Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 28

Sponsored Links

28
Assalamu Alaikum
Hajiyata kinada labarin kayan Egypt da muke kawowa kuwa to in baki saniba matso kusa kiji,
AINAM DRINKS AND MORE mun kawo muku kaya na gani na fada na gayu wainda sai wance da wance ake gani dasu ba kano made bane kunsan a koda yaushe burinmu mu kawo muku unique abu.
Idan muka ce kayan Egypt muna nufin na Egypt din fa,
kayan manyan mata,manyan Yan mata,mata masu aji,matan dasukasan kayan alfarma,
Available ne ba jira zakiyi akawo ba muna bada sari muna aikawa koina,duk abinda kike bukata hajiyata ki latsoni kawai 08146766440
Ko baki siyaba yanzu kiyi saving number ta murika ganin status din juna sbd idan kina Gani zakisan namu ba irin nasu bane.
Nagode

 

************
Naufal Jin yayi zuciyarsa na daukan Wani zafi da takaici tareda baqin cikin idan har Wani aka aurawa Amatun ba shi ba bare yasan bazai wuce Barr Faisal uban naci da taurin Kai ba.

Related Articles

Mum Aisha ruwa ta ringa sha tana godewa Allah a Fili da zuciyarta Dan itama tasan bazai wuce Barr Faisal dinba tinda sun San Shima dole bazai iya zama baibi Amatun kauyen ba,.Dan haka itadai koma wanene su je su qarata Allah yasa auren bazai mutu ba sai mutuwa,
Allah yasa auren ya dauru Babu abinda zai tabasa sbd Amatun tayita zamanta acan Babu ranar dawowa rayuwar gidan sun huta
Shi kansa Naufal Daya qwallafa mata Rai tasan ranta yanzu zai samu Nutsuwan Bai ga Amatun ba bare ya Kuma janyo mata maganar da zata kaisu babbar halaka a hannun ASH.

Naufal miqewa yayi batareda yace komaiba zai bar palon mum Aisha ya kallesa da sauri tana cewa

“Ina zaka?
Kasan dai Tinda su Sulaiman sunbaro dole ASH Shima yabaro Kuma inda yake Yana hanyar dawowa gidan Nan ko?
Tinda Bada Kai aka daura ba Maza ka hada kayanka ka koma gidan zayyan kafin komai ya lafa sai na basa hakuri muga idan zaa samu sassaucin da kaima zaka iya zuwa Basa hakurin ya Sauko tukuna ka dawo.

Sai a lokacin Shima fargaban dawowan ASH din ya shigesa Dan haka cikin fargaba ya Kalli mum din yace

“Mum idan ASH ya sameni gidan Nan zai iya miqani inda sai kema kin manta kamanni na kafin a fito Miki Dani ki Ganni”

Miqewa tsaye mum din tayi tana cewa

“Muje kayi sauri ka hada kayanka ka fice sbd jirgi zai biyo kowane time zakaji ya iso.”

Fitowa sukai da sauri zuwa dakin Naufal din Shida mum din suna rige rigen Saka kayansa a akwatinansa da duka ya dawo dasu harya Jere kayansa Yana jiran amaryarsa.

Cikin sauri da gaggawa suke hada kayan batareda tsarawa ba Dan haka kayan kusan duk a hargitse suka gama hadasu suka janyo zuwa mota tana sake maimaita cewa

“Wallahi Naufal ka nutsu kafin na cire hannuwana a lamarinka,
idan zaka koyi dangana da iya hadiye kwadayika akan mata kafin mu samu sassaucin fushin ASH Wanda ba magana zaiyiba Amma hukuncinsa abin tsoro ne,
dan kaje ka sake debo Wani abin maganar da zai dawo kunnen ASH wlh fitarda hannuna zanyi tinda Kai bakasan ana koshi da gundura da komai na duniya ba”

Harabar gidan suke kokarin Isa aka Bude makeken gate din Mansion din motocin ASH suka shiga a Jere sukai parking.

Maamah da Husnah ne suka fara fitowa kafin Abdul Daya fito ya nufi bayan motacin Yana fidda Yan kayan dasuka taho dasu Dan kusan duk kayansu sun barosu a kauyen.

AmatulMaleek ce ta fito karshe kanta Bai juya koina ba sbd Bata iya kallan kowa itama hanyar sashensu take kokarin nufa Kai tsaye saiga mum Aisha da Naufal sun fito cikin sauri.

Cak kowannensu ya tsaya cikeda tsoro da firgici,

Naufal daya sauke idanuwansa akanta ya Sakata Jin gabanta yayi mummunan faduwa take jikinta ya dauki rawa da qarfi idanuwanta take sukai mata naufi ganinta na ragewa sbd komai dawo mata yayi musamman yanda yake kallanta da duka idanuwansa da abinda yake zuciyarsa.

Kasa daukanta kafafunta ke Neman yi tayi Baya ahankali se Jin tayi anyi mata katangar data hana jirin dubanta.

ASH TALBA ne da kansa ya tareta da kansa tareda miqa hannunsa Daya ya qarasa tareda batareda ya kalleta ba.

Mum Aisha da Naufal ya zubawa idanuwansa dasuka kusan Saka mum Aisha sumewa agurin yayi musu kallo daya Babu Kalma ko Daya ya juya da Amatu a hannunsa zuwa sashen dayake matarsa da yayansa.

AmatulMaleek gaba Daya Bata hayyacinta sbd firgicin ganin Naufal datai Dan haka Bata tantance waye ne ya hadata da jikinsa ba saima sake qanqamesa datai Bata ko ganin gabanta har suka bar harabar gidan gaba Daya.

A harabar gidan kusan duk Wanda yake da alaqa da ASH dakuma Wanda yakeda alaqa da AmatulMaleek kusan kowa mutuwar tsaye yayi cikin rawar jiki da tashin hankalin da baa Saka masa rana ba.

Mum Aisha da Naufal da duk Wanda yake gurin tsaye yasan Kai tsaye magana ce Mai hade da mummunan mataki ASH yafadawa mum Aisha da Naufal batareda Bude Baki ya furta ba cewan shine Wanda igiyoyin auren Amatu suke hannunsa.

Maamah da Husnah kuwa kusan kasa motsawa sukai sbd tashin hankali da mamaki me girma.

Abdulhameed da ganin Naufal tin farko ya sakashi baro inda yake da sauri zai nufi yar uwarsa ya Bata kariya kafin kyaftawan ido kaman daga sama kowannensu baiga isowan ASH dinba sai ganin Amatun sukai a jikinsa dakatawa yayi batareda ya qarasaba sbd da alama Amatun Bata buqatan kowa.

Mum Aisha kuwa jikinta ne ya dauki rawa gaba daya abinda tagani a gabanta din ya faru bame taba yiyuwa bane har abadan abada,

Naufal ma sakin kayan hannunsa yayi jikinsa na fito da zufa koina yana kallan mum dinsa Dan shi Kam komai ya kasa fahimta ita yake jiran ta fahimtar dashi Dan kuwa dai Shima hankalinsa ma ya kasa daukan abinda idanuwansa suka ganar masa AmatulMaleek a jikin ASH TALBA.

Maamah mum ta kalla bakinta da jikinta na rawa kalmomin a rarrabe tace

“Asmau Wa kika aurawa ‘yarki?

Kam Husnah wadda idanuwanta suka ciko da hawaye ta mayarda kallanta muryanta na sake rarrabewa tace

“Husnah me na Gani?
Me aka aikota a kauyen??
Waye ya auri Amatun??

Hawayen Dake cike da idanuwan Husnah ne suka gangaro kan fuskarta batareda ta Kalli mum Aisha din ba tace

“AmatulMaleek da Dad aka daura aurenta,
Amatu ta zama matar Dad…..

Jiri ne ya dibi mum Aisha ta fara ganin duhu qafafunta tini suka kasa daukanta ta zube a gurin tana rintse idanuwanta da budewa ko duhun datake Gani sai washe.

Naufal da wutar komai na jikinsa ta dauke rasa tinanin kamawa yayi sai rawa da jikinsa ya dauka tareda tiririn me qarfin gaske Amma dai abinda zai fara shine barin gidan tukuna sbd tsoro da firgici.

Ko mum dinsa baibi ta Kai ba ya ja kayansa ya Isa motarsa ko Gani bayayi sosai ya jefa kayansa ya fada motan yabar gidan jikinsa Babu inda Baya rawa da daukan zafi sosai.

Maamah data rasa abin fada ko yi itama ja idanuwanta sukai tayi gaba zuwa dakinta Abdul na bayanta da kayanta.

Tana shiga kayanta kawai ya ajiye mata ya fita da nasa zuwa dakin Haydar da yanzu shi kadai zaiyi rayuwa a cikinsa,.hakama kayan Amatu Bai aje a dakin maamah dinba dasu ya fito ya nufi cikin Mansion dasu.

Kai tsaye dakinsa yafara shiga ya aje nasa kayan kafin yayo ciki Dana Amatun.

A babban main palon ba kowa sbd Amatu Kai tsaye babban bedroom din Dake maqale Dana Abeeda Wanda ita na Abeedan Palo ne lafiyayye da bedroom a cikinsa Wanda bayajin akwai macen da zata maye gurbin komai na Abeeda a rayuwarsa.

Bedroom din ya kaita har bakin gadon dakin ya janye jikinsa daga nata batareda ya juyoba ya fice daga dakin zuwa bangarensa.

Saida ya fice daga dakin ta iya Bude idanuwanta har lokacin hannuwanta na rawa kaman yanda zuciyarta ke rawa cikin damuwa da tsoro.

Dakin datake ta dago ta kalla Tagane inda take take ta zame bakin gadon tana rintse idanuwanta da sai alokacin suka ciko da hawayen da batasan Kona ganin Naufal bane Kona shigowarta wanna rayuwar bace.

Abdulhameed ne yayi knocking dakin tareda Kiran sunanta ahankali yace mata ga kayanta.

Kasa tasowa tayi kaman yanda ta kasa iya Bude Baki Tayi magana dole shine ya shigo ya ajiye mata kayan ya fice batareda ya iya ce mata komaiba Shima sbd yanzu Kam kowa dole ya fuskanci sabuwar rayuwar Dake gabansa.

Mum Aisha dole su Farida masu aiki ne suka kamota suka dawo ciki da ita Dan kuwa jininta ya Haye sosai dole Abdul ne su Farida suka iya sanarwa Dan shine kawai suka ga fuskarsa a gidan
Shine ya kira likitan gidan yazo ya duba mum Aisha da take Takoma mara lafiyar qarfi da yaji Dan kuwa sosai jinin ya hau gashi yaqi sauka sbd tashin hankalin dayake zuciyarta yaqi sauka sai daka hada da alluran bacci da magani.

Su Farida aikin abincin sukahau duk da sun San Mai gidan Baya cin abincinsu baima taba Ciba maamah ce kawai ke masa abinci Amma yau maamah din ko dakinta Bata iya fitowa tinda suka iso ta shige tayi sallan Azahar da lokacinta yayi ta zauna shiru daki tana lazimi Dan idan ma ta fito batasan tayaya zata iya kallan gidan Aminiyarta yar uwarta da basuda tamkar juna Amma yau an wayi gari ‘yarta data Haifa ace itace zata zama kishiyar Abeeda???
Innalillahi wainna ilaihirrajiun” wannan kalman itace taketa firtawa a duk lokacinda ta ambaci auren.

Tsaf su Farida suka shirya lafiyayyan abinci da drinks a dining tareda cutleries masu tsadan gaske suka sake tsaftace koina a gidan duk da kusan duk bayan awanni ake sake gyarewa.

Gidan tsit har bayan laasar kafin kowa ya tashi daga baccin bacin Rai da rashin mafita sukai wanka da sallah,
Husnah ce ta fara fitowa kafin Abdul sai Amatun daga baya wadda Bata iya cin abincin ba drink kawai ta sha ta komawarta daki Dan itama ta rasa ta Ina zata iya wanna rayuwar ta auren kaddarar Daya sameta.
#MAMUH#
#LA HOT
#AMATULMALEEK
#ROMANCE
#HOT LOVE
#ABEEDA TALBA

 

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button