Garkuwa Hausa NovelHausa Novels

Garkuwa 23

Sponsored Links

GARKUWAR FULANI*
*GARKUWAR FULANI*”Muhammad!”. Ya kira babban sunanshi tare da jawo hannunshi, ya zaunar dashi bisa kujerar da ya tashi a kai.
Cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoron abinda suke shirin aikatawa, ya kalli Mahaifin nashi, kana ya juyo ya kalli Lamiɗo da Galadima gefen damanshi ya juyo ya kalli Jadda cikin rauni ya kuma kalli mahaifin nashi tare dayin ƙasa da murya yace.
“Abba kada ka bari su ɗaura auren nan, dan Allah kace musu su bari, kada su ɗaura”.
Ya ƙarishe mgnar cikin tashin hankali da ɓacin rai da tarin rauni a fuskarshi.
Cikin zuba mishi ido Abbanshi yace.
“Meyasa? Sabida me za’a bari!? Meyasa baka so!?.”
Kanshi ya jujjuya tare da haɗe hannayenshi wuri ɗaya ya fuskanci mahaifin nashi cikin sanyi yace.
“Ni dai bana so. Abba dan Allah kada ka bari suyi.
Bana son garin nan bare mutanen cikinsa, kuma bawai haka banza naƙi auren nan ba, Abba inada matsala, Please Abba na tuba dan Allah kace su bari. In yaso a ɗaura da wani amman banda ni kam”.
Lamiɗo ne ya kamo hannunshi cikin isa yace.
“Auren’ nanfa, kamar ma an ɗaurashi an gama, domin babu wani abu ko wani mahaluƙin da ya isa ya hana wannan ɗaurin auren, gwarama ka kontar da hankalinka. Tunda ka iya jure bulalin aiko tabbas dole ka aureta, babu shakka dole sai ka aureta, bazai yiwu a dakeka a kantaba sannan ka barmusu itaba.”
Cikin jin haushin wannan fitinenne tsohon ya kwace hannunshi daya riƙe tare da cewa.
“Haka kenan kullum zanyi ta wahala a bisa wasu dalilanka da bana addiniba, me ruwanka da dukan da akayi min, ba dai kai-kasa dole aka dakeni ba”.
A hankali Galadima yace.
“Eh da kuma bakayi kukaba, baka guduba, yau kuma kasa yayi kuka ya gudu ai dole ka aure matar da a kanta aka haɗaku gasar, tunda mu dai ba sakarkaru bane, bare ace bamu san dokar gasar Shaɗi ba.”
Wayyo Jabeer ji yakeyi tamkar ya mammake tsoffin nan dan tarin baƙin ciki. Rai a ɓace yace.
“Bakufa fini sanin kainaba, tunda nace muku bana son aure, bazan kuma yi aureba, to ku barni mana, rayuwata ce ko taku, ko dole ne duk wata matsalata da sirrin rayuwata sai kun sani! Nace muku bana son wannan garin na tsani garin bana son mutanen garin karankatab ɗinsu.
Bani babu su, in kuma kukayi gangancin cusa min wata muguwar yarsu, tabbas! lallai ilaihin! A kanta zan rama sauran bulali ashirin da wancan ƙaton gardin ya min, hamsin, ni a talatin ya gudu”.
Kai Jadda ya girgiza tare da cewa.
“Ka rama mana kaida matarka, ka rama ka kuma jinyace ta”.
Shiru sukayi sabida jin muryar Dr Aliyu da kuma Galadima da Arɗo Bani da Bappa suna tabbar wa juna lfyar yaransu, cikin Mamaki ya kalli Galadima dake cewa.
“Muma ɗanmu lfyarshi lau, Namiji ne”.
Cikin sanyi Jabeer yace.
“Ji maƙaryacin tsoho, wai lafiyata lau, ko yaushe ya zama likita ya gwadani. Harda wani karkacewa yana zuba ƙarya ko farin gemunshi bai martaba-ba”.
Jin Abbanshi ya daki gefen ƙafarshi ne yasashi yin shiru.

A nan a gabanshi a gaban mahaifinshi. A gaban dubban al’ummar fulani makiyaya daketa tsastsafo tako wani sashi na duniya, a kuma gaban Lamiɗo da tawagarsa hakama Jalaluddin da tawagarsa.

Aka ɗaura auren Muhammad Jabeer da Aysha. Bisa koyarwan addinin Musulunci.

Related Articles

Sosai su Jalal, Jamil, Hashim, Haroon, Sulaiman. Sukayi mamakin wannan aure na ba zata. Ba zato ba tsammani.
Bayan an gama dai-dai-ta komai an ɗaura auren ne, kuma.
Lamiɗo ya kalli Arɗo Bani, cikin girma da ƙasaita yace.
“Yanzu zai tafi da matarshi.”
Cikin sanyi da al’hini Bappa yace.
“Allah rene yanzu kuma!?”.
Galadima ne ya amshi zancen da cewa.
“Haƙƙun yanzu zamu tafi da ita!”.
Arɗo Bani ne yayi murmushi mai cike da jin daɗin yace.
“To ba laifi ai, muje a fito muku da ita”.
Shi kuwa Bappa ido ya zuba musu.
Dan shi a zatonshi ba yau zasu tafin mishi da Shatunsa ba.

Nan duk suka ɗunguzuma, suka shiga motocin. suka nufi ƙofar gidansu Shatu.

Ya Salmanu kuwa, tuni ya shiga cikin gidan su.
Ya shiga ɗakinshi yana ta kuka kamar yaro. Bai tsamci haka abin kan iya juyewa ba, Ba’ana ya rasa Shatu shima ya rasata.

Suna isa ƙofar gidansu, duk motocin suka tsaya.
A hankali Bappa da Arɗo Bani suka kutsa kansu cikin gidan.

A tsakar gidan suka samu.
Shatu na zaune dan dawowarta kenan, hannunta tasa ta tallabe haɓarta ta zubawa su Junainah ido, shigowarta gida kenan daga dawowarta.
Cikin Ɓadamaya su Binto suka shigo gidan a guje suna ce mata wai an ɗaura aurenta da ɗan sarkin da akayi gasar Shaɗi dashi.
Jin hakane yasata yin murmushi tare sauƙe dogon ajiyan zuciya na gajiyar tafiyar da tayi, ido ta lumshe tare da cewa.
“Auren kuma wasane, da zai zama an aura min wani wanda ba’a san halinshi ba, ko ƴar tsana ma ai ba’a aurar da ita a hakaba bare ni”.
Ta faɗi mgnar cikin fargaban ganin yadda suketa rantse mata. Duk da bawai ta yarda da zancensu bane. Junainah kuwa dariya takeyi tare da ɗan tsalle-tsallenta tana cewa.
“Yeeh Auren Addana yazo, zanyi gayyan fati muyi gaɗa”.

Cikin zuba musu ido, ta zauna gefen, Ummey dake ta Binta da ido, cikin sanyi tace.
“Ummey na dawo! Ya jikin naki!?.”
Da sauri ta gyara zamanta tare da zubawa Ummey ido, cikin mamaki take kallonta ganin idanunta nata zubda hawaye ne, yasata cikin ruɗani da tashin hankali da fargabar abinda ke shirin faruwa da ita da rayuwarta.
A kiɗime tace.
“Ummey meya sameki? meya saki kuka? Jikin ne yake miki ciwo?.”
Sam Ummey bata iya mgna ba, sai kukan da takeyi,
hakanne yasa zuciyar Shatu karaya, cikin rauni wasu hawaye masu ɗumi suka fara tsiyayo mata.
Hakan ya ƙara ingiza kukan Ummey hakama,
Junainah sai ta raɓa gefensu tayi, zurui a zatonta aure abun daɗi ne ba kukaba to gashi taga su kuma kuka sukeyi.
Sosai Shatu takeyin kuka mai tarin dalilai.
Suna isa Bappa yasa hannunshi ya kamo nata, cikin sanyi yace.
“Taso kizo”.
Ido cike da hawaye ta mike tsaye bisa umarnin Bappa.
Shi kuwa Bappa cikin sanyi ya kalli Ummey da Junainah yace.
“Kada kuyi kuka, kuyi mata addu’o’in samun nasara a cikin wannan al’amari, muyi mata fatan aurenta ya zamo haske ne a rayuwarsa shi mijin da ahlinshin baki daya, fatanmu aurenta ya zamo ƙungiyar da zata jawo gskya cikin raminda aka binneta ya fito da ita kowa ya gani.”
Shiru Ummey tayi sai hawayen da suke kwaranya.
Hakama Shatu hawayenta wani na korar wani.
Ita kuwa Junainah faɗawa jikin Ummey tayi sukaci gaba da zubda hawaye.

Bappa kuwa hannunta yaja suka juya suna nufi hanyar fita.
Da kayanta na ɗazu wanda taje Genaral Hospital Ɓadawaya dasu, hatta hand bag ɗinta na rataye a kafaɗarta wayarta na ciki.

Cikin mamaki take bin bayan Bappa, tare da yin taku a hankali tana bin bayanshi yadda yake jan hannunta.
Arɗo Bani kuma na biye dasu a baya.

Suna fitowa ƙofar gidan, Haroon da Jalal suka juyo suka kalli juna,
Cikin tarin mamakin ganin kamar yarinyar ɗazuce.

Shi kuwa Sheykh Jabeer yana zaune cikin motar, shi ɗaya dan duk sun fita.
Da sauri ya dafe saitin ƙahon zuciyarshi jin ta tsananta bugawar da yakeyi.
A hankali ya maida bayanshi ya jingina da sit ɗin tare da rufe idonshi.
Yana mai jin sanyin A/C na ratsa mishi jiki da jini da zuciya.
Amman duk da haka zuface ke tsastsafo mishi a jikinshi sabida bugun da Zuciyarshi keyi ya wuce misalin.

A hankali ya juya kanshi ya kalli gefen hagunshi inda yaga motar Jadda da kuma Dr Aliyu ne da Barrister Kamal ke jere a wurin.

Bappa kuwa a hankali yake taku, yana nufo inda Lamiɗo ke tsaye Dogari na riƙe masa da laima, Ɗanzagi da fadawa na zube a kasa.

Ita kuwa Shatu cikin rawan jikin jin idanun mutane na yawo a jikinta dan ma Allah yasa akwai niƙab a fuskarta.
Take bin bayanshi. Shi kuwa Sheykh Jabeer yadda suke ƙara matso inda yake haka bugun zuciyarshin keta tsananta.
Suna isa gaban Lamiɗo Bappa ya miƙawa Lamiɗo hannunta cikin sanyi da nitsuwa da taushin lafazi yace.
“Allah rene, ga Aishatu matar Muhammad Jabeer.
Gata amana bisa jagoranci ka, nasabarka da yardarka.
Da kamala da nitsuwa da na gani a fuskar yaron yasa naji ƙarfin guiwar baku aurenta.
Ba tare da fargaba ba, yanzu kaine kaka kuma jagora a gareta”.
Sai ya kuma nuna Barrister Kamal da shima yana cikin wakilai, shi a zatonsa ma shine mahaifin Jabeer cikin sanyi yace.
“Kai kuma kaine matsayin mahaifi a gareta ku zame mata dangin ta data rasa, naso ace da mata a masu ɗaukanta, dan in danƙa amanarta a hannun macce yar uwarta.
Amman ba komai, na baku amanarta dan Allah kada a cutar da ita, domin nima ta kasance amanace a uwurina, domin ƴaƴan mu da muka haifama amanace Allah ya bamu kuma abun kiyayewa, bare kuma ɗiya irin Shatu ɗiyace da take da nasabobi masu yawa a gareni”.
Cikin gamsuwa Lamiɗo yasa hannunshi ya amshi hannunta daketa karkarwa, tuni niƙab ɗin fuskarta ya jiƙe jilak da ruwan hawaye.

Cikin Dattaku Lamiɗo yace.
“In sha Allah zan kula da dukkan lamuranta tamkar yadda nake kula dashi Jabeer, kuma kada ka damu akwai masu meye mata gurbin uwa ƙanwa yaya dama duk danginta a cikin masarauta Joɗo, baƙoma baya kukan maraici bare kuma, matar sashin jinina”.
Cikin sanyi da wasu hawaye Bappa yace.
“To Ngd matuƙa”.
Arɗo Bani ne ya dafashi tare da cewa.
“Ka sanya mata al’barka a cikin aurenta ba zubda hawaye ba.”
Sosai Haroon ya zuba mata ido.
Shi kuwa Sheykh Jabeer da mamaki yake kallon Bappa dake zubda hawaye.

A hankali su Bappa suka ɗan ja da baya.

Shi kuwa Lamiɗo ya juya ya nufi motar riƙe da hannunta.
Haroon ne yayi saurin buɗe musu marfin motar, suka nufoshi gadan-gadan.
Jalal kuwa ido ya zubawa yatsun hannunta da Lamiɗo ke riƙe dashi.

Shi kuwa Jabeer idonshi ya rufe da ƙarfi. Sai kuma ya buɗesu, dai-dai lokacin Lamiɗo ya kawota bakin ƙofar motar tare da cewa.
“Mamana kiyi bismillah ki shiga da ƙafar dama”.
Cikin shessheƙan kuka ta gyaɗa kai tare da yin bisimilla kana ta ɗan sunkuyo, sai kuma kukan ya kubce mata.
Shi kuwa Jabeer da sauri ya buɗe marfin motar ta gefen hagunshi. Kamar gilmawar walƙiya ya fita cikin motar.
Dai-dai lokacin da Shatu tasa ƙafarta ciki.
da sauri yasa hannunshi ya buɗe motar Jadda tare da shigewa ciki yaja marfin ya rufe sabida ji yayi zuciyarshi zatayi bindiga, wani irin dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai ƙarfi.

Ita kuwa Shatu, a hankali ta shiga ta zauna, don batama lura da shi bane tabbas dai taga mutun ya fita cikin motar.
Tana shiga Haroon ya maida marfin ya rufe
Shida Lamiɗo suka koma sit ɗin bayan wannan sabida su a zatonsu Jabeer na ciki.

Ganin Lamiɗo ya shigane yasa duk kowa ya shiga motarshi.
Hakama Jadda ya shiga ya zauna hankalinshi na woje.

Sai da akaja motocin suka fara tafiya ne, ya juyo da sauri jin Jabeer na jan wani ja’irin tsaki mai tare da ajiyan zuciya.
Cikin mamaki Jadda yace.
“Haaahh kai kuma Meya kawoka nan? Yaushe ka shigo min mota!?”.
Bai kula Jadda ba, asalima yi yayi tamkar bai jishiba.

Haroon kuwa cikin dariya ya ɗan bugi sit ɗin da yake zaton yana wurin cikin juya harcen Larabci yace.
“Masha ALLAH, gasar Shaɗi tayi mana rana mun rabaka da gwauranci”.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Haroon yace.
“Saura kai”. Murmushi yayi tare da cewa.
“Ni ai nan kusa za’ayi”.
Jin shirune, yasa Haroon yayi shiru,
Azotonshi ya ƙin mgna da shariyar ne suka zowa Jabeer bare, yasan yanzu a cike yake.

Su Jalal kuwa kab da al’hini suke tafeyi.

Jadda kuwa yayi iya mgnarshi yayi shiru ganin bai kulashi ba.

A haka suka isa cikin Masarauta Joɗo.

Suna isa kuwa Jabeer ya fito ya nufi Side ɗinsa, fitowarsa cikin motar Jadda ne yayi matuƙar bawa Haroon da Lamiɗo mamaki.

Haroon kuwa bayanshi yabi da sauri.

Suna shiga Side ɗinsa kuwa suka samu babu kowa.

Suna gama tsayuwa Sallama ya nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu bisa umarni Lamiɗo.

Yana shiga a babban Falon ya samu. Umaymah, Ummi, Aunty Juwairiyya, Hibba, Adda Rumana wacce take yayarsu Jabeer yar farin Abba kenan, sai mai bin mata Rumaisa.
Kana sai Gimbiya Aminatu dake tsakiyarsu, sai hadimanta.

Koda ya sanar musu, sun iso.
Kusan duk a tare suka miƙe sai Gimbiya Aminatu ce bata tashiba da hadimanta.

Su kuwa da sauri suka nufi woje, Umaymah ce gaba sai Aunty Juwairiyya dake biye da ita a baya riƙe da wani tire wanda samanshi ke ɗauke da al’kyabbar irin tasu ta matan masarauta da kuma wasu sauran tarkace.
Suna fitowa motar na isowa har bakin wurin. Da sauri suka nufi jikin motar.
Ita kuwa Zuwa yanzu ta tsagaita da kukanta, sabida ababen da take gani a cikin masarautar ya shallake tunanin mai tunani,
gaba ɗaya jikinta tsuma yakeyi, sabida idonta na gane mata ababe na ban tsoro.
Cikin ranta take mgnar zuci.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun, wannan wanne irin gidane? Me yake faruwa da mutanen masarautar? Sunko san gskyar junansu?”.
Da sauri ta rumtse idanunta sabida wasu irin hayaƙi da take gani yana tashi tako ina na gidan yayiwa gidan rumfa gaba ɗayansa.

A da sauri ta buɗe idonta jin an kamo tafin hannunta,
Umaymah kuwa cikin tsantsar jin daɗin da farin ciki maras misaltuwa tace.
“Marhababiki ya binti”. Wani irin azabebben tsinkewar zuciya da firgici da razanine ya daki zuciyar Shatu a lokaci ɗaya.
Da sauri ta ƙara ware idanunta, dan son kallon matar da take jawota tare da cewa.
“Kiyi bismillah ki fito da ƙafar dama, ki riƙe hannuna da kyau ɗiyata, ki kalleni nan nice jagorarki ki taka ƙafarki a inda zakiga na taka tawa”.
Ido ta zuba mata, tare da fitowa a hankali.
Tana fitowa bakin ƙofar Umaymah tasa hannu ta amshi al’kyabbar da Aunty Juwairiyya take miƙa mata.
Kangeta tayi kana tasa mata al’kyabbar, sannan ta gyara mata rufuwarshi da kyau ta rufa mata hularshi. Yadda sam mutun bazai samu damar ganinta ba.

Ga niƙab ga kuma hular al’kyabbar da lu’ulu’u danke reto a fuskarta.
Da sauri Aunty Juwairiyya ta matso tare da cewa.
“Marhabin yar uwarta, Alhamdulillah yau kam na samu yar uwa”.
Adda Rumana ce ta matso kusa da ita tare da yin mgna da fillanci tace.
“Sannu da zuwa Masarautar Joɗa ƙanwata”.
Adda Rumaisa kuwa murmushi yaketayi tare da matsowa, haka suka sata a tsakiya.
Jakadiyarsu kuwa sai bin takun ƙafar Shatu takeyin da ido.

A haka suka zagayeta, kana hadimai suka mara musu baya.

A haka suka isa babban falon Gimbiya Aminatu.
Suna isa Umaymah ta kaita har gabanta ta ajiyeta,
Cikin tsantsar jin daɗi tace.
“Alhamdulillah Gimbiya yau dai ga sabuwar Gimbiya dan yanzu itace amarya ba keba”.
Cikin dariyar jin daɗi Gimbiya Aminatu tasa hannu ta kamo hannun Shatu da Umaymah ke miƙa mata tare da cewa.
“Kishiya ban haushi, ta isa ta zama Gimbiya zakisa yanzu in korata woje”.
Dariya sukayi baki ɗayansu.

Yayinda tuni hadimai mata suketa jere ababen maƙulashe a gaban Shatu.
Danginsu, Zuma, Madarar shanu, Da ƴaƴan itatuwa masu sanyi.
Ita dai Shatu ƙasa tayi da kanta,
tana jin fargaba da kuma tsoron wannan bahagon gidan data shigo.

Su kuwa nan sukayi ta mata hidima da nuna mata so.

Ganin magriba ta ƙara to ne yasa,
Umaymah ta jawo hannunta ta kaita wani ɗaki dake nan kusa dana Gimbiya Aminatu.

Tare da cewa.
“Yauwa ɗiyata kiyi salla. Za’a kawo miki abinci, kada kici komai sai nazo”.
Cikin sanyi ta gyaɗa mata kai.
Ita kuwa Umaymah hannu tasa ta fara zare mata al’kyabbar, koda ta cire mata shi, cikin kula tace.
“Cire niƙab ɗin, babu mai shigowa nan yanzu sai nida Gimbiya Aminatu da Juwairiyya sai Jakadiyarsu”.
A hankali tace.
“To”.
Haka nan taji duk wani yarda na duniya ta sauƙeshi kan wannan kekyawar mata mai fara’ar nan.

A hankali tasa yatsunta ta kamo niƙab ɗin ta ɗin ta yayeshi.

Wasu irin tagwayen numfarfashi Umaymah ta sauƙe tare da cewa.
“Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!”.
Da sauri ta juyo ta ruggume Jakadiyarsu a hankali tace.
“Alhamdulillah Ummin Jabeer itace. Wlh itace”.
Cikin wani irin tarin jin daɗi Jakadiyarsu ta ɗan kalli Shatu, tare da yin murmushi mai cike da ma’anoni.

Jakukkunan dake hannunta ta ajiye, kana ta iso kusa da ita ido ta zubawa fuskarta kana tace.
“Ɗiyata menene sunanki?”.
Cikin yin ƙasa da ido Shatu tace.
“Aysha”.
Kusan a tare sukace masha ALLAH.
Nan Umaymah kam ta juya da sauri ta fita.

Ita kuwa Jakadiyarsu Jabeer shirya mata kayan data shigo dasu takeyi a drower’n.
Tare da bata umurnin taje tayi al’wala.

Umaymah kuwa tana fita kai tsaye Side ɗin Jabeer ta nufa.

Shiru ba kowa, da kamar duk sun tafi masallaci ne.

Aunty Juwairiyya da Hibba kuwa suna sashin Juwairiyyan.
Ummi kuwa na can wurin Shatu.

Kai tsaye ɗakin da nanne masaukin ta, ta nufa.
Bathroom ta faɗa ruwa ta ɗan watsa tare da yin al’wala kana tafito tazo ta kabbarta sallah.

Ita kuwa Shatu zaune take bisa sallayan.
Tunda ta idar da sallan bata tashiba.
Sai kanta data jingina jikin gadon da take gefenshi.
A hankali ta rumtse idanunta tare da motsa laɓɓanta tana karatun al’ƙur’ani cikin sanyin murya, Ummey da Junainah ne suka faɗo mata a rai shine ya sata zubda hawaye wasu na korar wasu.
Kewarsu da begensu, ya tuno mata su Ya Gaini da marigayi ya Lado.
Ummi kuwa itama bisa sallayan take tana lazumi.

A haka har lokacin sallan isha’i yayi.

Jin wata zazzaƙar murya mai matsifar daɗi na karatun.
Hannun tasa ta share hawayenta dan jin karatun takeyi yana ratsa mata zuciya ya tsananta zubar hawayenta.

A hankali ta miƙe itama ta kabbarta sallan isha’i.
Hakama Ummi.

Bayan an idarne. Ummi ta miƙe tsaye ta ninke abin sallan, kana a hankali take taku har kusa da ita.
Cikin sanyi ta zauna bakin gadon tare dasa hannunta tsakiyar kanta a hankali tace.
“AYSHA kuka kikeyi!?.”
Da sauri ta jujjuya kai alamar a a tana mai share hawayenta.
Cikin kula Ummi tace.
“Kuka mana kikeyi, gashi kinata zubda hawaye! Kiyi haƙuri kinji ko Aysha ki bar kuka, in kinji kewan mamanki ki kalleni a matsayinta, in kinji kewar yayarki ki kalli Juwairiyya a matsayinta, in kuma yayu maza kikaji kewarsu ki kalli Jalal da Jamil a matsayinsu.
In wani abu na damunki ki gayawa Sheykh, shine mijinki kuma majiɓancin lamuranki in kinji kewar ƙanwa mace ki kalli Hibba a matsayinta,”.
Bata hafimtar kalaman wannan matar,
bare tasan me take nufi saboda babu mutun ɗaya da ta sani cikin mutanen data kira mata.
Abu ɗaya ta fahimta Sheykh shine wanda wai tace shine mijine ko majiɓancin lamurane, bata sanshiba bai kuma santaba ta ina zai jiɓanci lamuranta,
Shin ta yaya zata zauna a wannan gidan da tun shigowarta take ganin ababe masu ban tsoro.”
Jin tayi shirune yasa.
Ummi shafa bayanta tare da cewa.
“Jikinki na rawa zazzaɓi kikeyi ne?.”
Cikin sanyin murya tace.
“A a sanyi nakeji”.
Da sauri ta ɗan miƙe tare da cewa.
“To bari in rage gudun A/C’n”.
Ragewa tayi kana tazo ta zauna kusa da ita.

Umaymah kuwa tana idar da sallan isha’i, ta miƙe ta dawo sashin Gimbiya Aminatu.
Tayi matuƙar mamaki ganin batun auren Jabeer ya karaɗe masarautarsu gaba ɗaya,
taki wani sashi kawo abincin amarya akeyi.

Ita da kanta da Gimbiya Aminatu sukayi ta shigar da Foodflaks ɗin abincin cikin ɗakin da take suna jerawa a gabanta.

Shi kuwa Sheykh Jabeer bayan an salla.
Ya fito kamar koda yaushe su Jalal na biye dasu a baya.
Haroon kuwa suna tafiya a jere,
suna cikin tafiya duk suka tsaya fuska a haɗe Jabeer ya juyo ya kalli gefen hagunshi da yaji an dafa kafaɗarshi, Jadda ne ya ɗan kalleshi kana ya kauda fuskarshi ba tare da yace mushi komaiba.
Murmushi Jadda yayi cikin sakin fuska yace.
“Ƙarfe tara dai-dai jirginmu zai tashi. Zamu koma da kawunan naku duka”.
Cikin muryar dake nuna cewa yana cikin tsananin ɓacin rai yace.
“Allah kiyaye hanya”. Ya ƙarishe mgnar tare da juyawa yaci gaba da tafiyarshi.

Shi kuwa Jadda murmushi ya kumayi, fahimtar Sheykh yana tsananin fushi da baƙin cikin abinda sukayi mishi.

Lamiɗo ne ya kalli Aminin nashi tare dayi mishi alamun ya barshi.
Su tafi.

Daga nan suka juya duk suka nufi, sashin Lamiɗo, inda aka gama shirya manya-manyan Foodflaks a tsakiyar falonshi bisa wani tattausan Turkey carpet mai masifar kyau da taushi.

Nan suka zauna sukayi Dinner sunayi suna hira,
Tare da yaransu.

Bayan sun gamane, suka miƙe dan tafiya Airport sabinda lokacin tafiyarsu ya kusa.
Kusan a tare suke fito zuwa babban falon dake tsakanin side ɗin Lamiɗo dana Gimbiya Aminatu.

Bayan sun zaunane, Sallama yaje ya sanarwa Gimbiya Aminatu cewa Sarki Jalaluddin yana neman Umaymah da Amaryar Sheykh.

Jin saƙon Sarki Jalaluddin daga bakin hadimanta da Sallama ya isarwa saƙon ne yasa ta miƙe ta nufi ɗakin da Umaymah take.

A cikin ɗakin kuwa, cikin kula Umaymah take gabatarwa Aysha da abin ci dana taɓa ka lashe dana motsa baki.
Adda Rumana kuwa kamar tasa mata abinci har bakinta,
Itako Aysha kanta a sunkuye, ta zubawa kulolin abincin ido tana ganin ikon Allah dake wanzuwa cikin kayayyakin cimar, da sai dai gidan wane da wanen.
Fahimtar kunya ne ya hanata cin komai yasa suka fito falo suka barta, da Umaymah kawai wacce taketa janta a jiki ganin hakane yasa, ta ɗan yarda taci abincin kaɗan.

Suna zaune a nanne Gimbiya Aminatu ta shigo ta sanar musu saƙon sarki Jalaluddin nan, Umaymah ta sake saka mata wata al’kyabbar cikin jin daɗi tace.
“Aysha ki saki jikinki dani, ki gaya min dukkan abinda kikeso, yanzu kinga wurin kakanunki zan kaiki.
Sarki Jalaluddin mahaifina ne, wanda kuma shine mahaifin maman mijinki, ɗaurin auren sukazo shida yayunmu da ƙannenmu maza yanzu zasu koma jiharmu ne.
Kinga wannan kuma Gimbiya Aminatu itace ta haifi mahaifin mijinki.
Kana Sarki Nuruddeen ɗan Sarki Bubayero jikan sarki Joɗa, shine kakan mijinki.
Mu ma mahaifiyarmu na Raye mijinki ne yasa mata suna Sitti, tana jiharmu ita bata samu zuwaba sai daga baya zata zo”.
Ajiyan zuciya tayi tare da kamo hannunta kana taci gaba da cewa.
“Mijinki ɗan babban family ne gaba da bayanshi.
A ƙalla zai ɗaukeki shekaru goma cikin masarautar Joɗa data musulmai baki gama sanin adadin dangi da yawan yan uwan mijinki ta gefen mahaifiyarshi da mahaifinshi ba.
Yanzu muje su ganki ki gansu.”
Cikin sanyi tace.
“To Aunty”.
Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa.
“Ba Aunty ku bace, Mijinki Malam Jabeer yafi yarda da ita fiye da kowa a dangin mahaifiyarshi, Umaymah yake kiranta”.
Kai ta gyaɗa tare da mgnar zuciya.
“Ikon Allah”.
Ita kuwa Umaymah murmushi tayi kana tana hannunta suka fita.
A falo suka samu Jakadiyarsu, da sauri Umaymah tace.
“Yauwa kinga wannan itace Jakadiyarsu, itace ta rainesu tun suna yara, bayan mahaifiyarsu babu wanda yasan halin Jazlaan sama da ita a cikin wannan masarautar, ki kasance mai bin umarnin ta, domin itace idonki cikin wannan masarautar, Jazlaan a matsayin uwa mahaifiya yake kallonta ba baiwar gidansu ba”.
Cikin nitsuwa Aysha ta gyaɗa kai tare da cewa.
“Nagode”.
Ita kuwa Ummi murmushi tayi tare da bin bayansu.

Suna isa bakin ƙofar tayi musu iso bayan ta shiga ta sanar musu da isowarsu.

A hankali suka shiga, cikin nitsuwa take bin takun Umaymah.
Ita kuwa Umaymah har gaban Sarki Jalaluddin da Sarki Nuruddeen taje da ita,
cikin shaƙuwarta dasu, ta ajiyeta a gabansu tare da cewa.
“Jadda ga amaryar Sheykh Jabeer a sanya musu al’barka”.
Murmushi yayi tare da kallon Aysha. Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
“Allah ya sanya al’khairi ya basu zaman lafiya. Allah yasa tazo mana da hasken da zai kore duhun daya meye hasken idanunmu”.
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu.
Uncle Abdulkareem ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace.
“Allah yayi miki al’barka dake da mijinki ya baku zaman lfy mai ɗorewa”.
Kanta ta ƙara sunkuyawa,
Ita kuwa Umaymah matsota tayi tare da cewa.
“Kinga ɗan ɗago kanki ki kallesu.
Kinga ga Mahaifina. Ga Sarki Lamiɗo”.
Sai kuma ta nuna Abba dake zaune cikin murmushi tace.
“Ga wannan shine mahaifin Jabeer mamanshi kuwa sai gobe a bisa ƙaidar masarautar keda shi Jakadiyarsu da Sallama zasuyi muki jagora ku zagaya cikin masarautarsu baki ɗayansu a nuna miki ahlinsu to da ɗakin mamanshi za’a fara kaiki”.
Kinga wannan shine babban Yayanmu sarki mai jiran gado.
Ga kuma wa ƙaninmu Abdulmumin.”
Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.
“A a Khadijah a rana ɗaya kikeso ɗiyar taki tasan komaine? Ai abun da wuya, dole sai a hankali zata gane mu”.
Murmushi Jakadiyarsu tayi tare da cewa.
“Hakane kam. Amman gwara an gabatar mata da manya”.
Sarki Jalaluddin ne ya gyara zamanshi tare da cewa.
“To Khadijah mu yanzu zamu wuce, ke kuma sai yaushe?”.
Murmushi tayi tare da kallon gefen damanta inda Haroon ke zaune da wani kekkyawa mutun mai matsakaici shikara.
Mi kama dashi wanda bisa dukkan alamu babanshi ne.
Kauda kanshi yayi daga kallon da Umaymah keyi mishi, cikin ƙasaita alamun shima jinin sarauta ne, yace.
“Ni kada ki wani kalleni, bance komaiba”.
Murmushi dattawan sukayi baki ɗayansu, Haroon ma murmushin yakeyi.
Ita kuwa Umaymah kauda zance tayi da cewa.
“Yauwa Aysha kinga wannan shine Haroon ɗan uwa kuma aboki amini abokin faɗan Jabeer.
Akwai kuma ɗan yayanmu Ibrahim shine shaƙiƙin Jabeer shi yana Cairo, amman kwanan zai dawo ki ganshi.”
Jadda ne ya kuma tsareta da cewa.
“Khadijah yaushe zaki koma?”.
Cikin sanyi tace.
“Jadda in Abban Haroon ya amince zanyi wata ɗaya rak, sabida ganin yadda lamuran zasu tafi.
tsakanin yaran, ita kanta Aysha tana buƙatar makusanci tare da ita, sabida baƙonci a irin gidajenmu abune mai wuya ga wanda ba irin gidajen ya taso ba”.
Murmushi Abban Haroon yayi tare da cewa.
“Ba laifi na Amince, Amman bazaki ɗauki azumi a nan bada”.
Da sauri tace.
“Na yarda”.
Haroon ne ya ɗan juya idonshi alum lissafi kana yace.
“Ke nan sati uku zakiyi tunda azumin saura wata ɗaya”.
Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa,
Jadda ne ya kalli Jakadiya tare da bata umarnin su tafi ita da Aysha.
Gane abinda yake nufine yasa ta kamo hannun Aysha suka fita. Gimbiya Aminatu na biye dasu a baya.

Gyaran murya Jadda yayi bayan sun fita, cikin nitsuwa da girma ya kalli Umaymah tare da cewa.
“Alhamdulillah Khadijah, aure dai an ɗaura, duk da tarin tsana da ƙin abin da ɗan naki keyi.
Haƙiƙa baya son wannan abun da akayi mishi. Naga fushi da tashin hankali mai tarin yawa a ƙwayar idanunshi da fuskarshi.
Ina da yaƙini bisa halin Jabeer in ya tsani abu tofa ya tsaneshi kenan har gaban abadan, wannan shine babban tashin hankali na,
Sabida yanada lafiya da tsayuwa kan kaifi ɗaya. Ya gayawa kakarshi Sitti babu wani gari na duniya da yakejin ya tsana sama da wannan garin. Yace baya son garin da mutanen garin. Sabida anci mishi zarafi a garin a gaban kafurai an tozarta shiga ta addinin Musulunci”.
Shiru sukayi baki ɗayansu, tabbas sun san hakane mgnar Jadda.
shi kuwa Jadda a hankali yaci gaba da cewa.
“Yanzu kubar Yarinyar a ta kwana a nan.
Kana a ɗan ɗaga kafa har sai an gyara mata inda zata zauna, kamar ko wacce amarya.
Sannan kada kuyi mishi mgnar auren bare ita yarinyar,
in anyi haka fushinsa bazai tsanantaba, zaici gaba da al’amuran rayuwarshi, tunda shi mutum ne mai ibada da kuma aiyuka”.
Murmushi Haroon yayi tare da cewa.
“In dai baza’ayi mishi mgnarta ba, to wallahi mancewa zaiyi da ita da babinta ma gaba ɗaya”.
Lamiɗo ne ya gyara zama tare da cewa.
“Ya isa”.
Murmushi Umaymah tayi sabida ta lura har yau su Lamiɗo basu gama sanin Jabeer da halaiyarsa ba.

Shi dai Jadda nan ya jadadda musu cewa, kada suyiwa Sheykh Jabeer mgnar sai an gama gyara komai na sashinta.
Ko gaisuwar su bari sai bayan kwana uku a zagaya da ita cikin Masarautar.

Nan dai sukayi sallama suka, tafi baki ɗayansu.

Suna tafiya, Umaymah ta koma ɗakin da Aysha take, nan ta samu Ummi na zaune da ita. Nan ta zauna ta suka ɗan yi hira ganin alamun gajiya da bacci a tattare da itane yasa, sukayi mata saida safe suka fita suka tafi.

Ratsawa sukayi wurin Gimbiya Aminatu suka mata saida safe kana suka fita suka tafi.

Cikin tsananin jin daɗi suke tafiya, har suka iso bakin.
Mashigar sashinsa, cikin nitsuwa sukaci gaba da tafiya.
Shiru ba motsin komai suna gab da isa bakin ƙofar, suka tsaya cikin zaro ido, suka kalli Laminu da Gimbiya Saudatu, cikin haɗe fuska da zafi Umaymah tace.
“Aoozubikalimatillahi taaa’ammati minshirin makalaƙa!.”
Cikin tsantsar tsanarta Gimbiya Saudatu tace.
“A kanki hegu masu jajayen kunnuwa”.
Tana faɗin haka taja hannun Laminu suka fita.
Su kuwa Umaymah da sauri sukayi ciki.

A falo suka tsaya. Ba kowa a falon haka yasa tayi sauri ta nufi arear’n Side ɗin Jabeer, a falo ta samu Haroon konce bisa kujera.
Yana ganinta ya tashi zaune.
Cikin gimtse dariyarshi murya a hankali yace.
“Yau duk kayan ahlin masarautar Joɗa sai an yagesu baki ɗayansu.”
Ya ƙarishe mgnar yana nuna mata ƙofar ɗakinshi.

A hankali ta kutsa kai cikin ɗakin tare da yin sallama.
Can ta hangoshi kan gadon yana konce rigingine, idonshi a lumshe,
a hankali takeyin taku tana nufo inda yake.
tare da mgnar zuci.
“Wato harda sharrin Haroon zayiwa ɗan Umaymah”.
A hankali ta zauna bisa bedside drower’n. Idonta ta sauƙe bisa goshinsa, cikin mamaki ta juyo ta fuskanceshi da kyau ganin yadda Goshinsa ke….!

 

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button