Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 62

Sponsored Links

*************
Duk tashin hankalinda Husnah take ciki Bude jajayen idanuwanta tayi ta zubawa kofan dakin Amatun Daya shige.

Maamah ma kusan mutuwar zaune take Neman yi sedai kafin suyi Wani motsi mr Jameel dayake siqe dasu Kiran Farha yayi Yace tace su fito ga motar zuwa airport na jiransu ya fasa bari gobe su tafi yau ze ingizasu Lagos suje su Jira visa daga can su wuce hankalinsu suka ya kwanta Dan idan ba zuwa sukai suka dubo madame Abeeda sukaga halinda take ciki bazasu bari a zauna lafiya ba tinda yanajin komai dayake faruwa a cikin gidan a bakin anty Farha gameda auren.

Mum Aisha ma da isowanta gidan kenan Mr Jameel yace Maza Maza su fito jiransu akeyi jirgi ze tafi ya barsu.

Related Articles

Mamaki me tsananin gaske dukkaninsu suka shiga musamman maamah da mum Aisha da basusan da tasu tafiyar ba tsoro ma ne yake Neman kama mum Aisha Amma Kuma tinda mr Jameel yace tafiyar zasuyi to tabbas ASH ne ya Bada wannan umarnin gashi babu me ikon tambayar dalili sedai Babu Wanda yakeda raayi na tafiyar a cikinsu a dai wannan halin da ake ciki har gwara maamah tanason ganin Abeeda Kam Amma ba yanzu da ake cikin wannan tashin hankalinba sedai Babu gurin musawa ko fasawa.

AmatulMaleek dinma Basu samu Gani ba anty Farha itace ta hado kayan maamah tana sake tausarta da maganganun nasiha da Sam Babu me shigar maamah din tayaya zata bar Amatun a gidan bayan ASH Yana gari.

Kaman wasa sai gasu a mota an wuce dasu airport zuciya fal tashin hankali da mamakin Daya kasa barinsu tantancewa Saida suka daga zuwa Lagos suka tabbatarda dai kuwa tafiyar zasuyi ba Shiri ba sanarwa.

Basu dawo hayyacinsuba Saida suka samu kansu a Lagos tareda anty Farha wadda zata jagoranci tafiyar duk da itama ba shiri Amma ta yarda ta biyosu su tafi din Dan masifar kowannensu yawa ne da ita gwara akaisu gurin Abeedan idan qarasa ta zasuyi da masifarsu su qarasata acan din.

Maamah da mamaki da firgici ya tashi kasheta sai gata a kwance ciwonta ya tashi a Lagos anty Farha taqi fadawa ASH Dan kadama Amatun taji suka kwasheta zuwa asibiti zata warke ta tashi su tafi.

 

*****
AmatulMaleek kuwa batama San su an tattara su kaman kayan kunya ba anbar gidan dasu sbd zazzabi me karfin gaske Daya rufeta hakama Sam ta kasa Dena hawaye sbd tasan maamah yanzu zai yiyu tasan komai gameda mu’amalarta da ASH din.

Duk yanda yake rarrashinta da lallabata sbd zazzabin Daya rufeta Bata iya dawowa daidaiba Dan haka Koda magrib tayi dole aka kira likita tazo ta dubata Batai mata komai ba maganin zazzabi kawai ta Bata tareda rage Mata zafin jikinta ta wuce.

Su khaltume sun gyare gidan tsaf ya koma kaman Babu tashin hankalin da Kai cikinsa yau din sun kunna AC na koina tareda kunna qamshi dasuke tashi a hankali cikin sanyi da nutsuwa.

Abincin ranar ma a dakin Amatun aka Jere musu shi lokacinda ya fita Sallahn ishah.

Bayan dawowansa da kansa ya samu ya lallabata taci abincin kadan tayi wanka ta kwanta.

Kadan yaci abincin Shima ya koshi ya miqe tsaye tareda daukanta suka bar dakin zuwa bangarensa.

Suna zuwa kwantar da ita yayi ya rufe ya wuce toilet ya shige,
Wanka yayo hankalinsa kwance yayo brush da sauran abinda zaiyi ya fito ya shirya cikin kayan bacci da qamshinsa yazo ya kwanta cikin jikinta,

Jin jikinta da zafi sosai ya sanyashi zare rigarsa ya janyota ahankali ya shigar jikinsa ya rungumeta dakyau Yana Jin zafin jikin nata na shigarsa Yana Dan sassauta mata shi.

Bacci sukai a natse har safe tana fama da Dan zazzabin haka suka sake wuni batareda ya fita koinaba Yana kulawa da ita.

Sai da Rana ta fahimci Babu kowa a gidan ta sauko qasa Dan zuwa gurin maamah anan aka sanar mata tin jiyan suka wuce Lagos zasu Greece.

Da mamaki ta dawo sama ta dauko wayarta a bedroom dinta ta Saka Kiran wayar maamah gabanta na faduwa da tafiyar tasu.

Wayar Bata shiga dan haka ta rasa wa zata kira Dan daga mum Aisha har Husnah batasan waye zata iya kiraba tinawa da cewan anty Farha ma ance tana tareda su ya Sakata Kiran anty Farha din tana Jin zuciyarta na shiga damuwa.

Anty Farha Koda Amatun ya kira sun dawo gida da maamah Amma dai bacci takeyi Dan haka Bata sanarwa Amatun ba tadai ce mata tana bacci sbd dan zazzabin damuwa.

Shiru Amatun tayi sbd harga Allah tana tsananin gudun bacin ran mahaifiyarta da damuwarta,
Sam Bata son ganin maamah cikin damuwa da bacin Rai shiyasa ma takejin duk jikinta yayi sanyi da auren Wanda batama San tayaya zata iya cirewa kanta tsananin son ASH TALBA ba daya Riga yayiwa zuciyarta illan da Babu gyara,
Tayaya zata iya Rayuwa batareda shi din ba,gashi maamah da gasken gaske ta tsani auren bare alaqarsu.

Cikin nutsuwa da kulawa anty Farha ta kwantar mata da hankali akan maamah din da fushinta tareda nuna mata hankalin maamah din akan tafiyarsu yake yanzu komai abarsa saisun dawo tukuna.

Daqyar anty Farha ta iya kwantarwa da Amatun hankalin harta samu ta zauna taci abinci sosai Tasha magani ta kwanta zazzabinta Koda yamma tayi ya warke Dan haka Koda ya dawo daga yar fitan da yayi sosai yaji dadin ganinta.

Da daddare kwanan Kwanciyar hankali sukai Dan kuwa duk Wani kalan sanyayyan love ya nuna mata shi musamman data sake narke masa tana rikitasa da sanyin jikinta tana kashesa da idanuwanta.

Washe gari Bai fita ba sai 11 sbd baccin da Basu Wani yi ba da daddare sai bayan asuba suka samu baccin kirki.

Khaltume da sauran masu aikin gaba Daya sun Dena hawowa sama idan har Yana gida sbd sakewa yayi sosai a cikin gidansa Yana rayuwar da little Abeedan ce kawai zata iya fadanta.

Cikin kwanakin da suke gudanar da sabuwar rayuwar da daga shi har ita yanzu ne suke sake sanin matsayi da girman abinda yake zukatansu,

Su maamah kuwa duk kwanakin da sukai a Lagos kafin suka wuce Babu me walwala tafiya ce Akai ta bacin Rai da damuwa Dan kuwa ko Husnah datake Jin tana tsananin son baro gidan zuciyarta ta kasa nutsuwa daga baqin cikin baro Amatu kadai a gidan Kuma Dad dinta na gari,
Ita kanta maamah tashin hankalin dayake cin zuciyarta kenan duk da tana Jin sanyin son ganin Abeeda Amma murnarta a dishe take da baro Amatun Dan haka ta duqufa da fadawa Allah ya kawar da barnar datake gudun afkuwanta.

Mum Aisha dai kusan ita tafiyar tazo mata a biyu ne,
Tana son zuwa ta isarwa da Abeeda labarin auren haka Kuma tana gudun kafin su dawo Wani abu ya faru tsakanin ASH da Amatun Azo a samu ciki su shiga uku su lalace da wannan mugun labarin.

Maamah na amsa wayar Amatu sedai Sam Babu sakewa gaisawa kawai sukeyi tayi mata Se anjima ta kashe wayarta Dan hakan yasa duk tayi waya da maamah din take wuni cikin damuwa da qunci ASH na gane Hakan sai ya hanata kunna wayarta kusan lokuta da dama wayar a kashe take wuni.

******Satinsu uku da tafiya Shima tafiya ta kamasa zuwa South Africa Dan haka suka shirya tareda ita ya tafiyarsa Daga can Shima zai tafi gurin Abeedan Dan haka zasu hade acan dasu Maamah su dawo gaba Daya.

Tafiyansu South Africa ya Sakar mata da sanyin jiki sosai sbd sanyi Daya shigeta hakama zazzabin dare ke damunta kullum idan ba cikin jikinsa ba Bata iya bacci Shima kusan yasan Bata iya baccin sai ajikinsa Dan haka ya Saba kwanciya kwata kwata yanzu ba Riga sbd ita.

Satinsu biyu a South Africa suka fara Shirin wucewa Greece sedai jikinta yafara tsananta daurewa kawai takeyi.

Washe garin ranar da zasu wuce kira yazo masa daga Greece din jikin Abeedan ya tashi sosai haka kawai anrasa meya rikitar da jikin nata Dan haka hankalinsa ya tashi suka wuce ba Shiri.

Koda suka Isa itama Amatun jikinta sai ahankali sosai yake tarairayarta su samu Isa Taga likita duk da ta nace akan sanyi ne kawai.

Da daddare jirginsu ya sauka motan da zata daukesu na zuwa ta kwashesu suka Isa masaukinsa Wanda duka su maamah dasu Husnah acan suke gida ne me Dan girma da kyau da tsari sosai.

Suna isowa anty Farha ce tafara fitowa ta tarbi Amatun wadda tafara karfin halin daurewa tana Hana yanayinta bayyana duk da tanajin jikin.

Maamah Bata gidan tana asibiti itada Husnah Dan haka daga mum Aisha Dake dakinta tana bacci sai Farha.

Sanin anty Farha zata kula da ita sosai ya sakashi barinta a gurinta Bai Wani Bata lokaci ba wanka kawai yayi da salloli ya fito suka wuce asibi Shida mr Jameel ita Kuma ta samu sallah da wanka ta kwanta bacci me qarfi da wahala.

Maamah da Husnah zaune suke a asibitin jigum jigum hankalinsu a tashe da yanayin da Abeeda sai gashi ya iso.

Idanuwa Husnah ta zuba masa tana kallan Wani irin freshness da lafiyayyar hutun Daya qarawa komai nasa kyau da aji da kwarjini,

Maamah kasa kallansa tayi Saida ya iso cikin mutuntawa da girmamawa suka gaisa tana masa barka da zuwa Dan duk basusan da Amatu yazo ba.

Amsawa yayi tareda wucewa Kai tsaye zuwa gurin likitocin Dake Neman ganinsa.

Ya jima sosai a ciki kafin ya fito ya Isa gurin Abeedan wadda ta samu bacci sedai Kuma abinda likitoci suka sanar masa Daya Sakasa farin ciki shine tashin jikinta ya Saka wasu sassan jikinta sun fara aiki Dan suna Saka ran zaa iya fara Sakata wheelchair ana Dan zagayowa da ita.

Su kansu su maamah sunyi farin ciki da wannan cigaban da aka samu sedai Kuma abinda yake tsinkar dasu shine abinda aka fada na cewa duk tsanani kar abari ta shiga shock na Wani abu ko damuwa haka.

Wannan Kalmar itace kalman data Saka zuciyar Husnah tsananin farin ciki me girman gaske bayan tsawon lokaci Dan kuwa wanna gargadin na likitoci na nufin dole Dad ya dakatar da maganar aurensa daga zuwa Wani matsayi na gaba.

Maamah kuwa shiga damuwa da tinanin tayi me zurfi itama Dan kuwa tasan itama wanna gargadin na buqatan itama ta takawa Amatu mugun burki akan komai na gidan ASH da ASH din kansa.

Shi kansa ASH din shiru kawai yayi sbd baisan Wani abu ne zaisa su bawa Abeeda shock ba tinda so sukeyi ta tashi hakama Babu Wani damuwa a rayuwarsu da zasu ce zai Sakata shock.

Se tsakar dare suka dawo gida
Suna shigowa sama ya Haye maamah da Husnah Kuma dakin maamah din suka nufa ga Mafi girman mamakinsu Amatun suka tarar kwance har lokacin bacci takeyi.

Daga maamah har Husnah sakin baki sukai suka kallanta Husnah zuciyarta na harbawa da rikicewan ganin Amatun a daidai lokacinda akace baa buqatan mum dinta da bacin Rai ko labarin bacin Rai komai qanqantarsa sbd barazana ga rayuwarta duk da mum din Bata saniba Amma ai Dad dinta zai iya abinda zata iya fahimtar Wani abin.

Itama maamah nata tinanin kenan tayaya Amatu zata kasance inda Abeeda take duk da Abeedan Bata saniba Amma ai zaa iya samun matsalar magana ko tsautsayi.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

63
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button