Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 29

Sponsored Links

29
Ga mamakin Husnah Dad dinta yafito yaci abinci tareda ita da Abdul Wanda kusan shine yake rage Mata kewan Haydar tin bayan tafiyar Haydar,

Ko a fuska ko a dama Husnah bataga ko Daya a gurin Dad dinta ba da zatai masa maganar auren nasa da bataso da AmatulMaleek data ganin Bai kamata ace tana auren Dad dinta ba hakama maamah bazata sake sakewa ba a gida sbd Bata kaunar auren har ranta itama to Kuma matiqar ba Dan sassaucin Daman magana suka Gani a tareda shi ba Babu me iya magana sedai suyita hadiye maganarsu da damuwarsu har ya musu illa Kila.

Ba sosai yaci abincin ba sbd wannan shine farkon abincin masu aikin gidansa daga na matarsa saina cooks na gidan saina maamah su kadai yake ci Amma yanzu sanin gidan ba Normal yake ba yasa Bazai tsaya Bada Daman korafi ko magana ba.

Related Articles

A natse kaman wanda duk duniya baida damuwa yaci abincin kaman yanda ya Saba,
Yana gamawa ya goge bakinsa yabar dining din.

Abdulhameed hankalinsa kwance yaci abincinsa sosai iya koshinsa kafin Shima ya tashi.

Husnah ma dole abincin taci ta koshi ta tashi ta koma dakinta.

Har dare gidan ba motsin kowa sai masu aiki da suka sake tsaftace dakin cin abincin suka jere na dinner wanda ba abinci ne nauyi bane sedai kaman yanda suka jera kusan haka suka kwashesa Abdul ne kawai yaci abincin,
Husnah tea Tasha
AmatulMaleek ma tea Tasha hakama maamah tea din kawai Tasha shi me gidanma kwata kwata be fito cin abincinba.

Washe gari Babu Wanda ya gansa ya ficewarsa aiki Dan haka har kowa ya gama boyon kansa a daki ya fito sukaci abinci Husnah ce ta fara shiryawa ta ficewarta school Abdulhameed ma fita yayi zuwa Wani gurin.

AmatulMaleek bayan tayi wanka ta Saka doguwar rigar atampa fitowa tayi ta nufi gurin maamah wadda itama ta fito dole sbd sanin ASH din Baya cin abincin masu aiki ta shiga kitchen da kanta.

Amatun ta zuwa gaidata tayi tana tambayarta jikinta.

Amsawa tayi cikin kulawa tana cigaba da aikin dayake gabanta.

Hannu AmatulMaleek din ta miqa tana cewa

“Maamah kawo na tayaki ki huta sbd jikinki”

Numfashi maamah ta sauke tana kokarin hana zuciyarta ganin lefin Amatun akan aure sbd itama ba laifinta bane kaman yanda Abdulhameed ya mata nasiha akan lamarin sosai Kuma tabbas idan Taga laifin AmatulMaleek batai mata adalciba amatsayinta mahaifiyarta,
Abu ne da Akai Wanda ita Amatun kaman auren dole ne,auren kaddara,
Tashin hankali da fushi da qunci bazai kawo salamaba ga abinda suke kalla kaman haramun,Dan haka zatai amfani da zamanta uwa ga Amatun ta nesantata da auren cikin sauki batareda Rai ya Baci ba ko shiga damuwa.

Bata sakarwa Amatun aikin duka ba sedai sukai tare su Farida kuwa sai kaffa kaffa sukeyi da Amatun suna Bata girma ita Sam batama lura ba sbd aikin gabanta kawai takeyi cikin nutsuwa, maamah ce kawai ta lura da komai nasu ya canza gameda Amatun Amma dai itama tayi kaman Bata ganinba sbd kada abin yayi tsayi.

Aikin girkin sukai tare suna gamawa su Farida ne suka jere komai a dining maamah Kam batajin yanzu zata iya cigaba da zuwa cikin gidan sosai sbd kunyar ma ganin kanta takeyi a Mansion din kwata kwata.

Mum Aisha kuwa dai jinya takeyi sosai Dan ko wunin ranar a kwance tayisa cikin wahala da baqin cikin duniya dayake nukurkusanta tanajin kaman ta balbalawa gidan wuta ya cinye gaba daya harda mutanen Dake cikinsa Dan kuwa da Asmau da yarta su zama mamallakan duniyarta ASH gwara ya mutu tun Bai mayar da Amatun matarsa ba kowa ya rasa idan yaso Haydar ya gaje dukiyar ta ubansa duka tinda Husnah batada gadonsa sai abinda ya Bata kyauta tin Raye.

AmatulMaleek kuwa tana komawa dakinta wanka tasake yi tayi sallan Azahar tana idarwa ta fito taci abincin ta ta koma sbd itama kaman yanda Abdul ya sanar mata ASH TALBA ya aureta ne kawai Dan kwantar da kura da tashe tashen hankalin da aketa yi ba lallai zai zai ajeta matarsaba har abada Kila ya Bata Daman komawa karatu tana gamawa ta samu me Sonta yabata Daman yin auren Dan haka ba amfanin quntatawa rayuwarta komai zai wuce.

Tana cikin cin abincin a palon Husnah ta dawo sama sama sukai magana ta wuce daki ta fito cin abincin itama.

Tare sukaci AmatulMaleek tafara gamawa tana barin gurin Dad din Husnahn na shigowa sedai Basu gansa ba qamshinsa sukaji alaman yabita ta kofar palon Daya hada nasa palon da wanna ya wuce Dan haka Husnah ce ta sake gyare table din tsaf da kanta sbd yau abincin maamah ne zaice sosai Kila.

Da daddare ma ba dukansu sukaci abinci ba sbd Amatu bata fito ba sanin da dare tareda iyalinsa yake cin abinci Dan haka taqi fitowa tayi zamanta a daki tea Tasha tayi Shirin bacci ta kwanta.

 

Washe gari bayan Husnah ta fice makaranta tana fitowa ga mamakinta saiga Mr Jameel yazo ya sanar da ita ta shirya ga driver Nan zata ci gaba da zuwa school dinta.

Taji farin cikin Hakan amma nutsuwarta ta Sanya baiga hakan ba Godia tayi masa kawai.

Maamah ta fadawa itama Tayi mata addua Dan haka taje ta shirya 10 ta fito sanye cikin jallabiya maroon da yar handbag dinta kafin ta iso Daya daga cikin securities na gidan ya taso da saurinsa ya Bude mata motar Yana mata barka da fitowa Dan kuwa sukam ita suka sani tinda basusan tsohuwar matar the great ASH TALBA
dinba sbd tini aka sauya sabbin securities masu qarfi da tsanani Dan haka yanzune zasu San matan maigidansu ASH TALBA.

A natse ta shige motan tareda masa Godia driver ma cikin girmamawa ya gaidata tareda Jan motar suka fice zuwa makarantar tasu.

Koda suka Isa makaranta Daman ana kan karatu ne tai tafiyarta Dan haka kusan kwanakin kadan ne tayi missing Dan haka ta Dan maida hankali kawai tasan ba Wani sosai zai mata wuya ba.

Driver be tafi ba har yamma Saida tagama suka fito kusan tareda Husnah itama Saida tayi lectures din yamma kafin suka shiga motan tare batareda Husnah ta tsaya Kiran nata drivern ba.

Har suka iso baifi magana biyu ba zuwa uku sukaiwa juna kowa hankalinsa na kan abinda yakeyi, Husnah wayarta take dubawa
Amatun kuwa Wani littafi take dubawa.

Parking driver din yayi ya fito kaman Amatu tayi Wani yunqurin harya Bude mata motar Yana matsawa gefe.

Daga Amatun har Husnah shiru sukai da mamaki musamman Husnah data kasa yarda da abinda yake Shirin faruwa da rayuwarsu.

Fitowa Amatu tayi a natse tareda masa Godia tana wucewa batareda t Jira Husnah ba da itama ta fito ta nufi ciki zuciyarta na nauyi.

Koda Amatun ta shigo Bata wuce bedroom dinta ba gurin maamah tafara zuwa ta fada mata dawowanta tareda ajiye Jakarta anan dakin tayi alwala tayi sallan laasar tareda cin abincin suna Dan magana Sama sama da maamah din har magrib
anan tayi sallan magrib kafin ta fito ta nufi dakin mum Aisha tai mata ya jiki wadda ko amsawa batai ba Dan taji sauki Amma Babu Wanda tafara tankawa magana a gidan sbd shock din rayuwarta Bai gama sakintaba.

Juyawa tayi ta fice mum din ta bita da Wani irin kallon baqin ciki da tsana wutar zuciyarta na sake balbaluwa Dan kuwa akwai masifa a qasa kwance indai akan auren Nan tafison kowa ya tafi lahira ba shiri.

Amatu na Isa bedroom dinta wanka ta fara yi tayi Shirin bacci har zata kwanta ta Tina gaba Daya yau Bata ga Abdul ba Dan haka ta ziro takalminta ta fito.

Hanyar dakinsa take kokarin nufa taji motsi a dining room Dan haka ta juya ta nufi can din Kai tsaye Dan tasan shi kadai ne zai iya fitowa a wanna lokacin cin abincin dare.

Dayake kowa ya shige ba motsin kowa hakama kusan duk an rage hasken koina,
Kai tsaye ta shiga gurin cin abincin tareda ambatar sunan Abdul din da muryanta me taushi da nutsuwa…..

Dagowa yayi a natse daga tea dayake hadawa Batareda ya iya hadawan ba yayi mata kallo daya da fararen idanuwansa ya mayar dasu kan abinda yakeyi din.

Itama cak ta tsaya a gurin dataken tana sauke idanuwanta qasa tana rasa abin yi sbd taba tsammani ko tinanin shi din bane a daidai wannan lokacin.

Cikin nutsuwa ta Bude Baki ta gaidasa

Batareda ya dago ba ya amsa Yana nuna mata flask din Daya kasa budewa a natse yace

“Bude wannan abin Ina buqatan hot tea din yanzu”

Wani numfashi me Dan nauyi ta hadiye tareda danne rudewanta ta qaraso gurin a natse batareda tace komaiba ta miqa dogayen yatsun hannunta farare akan flask din ta dauka ta Bude a hankali tareda janyo cup ta zuba masa sedai Sam ruwan tea din Babu zafi sosai Wanda da alama tin na safe ne Kokuma Husnah ta Bude tabarsa Bude ya huce tinda baya yiyuwa ace masu aiki Basu kwashe komai suka sake jera wasu ba.

Rasa ya zatayi tayi dole ta Bude Baki kanta a qasa cikin nutsuwa da sanyin murya tace

“Ba zafi,zaa dafo Wani tea din”

Da hannu ya nuna mata kofa Yana mata alamar ta ta kawo wanin sbd Yana buqatan tea din sosai sbd yau be Wani ci abinci ba sbd Taron baqin da yayi akan hanyewarsa daga siyasan nan da Sam batai masa ba idan har sirrin gidanka bazai sake zama sirri ba sbd siyasa Dan haka Baya raayi tattara iyalinsa zaiyima subar qasar.

Kitchen din palon ta nufa ta kunna gas a natse ta sake dafa Wani ruwan tea din da kayan qamshi da lemun tsami kadan sai pure honey ta zubo a wasu gurin daban ta dauko ta kawo.

Har lokacin Yana dining room din gaba Daya qamshinsa har palonsu har kitchen ya gauraya koina sbd yar jimawansa a gurin.

Ajiyewa tayi tareda zubawa a cup ta sake ajiyewa ta juya ta nufi kofa.

Thank you” ya furta can qasan maqoshinsa cikin nutsuwa kafin ya dauko cup din ya Kai bakinsa lips dinsa na Hawa kan cup din ya Dan rufe ido sbd Jin qamshi da zafin tea din zai basa abinda yake buqata ataredi.

Tana baro dining din kasa wucewa tayi dakin Abdul ta koma dakinta ta nemi guri ta kwanta.

Washe gari Mr Jameel ne yazo da kansa tareda wata budurwa da zata girmeta sosai Amma dai batada tabbacin budurwa ce ko matan aure ya hadata da ita akan ita zata kula da ita kwana biyu.

Bata gane wace irin kulawa ba Dan haka Bata iya cewa komaiba Saida suka fita zuwa makaranta suna dawowa Kai tsaye ba gida suka nufa ba gurin siyayyan kayanta suka nufa.
#MAMUH#

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button