Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 21

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

Related Articles

21
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

************
Washe gari Koda aka duba dakin Naufal bayanan ya tafiyarsa ga mum Aisha a gida ta kwana Babu Wanda yake tinanin tanada Saka hannu a tafiyar tasa ko sani Dan kwata kwata baa asibitin ta kwana ba.

Suna cikin wannan mamakin da baqin cikin maamah da Amatu suka farfado Suma Dan haka suka mayarda duk hankalinsu kansu Amatun.

Amatu tinda ta farfado bayan kuka Babu abinda takeyi zuciyarta nauyi take mata sosai musamman mummunan labarin dasuka tadda ya gama zagaya koina.

Maamah ma kukan zuciya takeyi me tsananin ciwo da radadin zuci,
Wannan shine karo na farko dataji Babu inda take buqata da so bayan kebancewa daga wannan duniyar ta masu kudi,

Rayuwar Amatu ta samu tabo me wuyan warkewa duk da baayi mata fyaden ba Amma duniyar daukakan Wanda suke qarqashinsa ta qarasa lalata sauran mutuncin Daya ragewa Amatun tinda gashinan koina an gama watsawa mummunan fyade Akai mata.

Kuka da Hana kowa kusanto inda take yasaka yanayinta sake tsananta tanajin komai da kowa Bata son Gani ko kasancewa dashi.

Maamah ce kawai ke iya rabarta ta rarrasheta duk da itama tata zuciyar quna takeyi tana yanka da azabar qunci da baqin ciki.

Mum Aysha datazo tashin hankalin rashin ganin Danta kawai tayi ta gama masifarta ta juya Takoma gida tana jiran ta inda zasu fuskanci fushi da bacin ran ASH Wanda kusan koina yanzu abinda ya faru din aketa magana wasu na cewa bazasu zabesa ba tinda a gidansa ba Babu adalci ga masu aikinsa bare Al’umma.

Abdul da su Haydar na cikin damuwa da sanyin jiki Mai tsanani na ganin halinda Amatu take ciki da yanda maamah ta kasa cewa komai har lokacin.

Maamah aka fara sallama kafin aka sallami Amatu wadda ta batajin zata iya komawa gidan gaba Daya.

Ita kanta maamah ta Yanke hukuncin bazata iya komawa gidan ba sai Kuma ga Kiran kawu bello da Babu labaran Daya shafi ASH TALBA da basa bi Dan sanin sunada alaqa da gidansa tinda Asmau na can da ‘yayanta dasukaci buri da jiran su zama Wani abin a duniya su fito suce sune dangin mahaifinsu.

Samun wannan mummunan labarin ya girgiza su sosai Dan sun dauka iya irin gidajensu irin wannan yake faruwa sai gashi har gidan masu taka Naira ma Yana faruwa Dan haka kwadayin Asmau ya qare ta dawo gida kawai.

Irin zagi da cin mutuncin da kawu sukai mata a waya tareda gori masu tsananin nauyi ya Saka zuciyarta ta kasa dauka ciwon zuciya na Neman kasheta cikin sanyi Dan haka hankalin Abdul ya sake tashi ya ringa rokon Amatu data sassautawa kanta ko maamah din zata sassautawa tata zuciyar.

Daga asibitin maamah ta Yanke hukuncin tafiya su koma kauye gaba Daya,

Wannan hukuncin na maamah shine ya girgiza duniyar Husnah Dake cikin tsananin tsaka me wuya sbd a Daren Haydar jirginsa ze tashi hakama idan maamah ta tafi tabarta zata iya haukacewa a rashin maamah da Haydar din lokaci Daya Dan haka ta haukace cikin tsananin tashin hankali da kukan rokon kada maamah tabarta rayuwarta zata lalace.

Shi kansa Haydar yashiga damuwa sosai ta halinda Husnah ma zata shiga duk da zuciyarsa sai ta Wani bangaren take samun nutsuwar Amatu ta koma kauye Dan acan zatafi zama safe daga Maza ma gaba Daya har lokacin dawowansa to Amma Kuma Husnah tini ta rikice gwanin tausayi tana rokon kowa kada a tafi a barta ita Daya.

Zuciyar maamah tariga ta Yanke hukuncin tafiya duk da zuciyarta na yanka sosai da ganin halinda Husnah tashiga na fita hayyaci kaman zata zauce Amma batajin zata zauna gasu kawu sunyi rantsuwar saita dawo da AmatulMaleek kauye idan ita bazata dawo ba saisu Amatu sun dawo.,

To idan ta bar Amatu suka koma ita tana nan batasan mezai faruba acan Dan kusan duk abu Daya ne suke tsoro da can da Nan din.

Haydar da zai wuce tin yamma yake asibitin tareda Amatun wadda itama adaidai wannan Gabar kukan rabuwar dashi takeyi Dan kuwa tabbas da Haydar ya Isa auren shi zata aura zuciyarta tafi nutsuwa dashi a aynzu fiyeda kowanne namiji a duniya.

Kuka takeyi sosai Yana rarrashinta kamar zaiyi kukan Shima.

Husnah kuwa har airport ta rakasa tareda Faisal Wanda dole Saiya kula da ita Dan tana cikin wani mummunan hali na kadaici da gariri yanzu.

Qanqame Haydar tayi tana kuka sosai kaman shine yayanta itace kanwarsa,
Shi kansa hawayen yakeyi sosai yake tausayinta Dana kansa duk da tareda Jameel zasuyi tafiyan sbd yariga Dad dinsu isowa.

Husnah Jin takeyi kaman tabi ‘dan uwanta su tafi duk inda zasu tare Amma ba Daman Hakan tayi kuka sosai Wanda yasaka dole tausayinta cika zuciyan Faisal haka ya lallabota suka dawo gida kafin da safe tasake komawa asibiti ta Hana maamah tafiya Dan bazata iya rayuwa babu maamah dinba Babu Haydar Babu mahaifiyarta da tini ta barsu.

Faisal ma daga mansion din gidansa ya wuce sbd dare yayi Saida safe ya koma asibitin.

********karfe Biyar na asuba su mamah suka Isa Tasha daga asibitin bayan Abdul yaje da kansa ya tattaro kayansu da duk abubuwansu da zasu iya tafiya dasu.

Maamah Bata sanar da Husnah ba sbd kaucewa tashin hankalin da zata shiga ita Kuma mum Aisha Daman itace ma da kanta ta sake tsayawa akan tafiyar tasu duk da Basu ce mata komaiba kaman yanda Bata ce musu komaiba gameda abinda Naufal din yayi.

Cikin saa Basu Wani jima ba karfe 6 na safe motarsu ta tashi Babu me walwala a cikinsu hakama Babu me magana suka dauka hanyar tafita me Nisa.

Husnah kuwa lokacinda taje asibiti tinda safe karfe 7 ta Tararda sun wuce sakewa jikinta yayi ta zubewa Faisal da Shima isowansa kenan.

Tashin hankali me tsananin gaske ta shiga da Bata gane komai bayan kawai dawowan maamah gareta kota halin Yaya.

Babban tashin sa’ar da aka samu da sabani shine a ranar ASH ya sauka kasar,
Securities masu yawa suka tarbosa sbd yanda Yan media suka cika suna jefa tambayoyinsu akan abinda ya faru Baya qasar dakuma mataki da adalcin da zaa yiwa me aikinsa wadda akace ‘yar uwar matarsa ce da ‘yarta.

Ganinsa yanda ya kamata Yan media din basuyiba sbd tsananin tsaro da yawan securities dinsa harya shige mota Babu inda ya kalla bare Saka ran tankawarsa hakama kwarjinsa ya hanasu jefa wasu tambayoyin da sukaso.

Koda ya iso Mansion din Daman tini aka qara securities Dan haka Babu Yan jaridu ko a anguwar.

Bangarensa Kai tsaye ya nufa sai kusan bayan awa Daya ya fito cikin wasu kayan daban Dake nuni da yayi wanka.

Kofar palonsa da zata sadasa da Babban palon iyalinsa ya nufa ya fito palon dayake tsit Babu motsin kowa sai AC da qamshin gyaran da Akai Dake tashi.
Kai tsaye dakin Husnah ya nufa wadda ke kwance a dakin ita Daya Babu kowa shiru.

So Daya yayi knocking tareda Murda kofar ya Kalli cikin dakin yaganta kwance a qasan tiles sbd ba zuciyarta kadai ke Mata radadi da zafi ba hatta gangar jikinta da jininta Jin takeyi suna mata zafi sosai.

Lumshe idanuwansa masu haske sosai yayi ahankali tareda Jin zuciyarsa na yanka ya Tako a natse ya nufota cikeda tausayi da tsananin so da kauna irin na Uba da ‘yarsa.

Idanuwanta Dake rife ta Bude ahankali batareda ta motsa ba Jin motsin mutum.

A fafaren qafafuwan datasan Babu me irinsu a gidan idan ba Dad dinta ba Idanuwanta suka fara sauka ta motsa ahankali tareda yunkurawa ta tashi zaune idanuwanta suka sauka akan fuskar Dad din da shi kansa idanuwansa sun Dan fada sbd damuwar yayansa da akaita wannan tashin hankalin bayanan Dan haka yayi alqawarin daga wannan Karan bazai qara tafiya yabarsu a irin wannan rayuwarba zai zauna ya kula da yaransa da kyau tareda inganta rayuwarsu da kansa dakuma taimakon Asmau da kokarinta da bata gajiyawa.

Husnah kasa cewa komai tayi ganinsa bayan hawaye masu tsananin gudu da suka balle mata Kai tsaye abinda tafara Bude Baki ta furta kuka na tsinke mata shine

“Dad muna buqatan Mum kowace iri ce koba mum dinmu ba”

“Dad I can’t live like this,
Dad ka dawo min da maamah,
Dad Ina tsoron kadaice,
Dad maamah ta tafiyarta ta barni,
Haydar ya tafi,
Banda kowa,
Mum Aysha Bata zama,
Banda kowa,
Ina son maamah ta dawo,
Dad Dan Allah kayi aure ko zan samu wadda zata zauna damu batareda tace zata tafiyarta ba kaman Maamah……kuka ne me karfin gaske yazo mata ta soka kanta cikin qafafunta tana Jin tsanani kewan mahaifiyarta ayau fiyeda kullum.

Shi kansa kasa cewa komai yayi ya qaraso a hankali kafin yayi magana ta fada jikinsa tana sake fashewa da Wani kukan sosai zuciyarta na Susa batareda kowa yasan irin radadin datake ji ba Dan kadaici tsananin tsoro da firgici yake Sakata.

Kasa magana Dad din yayi sai Jin dayayi tinaninsa Shima ya tsaya cak da Jin Maamah ta tafiyarta,
Tabarsa da yayansa itama kenan..

Jin yayi kansa ya Sara Dan kuwa komai Yama wuce yanda yake tinani kenan tinda maamah ta tafi to tabbas abin ya girmama.

Kukan da Husnah takeyi sosai Yana shafa bayanta cikin lallashi da kauna me karfi batareda yayi magana ba Dan idan ransa yayi mummunan Baci Baya iya furta ko Kalma Daya shiru yakeyi sedai aga hukuncinsa data Baya.

Ciwo ne me qarfin gaske na zazzabi ya rufe Husnah dole ya kira asibiti aka Aiko likita da nurse wadda zata kula da ita sosai sbd mum Aisha itama a ranar ta silale tayi tafiyar kwana buyi kafin ASH ya Dan huce Dan tasan akwai babbar masifa a kwance.

Kasa rintsewa ASH yayi a Daren Shima sbd kusan a qanqanin lokaci Naufal ya wargaza masa gidansa da rayuwar yarda harma da yar Asmau,
Kewan Abeeda ce Shima ta dawo masa sabuwa Dan kuwa ya tabbatarda harda rashin matarsa ya Sakasa cikin wannan halin Shida yayansa.

Husnah jikinta yaqi sauki gaba Daya ta daga hankalinta ta daga na Dad din akan dawowan maamah Dan tasan idan bata daga hankalinsa sosai ba bazaa dawo mata da maamah da wuri ba,
Shi kansa baida niyar Bata lokaci batareda yaje da kansa ya dawo da Asmau ba sbd Bata adalcin datake buqata itada AmatulMaleek din bisa ga abinda akaiwa Amatu hakama a ayanzu da babu kowa mansion din sai Yan aiki Husnah na tsananin buqatan maamah da mutane a tareda ita.
##MAMUH#

 

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
Vip for each 2k
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button