Allah cikin ikonshi aka kaishi lfy.
Watan Shawwal ya baiyana Ramadan ya tafi kuma sai mai nisan kwana.

Shatu kuwa a wunin ranar Yar aikin Aunty Juwairiyya Sato, ta zana mata jan lalle mai ɗan karen kyau.

Koda ta dawo kuma jarakuna madarar shanu data gayawa Gimbiya Aminatu tanaso
Aka kawo mata ta tafasashi kana tasashi a manyan kware da ƙananan kwore da kyawawan robobi tasa tsami kaɗan a ko wanne kwarya da roba.
Ta rufesh ta jerasu a Fridge a ƙalla sunfi kore goma madaidaitan ƙananan sun kai kore takwas sai robobin su kuma sun kai goma suma.

Bayan sallan magriba ansha ruwa anyi nak.
Hibba sai tsalle da farin ciki da kiraye-kirayen ƙawaye da yan uwa da abokai sai tsiya Jamil ke mata.

Bayan sun gama shirya komai na aikin da zasuyi gobene.
Suna zaune a falo Ummi ta kalli Jamil tare da cewa.
“Jamil wai sai yaushe zaka share Side ɗin Sheykh ne, munyi waya da Umaymah ɗazu tace min gobe fa zasu dawo.
Anayi sallan idi a can zasu taso”.
Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“To naga mutun ga matarsa ace Ni in mishi shara”.
Ko inda suke Shatu bata kalla ba.
Ummi kuwa jingina tayi da jikin kujera tace.
“Ai bazata san ƙaidar yadda yakeson a gyara mishi ɗakinshi ba.
Dole sai ka nuna mata.”
Cikin gamsuwa da hakan yace.
“To ba matsala sai gobe da sasafe mu hau kan aikin abinda ɗakin ba wani ƙura da tarukucene da shiba”.
Eh hakane Ummi tace tare da kallon Shatu tace.
“Gobe in Allah ya kaimu Shatu ku gyara mishi ɗakin nashi”.
“To Allah ya kaimu. tace ba tare da ta kalli inda sukeba.

A can ƙasa mai tsarki kuwa.
Ana idar da sallan isha’i da yawa suka fara ɗawafi.
A cikinsu kuwa harda Sheykh Jabeer da mai sunanshi kana da Haroon
A nitse bisa tsari suke ɗawafin sunje ƙafa biyu ana uku sun isa dai-dai. Maƙama Ibrahim.
Sheykh Jabeer ya juyo kanshi ya kalli gefen damanshi da sauri cikin tarin mamaki al’ajabin Fuskar mutumin da ya ga ya wulgawa a idonshi…!

 

Littafin GARKUWA na kuɗine idan kina buƙatar saya ga number 09097853276 katin mtn na ɗari uku. Normal group in kuma special Group kikeso 1k zakiyi min TRANSFER ta ac ɗina 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.

By
*GARKUWAR FULANI*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button