Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 35

Sponsored Links

Kasa dagowa tayi a shafa maganin saurin gurin dayake ta gurin muyanta daga gaba zuwa kirjinta daga sama saman,
Shi kansa bayajin Yana buqatan shafawa har can din duk da ya lura akwai konuwar har agurin Amma Kuma bazai iya barinta taci gaba da Shan wannan wahalan konuwar ba,

Ahankali ya Dora hannunta a kafadanta zai juyo da ita tayi saurin rufe idanuwanta tana kasa juyowa sedai batada qarfi ko kuzarin iya Hana kanta juyowan.

Juyowan da yayi da ita har lokacin hannunta Daya nakan kirjinta data rufe da abin rufa.

Related Articles

Shi kansa Bai kalleta sosaiba gurin kawai ya kalla Yana Kai hannunsa ya shafa maganin ahankali,

Rintse idanuwanta ta sake yi tana juyar da kanta gefe cikin sanyi sedai juyawanta ya Sanya numfashin data fitar me dumi ya sauka acikin wuyansa a hankali.

Shiru yayi tareda dakatawa daga shafa maganin Yana dauke hannunsa daga jikinta batareda ya Kalli fuskartaba ya gyara mata Kwanciyar tareda saukowa a natse nufi toilet ya wanko hannunsa ya goge ya fito tareda kashe wutan dakin ya koma ya kwanta batareda kowa ya sake motsi a dakinbata suka koma bacci Wanda kusan Babu Wanda ya koma,sai guraren asuba ita ta samu baccin ya dauketa shikuwa Saida yayi asuba ya koma baccin.

Saida gari ya fara haske ta samu tayi sallah ta kasa komawa kan gadon ta fito Palo ta zauna shiru tareda Nisa a tinani daga qarshe a kan kujera bacci ya sake daukanta a zaune.

Qamshinsa Daya cika hancinta ya farkar da ita tareda tabbatarda Shima ya tashi Dan haka ta tashi tana Dan gyara zamanta ko gama wartsakewa bataiba ya fito a shirye kyakkyawar fuskarsa sai daukan ido takeyi komai nasa a tsare kudi ne kawai ke nuna kansu a jikinsa Tako Ina.

Idanuwansa akanta ya saukesu Ya kalleta tayi qasa da Kai cikin sanyi ta gaidasa.

Kafin ya amsa gaisuwar cikin nutsuwa jikinta ya fara tambaya ta amsa a natsen itama.

Abinci aka kawo zaa Jere ta miqe ta shige seda aka gama jerawa ta fito da kansa ya tsaya Saida Tasha magani bayan taci abinci kafin ya fice.

Bayan fitarsa ajiyan zuciya ta sauke ahankali ta Dan bari abincin ya fada mata kafin taje ta shiga wanka.

Ko data fito an gyare koina dakin sai qamshi da sanyi me dadi ke tashi koina Dan haka tana shiryawa da kanta ta shafa maganin inda hannunta yake kaiwa ta dawo ta zauna tana kallan dole sbd batajin rayuwartama gaba Daya Bata Kuma San me zatayi ba ga jikin nata da sauki ba laifi.

Ita kadai ta wuni idan lokacin sallah yayi ta tashi tayi ta dawo ta zauna ko ta kwanta ta tashi harsai yamma tayi yau da wuri ya dawo sbd jikin nata Dan haka Yana dawowa ta zauna Palo tasake shiga dakin ba Saida ya fito cin abincin dare.

A tare sukaci abincin ya sake Sakata Shan magani tana sha ta shige.

Wanka tayi ta kwanta take bacci ya dauketa,

Ya Dade be shigoba sai dare sosai ya shigo yayi duk abinda zeyi ya kwanta
Yau din Bata tashi ba Dan haka ya samu baccin nutsuwa.

Da asuba kusan tare sukai sallah Takoma Palo kaman jiyan Saida ya fita Takoma daki.

Yau dayake ya lura data ji sauki ba laifi bayan fitarsu mota aka Aiko ta fita da ita.

Batasan koina ba Dan haka yawon sama sama sukayo driver ya dawo da ita taci abinci kawai tayi wanka ta kwanta baccin Rana.

Ta Dena mamakin yanda maamah ta manta da ita zatace ko shareta hakama ta tsaya kallan rayuwar datake Kai a yanzu,
Abu Daya data tabbatar shine aure dai yahau kanta ko Bata so tinda har kaddara tasa ta kwana a guri Daya da mutumin da ko hanyar dakin baccinsa Bata taba bi ba a gidansa,.hakama Dad din Haydar Kuma mijin amaniya yar uwar mahaifiyarta.

A cikin kwana biyu saima ta fara samun nutsuwa da Kwanciyar hankalin data rasa mansion,
Babu abinda takeyi sai hutawa duk da tana cikin damuwa wasu lokutan da kadaici tareda kewan maamah dasu Haydar.

Shi kansa yanzu ya gama abinda ya kawosa Dan haka tafiyarsa Ghana tana Dan Neman fasuwa Dan haka ya dakata tukuna su gama duba lamarin idan tafiyar zata yiyu ya wuce kada yayi saurin komawa Dan haka Baya fita koina hutawa yakeyi sosai Shima.

Bayan gaisuwa da serving dinsa abinci sai jikinta da kusan koyaushe shine abinda yake tambayarta Babu abinda yake hadasu.

Abu daya ne dukkaninsu suka kasa sabawa dashi ko sakewa dashi shine zama guri Daya da juna duk da shi a nasa bangaren me sauki ne Dan Sam mantawa yakeyi wasu lokutan da akwai wanzuwarta.

Ita kanta ta fahimci so da dama baya noticing na akwai mutum a tareda dashi Dan haka ta hutarda kanta daga takura na rakubewa.

Abu Daya ne yake Dan kokarin fara sabawa dashi a kwana biyun shine yanayin serving na abincinsa a natse datake da Kuma duk yanda ake kawo ruwan sanyi tana sauyawa masa zuwa mara sanyi batareda tasan cewan Daman bayason ruwan sanyin ba
Sai Kuma yawan kukan darenta da Shima ya fara sabawa dashi sbd haka kawai ko qaiqayi wutanta Daya fara warkewa yayi mata sai hawaye sbd ta Saba maamah kusan komai idan suna dakinsu ita ke Mata sbd a dakinsu ne kawai take uwarsu tana fitowa uwar Husnah ce Dan haka ya fara sabawa da wannan kananun motsin nata na dare Tana farawa farawa zai kama hannunta daya cikin nasa zatai shiru tana sedai Kuma shikenan baccinta ya Yanke haka nasa Se Kuma asuba shiyasa suna sallah suke baccin safe sosai abinda Sam Bai Saba dashi ba a rayuwarsa wato baccin na safe.

Ita Kuma a nata bangaren qamshinsa ne abinda hancinta ya fara sabawa dashi da kuka taushi da dumin fatar hannunsa da kusan duk dare yake kama Nata hannun.

Mr Jameel Dayaga Mai gidan nasa na samun hutun safe da Baya samu sai Hakan ya Sakasa Jin nutsuwa sbd babban farin cikinsa shine ASH din ya samu nutsuw ta rayuwa da Kwanciyar hankali,
Koyaushe rayuwarsa Babu kulaw daga inda y kamata sai aiki sai tafiya Dan haka ya ringa Jan maganar tafiya Ghana din bayan yasan ta lalace babuta Amma ya kasa tabbatarwa da ASH din haka Dan ya sake hutawa.

AmatulMaleek na buqatan kayan sawa Dan haka Koda mr Jameel yayi magana da Farha a waya ita ta zaba kayan da yayi shopping ta online aka kawo kallo daya Amatun tawa kayan ta ajiyesu.

Kayan baccin ciki kawai tayi amfani dashi dayake Riga da wando ne masu tsayi Kuma masu santsi duk da tasan zasuyi kudi sosai Amma dai basuda wani hayaniya.

Ahankali ahankali Saida suka share kwana Tara a lag din kafin suka dawo zuwa lokacin kusan duk yanda nesancinsu da juna yake ya Dan Ragu Dan kuwa so biyu tana waya da Abdul da wayar ASH din sedai bata iya magana da Haydar ba Shima Abdul din Bai bawa Haydar wayar ba sbd kada Haydar din yaga da wayar Dad dinsa Amatun tayi magana dasu.

Shi kansa Abdulhameed yayi mamakin jinta da wayar Dad din Amma Kuma ba Daman tambaya haka suka gama magana Sama sama.

Jirginsu ya sauka abuja kusan mota uku ce tazo daukansa daga airport din suka nufi sabon mansion dinsa Kai tsaye.

Batai mamaki ba sbd tayita jinsa a waya Yana maganar sabon mansion din da wasu abubuwan da Mr Jameel ke tambayarsa yanda zaayi.

Mansion ne me girma kaman wancan hakama wannan kusan shi kadaine ya sama Se iyalinsa extra bedrooms din baqi da irinsu mum Aisha sune a qasa sai penthouse Dake can sama kwata kwata wannan gurin zuwansa ne shi kadai.

Maamah bangarenta na musamman Akai mata Palo and bedroom gefen bangarensu Haydar da Abdul idan sun dawo sai bangaren masu aiki a bayan nata.

Babu tsadaddiyar sabuwar rayuwar Jin dadin duniyar da baa Saka ba a mansion din,
Komai na cikinsa kudi ne suka daku kafin suka siyesa,
Komai na sabon mansion din ya doke na tsohon duk da tsohon ma kusan wata aljannar duniyar ne.

Komai an zuba Amma Babu Wanda aka daukowa kayansa kowa Saiya dawo ya dauko da kansa sbd Bai Bada Daman a shiga bedrooms na kowa ba abarwa kowa sirrinsa ya dauko da kansa.

Kayan Amatu ne kawai aka dauko sbd itama Babu abinda zaisa ya bari ta bi ko ta hanyar gidan Dan kawar mata da duk Wani memory mara dadi na gidan.

Farha ce tayi parking na kayan Amatu duka ta Kai mata aka Jere mata komai kaman tana Nan haka Suma su Karima tini aka kwashesu zuwa sabon mansion,
Khaltume ma andawo da ita bakin aikinta Dan haka ma aikatan suka Qaru,
Karima a iya me aikin AmatulMaleek take sauran ma’aikatan Kuma tini aka rarraba musu aiki Wanda wannan aikin na kulawa da duka masu aikin mansion din ya dawo hannun Farha Kuma bata daukan nonsense kana wasa da aikinka zata saukeka a dauki Wani Dan haka kowa ya sake shiga taitayinsu Daman Kuma sunsan baa wasa da aiki ko kadan a gidan Dan haka komai ya qara daukan tsanani.

Bedroom din Amatu a sama yake guri Daya da Husnah sbd palonsu Daya kowa da bedroom dinsa saina mum din Husnah din dayake gefen nasu shikuma Palo babba da bedroom set qaton dining room Wanda shine yakeda kofar da zata kaika palon Mai mansion din da komai nasa yake dabam.

Dawowan Amatu da Mai gidan ya sanya masu aikin sake nutsuwa kan ayyukansu,
Ganin Farha na gidan Bata wuceba ya Saka Amatu farin cikin ganinta tana cewa

“Anty Farha nayi missing fadanki kwana biyu”

Dariya Farha tayi tana kallan yanda tayi Dan fresh na hutun data samu zallansa Babu aikin komai tace

“Daga tafiya Se kashe waya Kuma Am”

Rasa abin fada tayi sbd ta rasa wayarta ne a wutan Daya faru batamasan Yaya aka qarasaba bare.

Su khaltume ne tareda sauran masu aikin duka suka shigo cikin girmamawa sukai mata barka da dawowa tareda mata sannu da jiki da fatan samun lafiya dorarriya.

Cikin nutsuwa da kulawa ta amsa tana gaidasu itama sbd Bata Saba da Hakan da suke mata ba.

Bayan ficewarsu sama ta Haye ta shiga bedroom dinta tareda ajiye handbag din hannunta tana Dan kallan dakin da ita kanta takasa yarda da nata dinne Amma Kuma zuwa yanzu tasan rayuwa ma koyaya tazo batada zabi bayan karbanta.

Alwala ta fara yowa tayi sallan laasar tana idarwa ta kwanta bacci duk da Bata tareda gajiyan komai.

Sai kusan magrib ta tashi
Toilet ta sake shiga Tayo alwala ta fito tayi sallah,

Bayan ta gama wanka tayi jikinta ya sake sakewa ta Saka straight gown black ta Roba me tsada ta Sako slippers ta sauko qamshinta me sanyi na tashi.

Yunwa takeji Dan haka kitchen take kokarin nufa saiga khaltume Farida na bayanta da kayan abinci zaa shirya abincin dare a dining.

Ganin Hakan ta nufi kitchen da kanta San ganin ko zata iya dafa masa tea din dayake sha din.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button