Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 22

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

Related Articles

22
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

***************
Shirin tafiya kauyensu maamah da kansa yayi a karo na farko rayuwarsa dazai tafi Dan dawowa da ita sbd zai iya rasa yarsa matiqar Asmau Bata dawo ba hakama Yana buqatan yin adalci a lamarin da Naufal ya aikata sbd bazai dawoba alqawari ne ya dauka Saiya daurowa Amatun aure da Naufal idan har Hakan zai rage ciwo da baqin cikin abinda Naufal din yayi.

Husnah dataji tafiyar ta Dad Jin tayi bazata iya daurewa baa tafi da itaba Dan haka ta daure ta samu karfi a tafi da ita zata roki maamah,zatayi mata kuka ta taimaki rayuwarta su dawo Dan zata iya shiga Wani halin daga ita har Dad dinta dashima yake cikin tsananin damuwa yabarwa zuciyarsa ne kawai Amma Shima Yana buqatan macen da zata kula dashi Amma tsananin son Mum dinsu ya hanasa iya kallan kowacce macen bare yayi tinanin qara Wani auren musamman mum dinsu nata kishi me girma a kansa tayaya zata karbi mijinta yayi aure duk ranarda ta tashi.

Faisal da baisan zasuyi tafiyarba Shima Shirin tafiyar yayi harma ya rigasu wucewa.

Dangin mahaifin Naufal ASH ya kira Kai tsaye ya sanar dasu hukuncinsa akan abinda ya faru din Suma Kai tsaye suka amince da maganar auren Dan haka su uku suka yanke shawarar biyo bayan ASH zuwa kauyen idan ankai karshe zaa dauro auren su dawo.

Mum Aisha a bakin kawun Naufal din takejin zancen auren batasan tafara hada kayanta ta dawo Abujan ba hankali a matsanancin tashe Dan kuwa idan aka daurawa Naufal aure da Amatu wlh angama cutatarda ita da duk burinta ita da ‘danta hakama a rasa wadda zaa daurawa Naufal din aure da ita sai Amatun bayan fyaden ma da aketa tashin hankalin anyi beyiba to Menene na daura masa aure da ita.

Shi kansa Naufal din ba kunya ya tattara yafara Shirin dawowa Dan Shima wlh baitaba shirin aureba yanzu Amma idan har andage akan daura masa aure da Amatun to zai amince Kodan ya mayarda yawunsa da ran Daya qwallafa akanta.

Mum Aisha najin abinda ya fada din na idan sun nace ta bari a dauka auren kawai tasan abinda yake nufi da Hakan
Wani mugun baqin cikinsa da takaicinsa ne ya Sakata jefa masa Wani mugun zagi tana cewa

“Kenan haryanxu baka dawo hankalinka ba,
Wai uban me ne Amatun take dashi da matan duniya basuda shi da haryanxu tsinannen abinda kake ji din Bai sauka ba?
Wlh tallahi bazaka aureta ba,
Ko an daura auren saika ana kawota saika mata saki uku,
Kwadayinka bazai taba bari kaga abinda yake gabanka ba,
Me zakayi da Amatun?
Yarinyar da uwarta take wankewa taka uwar toilet?
Yarinyar da sukewa gidanku bauta zaka nacewa sbd masifaffiyar jaraba.

Baqin cikin yawa yayi mata ta saki Wani mummunan tsoki tana kashe wayarta tareda kashewama gaba Daya sbd tayiwa ASH kira yafi ashirin Amma Baa dauki ko Daya ba karshe ma a kashe taji wayar Dan haka ta matsu ta iso Abuja kafin ASH din su wuce kauyen.

******Su maamah tinda suka iso kauyen a ranarda suka dawo
Da yamma suka dauka Dan haka Koda suka iso gida har anfara Kiran sallan magrib a masallatai.

Da kawu bello suka fara cin karo a kofar gida tareda kawu ashiru
Da kallo suka bisu kowa zuciyarsa a wuya da Asmaun,
Ta kwashi Yara sunje yawon kwadayi gidan masu abinda duniya gashinan Babu abinda suka tsinto sai mummunan tozarci Wanda aka gudu Dan kada ‘yayansu su da ake gujewa gashinan Wani a banza ya samu ya farke mata mutunci.

Dayake kawu ashiru yafi fushi da zafi ko gaisuwar asmaun Bai amsaba bare tasu Abdul Wanda yasan Daman ba qaramin tozarcin zasu tararba anan din.

Kawu bello ne kawai ya amsasu Shima Yana bin kayansu da mugun kallon takaici da baqin ciki.

Ciki sukai mutanen gidan kusan kowa nata fitowa ana musu sannu da dawowa wasu Kuma Amatun kawai suke kallo cikeda manufofi da tarin gulma a zuciyarsu,
Wasu kuwa Kai tsaye suke nuna sunsan abinda yasa suka dawo din.

Basuda gurin sauka ma kaman baya dole dakin inna lami suka nufa Wanda yagama mutuwa sbd rashin gyara da tarin kayan Dake cikinsa ga Kuma Yara da Yan mata kusan dai dakin ko sabulun wankanka baka ajiyewa minti Daya zuwa biyar yayi yawa an dauke.

Dayake zuciyoyinsu da hankalinsu acikin damuwa me girma suke Babu Wanda ya damu da yanda dakin yake haka suka Dan gyara suka samu inda suka ajiye nasu akwatinan da ko da ganinsu kasan masu tsadan gaske ne.

Sallah sukai suna sake amsa gaisuwar masu leqowa yi musu barka da dawowa harda abinci aka kawo musu daga sashen amaryar kawu bello Amatu dai Bataci ba hakama maamah daurewa tayi ta tura sbd kaucewa abin magana da zaa gara sakosu gaba dashi suna fama da kansu.

Abdulhameed a waje yaje yasha shayi a gurin me shayin kauyen ya dawo gida tareda shigowa ya dauki kayan bacci da abin rufa daga kayansu ya nufi dakin samarin gidan da warin qatti yagama kame iskar dakin da yanda Babu yanda za’a yi a iya fidda warin Se babban gyara.

Hakanan ya daure Yana dauke numfashinsa ya kwanta cikinsu daga bakin kofar dakin Dan idan yayi ciki da yawa zai iya rasa numfashinsa.

Su maamah acan cikin gida haka sukai kwanan hakuri da damuwa Amma Kuma dole su sabawa kansu tinda sun dawo rayuwar da itace tasu Daman.

Da asuba su kadai ne suka tashi sallah kusan Yan gidan kaf basa tashi sallan asuba sai gari yayi haske suke fitowa ba kunya ba tsoron Allah suke sallah.

Dan haka daga maamah Se Amatu da Abdul din sukai sallah da asuba
Bayan gamawarsu Babu Wanda ya koma bacci Dan Daman Basu Wani samu yin baccinba dole sai ahankali Kuma yanzu zasu Saba da Nan din.

Da safe still anbasu abincin Karin kumallo Hakan dukkaninsu suka daure suka ci sbd fada da kawu bello keyi akan ai bazasu iya cin abincin gidan ba tinda a gidan the grt ASH TALBA suke rayuwa komai na aljannar duniya akwai acan din.

Koda sukai Karin Babu Wanda ya sake bi ta kansu tinda angama musu sannu da zuwa hakama tini samari da matasan gidan suka sauke idanuwansu akan Amatu datake tamkar an kwana qwai da Madara tsaban kyan fata da kyau me sunan kyau da nutsuwa,
Masu aure da marasa auren tini suka fara fitarda maganar su zasu aminta su auretan duk da abinda akayo mata a birnin zasuyi jahadi.

Bayyanar wannan zancen ya daga hankalin maamah da Abdul
Ita Amatu gaba Daya a yanzu Jin takeyi ai rayuwarta tagama mutuwane daga lokacinda Naufal yayi yunqurin yi mata wannan fyaden Kuma har duniya ta sani Babu abinda y rage mata Dan tasan kowama cewa zeyi zai aureta Dan ya taimaka ya rufa mata asiri.

Kawu bello da kawu ashiru harma da sauran qannen mahaifinsu Amatun zauna sukai da maamah sukai mata tatas da maganganu masu tsananin ciwo da radadi a zuci Wanda ya Sakata kukan da Bata taba yi arayuwartaba tin bayan rasuwar Babah sai yau daga qarshe Kuma suka yanke hukuncin daura Amatun aure a satin da Daya daga cikin yaran gidan tinda Babu abinda zasu ajeta a gidan tayi hakama kowa na kallansu da abinda ya farun gwara su aurar da ita a huta.

Wannan shine Mafi girman tashin hankalin da maamah ta shiga a rayuwarta bayan fyaden da aka kusa yiwa Amatun,
Tayaya zasu aurar da Amatu ga yaran gidan da ko Yan uwansu dasuke daki Daya dasu suna iya bibiya tinda gidan taro ne kusan sunayen ma da ake sakawa Yaya sun kusa qarewa.

Kukan da maamah Bata taba yiba a rayuwa shine a cikin kwana biyun da dawowansu takeci kowannen dare ta kwanta,
Ita kanta Amatun batasan me zatai ba sbd zuciyarta tagama daskarewa da Wani irin girmamman tashin hankali da tsoro.

Abdulhameed ma a cikin tashin hankalin yake Yan Jin inama yanada karfin arzikin dauke uwartasu da yar uwarsa subar garin gaba Daya suje Wani gurin suyi rayuwa Amma Sam Shima Yana cikin tashin hankalin wannan auren da ake shirin daurawa Amatu.

A cikin gidan ta bangaren Wanda ma zaa bawa Amatun fada ne ya barke sosai Dan kuwa masu matan da samarin kowa yace yanaso hakama kowa yace bazai hakura ya barwa Wani ba dan haka aka kasa tsayar da mijin ga lokacin da kawu yayi rantsuwar ya Yanke Yanata cikewa.

Kwanansu biyar da dawowa saiga Faisal kamar a mafarki ya dira kauyen cikin tausayi Dan duk ya gama jigata da Nisan tafiyar.

Mamakin zuwansa dukkaninsu kamasu yayi musamman Amatu wadda ta yanke Rahama da sake ganin kowa daga Abujan.

Shi kansa Faisal yashiga mamakin ganin inda suka yanke shawarar dawowa suyi rayuwa ta dindindin.

Abdul ne dole yaje gidan uzaifa daya gama ginawa Tim kafin zuwansu na qasa Wanda aciki zai Saka Amatu idan shi aka bawa ya gyara tareda siyan sabuwar tabarma ya shimfama masa acan ya saukesa.

Ba wata wata zazzabi ya kwantar da Faisal din sbd shine ya janyo motarsa Tim daga Abuja din.

Abdul tareda Faisal ya kwana a gidan Yana kulawa dashi Dan zazzabi me karfin gaske ne ya kamasa sbd Shima Bai Saba da wahala ba.

Washe gari bayan Faisal din yaji sauki yadan warware ya sake zuwa suka gaisa da maamah dasu kawu da basusan waye Faisal din ba kafin a shiga zancen daya kawo Faisal din saiga isowar motacin ASH TALBA da securities dinsa duk da ba masu yawa bane tinda flight suka biyo
Sai motar iyayen Naufal Dake bayan nasa motocin.

Kaf jamaar Dake kauyen idan aka cire su maamah da Faisal Babu Wanda ya taba ganin motacin da suka kawo ASH din Dan kuwa motaci ne dasuke shiga dashi matsu tsadar gaske duk da babu hanyar mota a kauyen sai gasu har cikin kauyen da motacinsu har gaban gidan zuraiar Sanda Fulde.

Maamah batai mamakin zuwan ASH ba sbd tasan bazai taba barinta da yayanta su wulaqanta ba su tozarta Amma zuwansa da iyayen Naufal shine ya Sakata cikin Mafi girman tsoro da mamaki sbd tasan dole da niyar Wani abin sukazo Wanda take da tabbacin idan aure ne bazata taba iya barin AmatulMaleek ta auri Naufal ba Dan haka ta zabi zaman kauyen har tsufa da mutuwarta da Naufal ya auri Amatu.
##MAMUH#

 

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
Vip for each 2k
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
0903318107

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button