Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 51

Amatulmaleek 51

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

Related Articles

51
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

**************
Daga Husnah har mum Aisha idanuwansu akan Amatun suke fatar jikinta na daukan idanuwansu sbd Babu Wanda ya taba ganinta a Hakan acikinsu,Basu dauka kyau da lafiyayyar jiki har haka ne da ita ba,

Mum Aisha kallan qurullan datake mata Se yanzu ne take jin tausayin Naufal Ashe abinda yasashi nacewa Amatun kenan sbd ganin asalin kyanta da Kila shine kadai ya taba ganinsa gashinan an sabauta mata shi sbd wannan kyan Dan macijin,

Husnah ma kuwa kasa dauke idanuwanta tayi daga kan Amatun Babu abinda yake jikin Amatun da Bai tsole idanuwanta ba ya tokare kirjinta Dan kuwa da ace Amatun da gaske zata zama matan Dad dinta kishiyar mum dinta zata iya zaucewa Dan Taya mum dinta kishi sbd da ba ita din yarinya ce ga zama matar Dad dinta ba da tabbas Amatun zata iya zautar da Dad dinta idan ya ganta ahakan,

Anty Farha ce ganin duk sun rude sunma rasa me ya kawosu bare magana ta nufi wardrobe zata daukowa Amatun rigar da zata Saka aka Bude kofar bedroom din cikin nutsuwa tareda turowa
Kaman a mafarki dukkaninsu qamshinsa ya sakasu juyawa ga kofar gaba dayansu.

ASH TALBA ne da kansa ya Bude kofar bedroom din Yana sanye da kayan Daya fita dasu tin safe hakama qafafunsa ba slippers bane Da Yana dawowa gida yake zare takarminsa ya Saka slippers dinsa masu taushi da tsada dasu yake yawon cikin gidansa Dan sakewa.

Da alama dawowansa mansion din kenan Kokuma daga mota Kai tsaye Nan din ya fara zuwa.

Mamaki ne a kan fuskan kowannensu Banda Farha data ji sanyi da farin cikin ganinsa zuwa duba Amatun dasuka cire Rai da zuwan nasa,

Maamah Amatu ta juyo ahankali ta kalla da idanuwanta dasuka cika da mamaki Amma tana boyewa,

Amatun kaman yanda Bata dago ta Kalli su Husnah ba bayan shigowansu hakama yanzu din Bata Kalli kofarba duk da qamshinsa ya bata tabbacin waye din y shigo dakin.

Mum Aisha Baki take Neman saki zarginta na son sake tabbata sedai Kuma itama dole ta danne nata mamaki da tashin hankalin tana boyewa kaman yanda maamah tayi.

Husnah ce ta kasa boye mamaki da firgicinta harma da baqin cikin dayake neman mamayeta na ganin Dad dinta a dakin Amatun,duk da tasan bedroom dinta zai tafi kila ya zo Nan din.

Cikin kokarin daidaita kanta kada ta bayyanarda abinda takeji a gabansa tace

“Dad ba Nan ne bedroom dina ba,
Kuma naji sauki sosai kana fita na farfado na…..

Idanuwansa Dasukai ciki ciki da pressure datai masa yawa ya dauke daga Amatun Daya zubawa su tin shigowansa ya watsawa Husnah ahankali ya furta

“Husnah kuje idan na fito zamuyi maganan zan duba Abeeda I have a flight to catch”

Yankewa maganar Husnah tayi tana sake matsowa tace

“Dad mum zaka duba yanzu? Ta Vconference?
I want to join too D….

Katseta yayi cikin nutsuwa da rashin son hayaniyar da cewa

“Little Abeeda”

Faduwa gabanta yayi da karfi tana Neman sarqewa da yawunta dataje hadiyewa ta juyawa da sauri ta kalli Amatu wadda taqi kallansu har lokacin saima sake rufe idanuwanta datai ahankali cikin sanyi da rashin kuzarin datake tare dashi.

Maamah wannan gabar kasa riqe mamakinta tayi ta zubawa AmatulMaleek idanuwa tana shiga tashin hankali da faduwan gaban itama,Ina take Jin little Abeeda, Amatun ce ya ambata Hakan??

Mum Aisha kuwa rikicewa ma tayi ta nufi hanyar fita maamah na bin bayanta da anty Farha data fasa dauko mata rigar sakawa tabi bayansu bayan takama hannun Husnah suka fito sbd Taga alaman bazata iya motsawa daga inda take tsayenba.

Anty Farha Jan kofar tayi bayan sun fito tana kallan maamah da batasan ma Ina take Saka kafartaba tsaban duhun da idanuwanta ke Neman yi sbd tinana da tashin hankalin meya hada ASH da zuwa duba Amatun ana zaune kalau,hakama waye ma ya sanar dashi ciwonta?
Hakama ciwon bama Wani me girma ba da zaace zaa zo dubiya a irin wannan lokacin.

Mum Aisha kuwa kujeran datake seti da bedroom din Amatun ta nema ta zauna a palon sbd ta hango ficewansa da lokacin da zai dauka a dakin.

Husnah anty Farha ce ta riqeta da kyau ta zaunar da ita tana cewa ta lura karta Fadi.

Ahankali ya Tako zuwa gadon datake a zaune din idanuwansa gaba Daya akanta Yana Jin pressure dinsa na raguwa kaman ana zazzage masa su suna bin iska.

Jin takowansa zuwa gareta ya Sanyata Bude idanuwanta ahankali batareda t dago ta iya kallansa ba Dan kuwa mutuwa jikinta yakeyi da zuciyarta akan matsayin da zata samu kanta yanzu da matarsa ta farfado,sedai Kuma tasan a Wani gabar ita Kanta tana murna da farin cikin tashin Madame abeeda bare shi dayake mijinta tinda dukkaninsu Babu Wanda qiyayya ta hada kowa kaunace ta hadasa da Abeedan daga ita har shi din.

Rashin saukan idanuwanta akansa ya Sanya jikinsa nauyi ya zauna ahankali cikin nutsuwa gefenta tareda miqa hannunsa Daya ya zagayota jikinta Dayan Kuma ya kama hannunta Daya ya sarqe da nasa din Yana sauke numfashi tareda ajiyan zuciya me sanyi a cikin kunnenta Wanda ya Sanyata Maida idanuwanta ta rufe tana riqe hawayen dayake son zuwa idanuwanta ta hanasu taruwa.

Cikin nutsuwa da kulawa ya sake sarke yatsunsa da nata ya zuba mata idanuwansa yace

“Yaya jikinki?
Are you still in pain kaman da safe?
Dr zaizo da Daren Nan ya sake dubaki before na wuce…..

Se a lokacin ta Bude idanuwanta ahankali ta Dan kallesa tana zuba mata idanuwanta dasukai laushi gaba Daya.

Jin yayi kansa na Neman kuncewa da kallanta sedai Bai nuna Hakan ba cikin kulawa a natse yana Kai hannunta bakinsa yayi kissing ahankali yace

“Zanyi tafiya a yau din Nan dole zuwa Lagos daga can Greece zan tafi….Abeeda ta farfado,I have to be there,akwai formalities and…”

Shiru kawai yayi batareda ya qarasaba ya dago ya zuba mata nasa idanuwan Shima Yana shafa wuyanta da fuskansa a natse Dan Jin zafin jikinta Daya sauka.

A handkali ta dauke idanuwanta daga kallan dayake mata ta Bude Baki cikin sanyi tace

“Allah ya tsare hanya,
Allah ya Bata lafiya yasa qarshen wahalan ciwon nata kenan”

Maganarta ya sanyashi zuba mata idanuwansa Batareda ya daukeba,
Jin yakeyi kaman bazai iya barinta ba a yanzu datake buqatan kulawa sosai sedai Kuma hankalinsa zai rabu ne zuwa da ita kaman yanda itama can Abeedan take buqatansa hakama little Abeedan bayajin tana buqatan ayi doguwan tafiya da ita a wannan halin datake ciki dayake ga kaman ko dogon motsi bayason tana shiga Dan shi kadai ne yasan irin yanda take buqatan zama guri Daya ta samu lafiya.

“Amin” ya furta ahankali kusa da kunnenta da sautin da bazai dametaba kafin ya Dora da tambayar taci abinci?

Gyada Kai tayi ahankali har lokacin Yana zagaye da ita da hannunsa Daya Dayan na sarke da nata.

“Ya maganinki,did you take them too??

Gyada masa Kai tayi tana dan dagowa ta kallesa take ya Kai bakinsa yayi kissing idanuwanta ahankali Yana sauke ajiyan zuciya me Dan nauyi.

Motsawa tayi zata gyara zamanta ya gyara masa da kansa Yana tambayarta Yaya dai,ko tanajin wani abin ne.

A Palo kuwa zaman jiran haihuwar gwaggo sukeyi gaba dayansu babu magana Se kallan kallo da Satan kallan hanyar bedroom din.

Maamah a jiqe take da zufa cikin rigarta Amma dai ta danne ta boye tinda dai bawai abinda suke tinanin bane na ASH din zai fara bawa Amatun matsayin matansa kawai dai dubiya ce sedai dadewan ne duk ya daga hankali da Sakata tinani da damuwa jiki a mace,harga Allah batason abinda zai hada Amatu da ASH ko kadan tinda Akai wannan auren.

Mum Aisha kuwa hankalinta rabuwa yayi uku akan makomar ‘danta da Kuma abinda yake Shirin faruwa tsakanin ‘yar Asmau da ASH dakuma farfadowan Abeeda datake fatan Allah yasa daga can ASH din na zuwa yafada mata yayi aure zuciyarta ta buga Cancer dinta ta haukace koina kaca kaca ta koma mutuwar kwancenta
Dan kuwa matsalolin yawa zasu mata Bata gama data Asmau da ‘yarta ba yanzu Abeeda ta taso tace ta amince da auren shikenan Asmau da yarta sun zama masu gida,hakama shi ASH ya samu yanda yake so bayan ya kassara mata nata Dan tana ji tana Gani yakoma gurgu,
Wlh yanda batajin dadin rayuwar yanzu ita Danta Babu Wanda zeji dadi a mansion din TALBAs kowa Se yaji abinda bayason ji, Wanda zuciyarsa zata buga ta buga ya mutu, hakama Wanda ze haukace ya haukace hakama me Rabon sake komawa coma ya koma me mutuwa da ciwon so Shima Dan ubansa ya Dade be mutu ba.,
Itace zata sama yar sakon mugun labarin kowa kaman yanda kowa ya zama Dan isar mata da baqin cikin zuciya,
Fatanta yanzu ASH ya Maida Amatu matarsa ta fasawa maamah labarin tareda qarawa da Wanda ze fasa zuciyarta ta qara gaba ko itama tabi Aminiyar tata coma can su qarata ta samu taji da Amatun kawai Dan haka take Saka ido sosai akansu tinda alamun sun fara nuna Hakan na kusa a yanda ASH Baya iya Hana idanuwansa kallan Amatun.

Husnah kuwa asthma da basusan tanada shi bane yake Neman tashi ahankali ahankali
Mum Aisha ta Gani tayi mata banza tana hakama Aunt Farha ta Gani itama ta dauke Kai tana cigaba da wayarta na Dr beeba data dawo sake duba Amatun.

Maamah dai batama San me kowa yake cikiba ta sauko qasa kitchen ta zauna cikin sanyin jiki da tinani tareda damuwa me nauyi.

Dr beeba ce ta shigo palon saman karima data hawo da ita tana bayanta kafin ta juya ta sauka.

Anty Farha ce ta miqe tana masa sannu da qarasowa kafin ta nufi bedroom din tayi knocking ahankali.

Bata sake buga kofanba ta dawo ta dauki wayarta ta kira Mr Jameel ta sanar masa ya fadawa ASH Dr beeba tana Jira a Palo.

Mr da Daman Shima a matse yake da ASH din sbd suna kokarin yin lattin zuwa airport Amma ya kasa kira dan yasan bama lallai ya dauka ba Dan yafara lura da idan Yana tareda Amatun samun daukan wayarsa dace ne.

Daurewa yayi ya turawa ASH din sakon Dr beeba na Palo zata duba Amatun kaman yanda ya buqata.

Daman shigowa ya bawa Dr beeba wadda ita kadai ce ta shiga dakin ta rufe ta qaraso ta zauna tana Dan kallansu cikin nutsuwa da shaawan kulawansa gameda iyalinsa.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070<

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button