Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 72

Sponsored Links

*************
Kokarin boye mamakinsa Abdulhameed keyi sedai ya kasa boyuwa Dan haka ya zuba mata idanuwansa dasuke a bushe tin jiya sbd Radadin rasuwar,

Qasa tayi da kanta tana kasa kallansa hawayenta na tsananta gudu Dan kuwa Bata sanar masa tanada cikin ba sbd kunya.

Juyawa yayi ahankali ya Kalli inda Haydar yake zaune har lokacin idanuwansa akan Amatun hawayensa na saukowa ahankali.

Related Articles

Dawo da kallansa yayi kan Amatun tareda janyewa gefe Yana boye mamakinsa ya Bude Baki ya gaisa da anty Farha sukaiwa gaisuwan rasuwar kafin ya Kalli Amatun itama Yana mata gaisuwan rasuwar mum Abeedan.

Amsawa tayi muryarta a qasan makoshi da sanyi kafin ta daga kafafunta ahankali ta Isa gurin Haydar Wanda Bada tanada aure akanta ba aurenma na Dad dinsa da saita rungumesa ta rarrashesa sbd tana iya hango radadin dayake ciki na rashin uwa wadda duk girma da tsufanka ita uwa rashinta radadinsa daban yake.

Shi kansa Badan girma da yayi ba ya sake zama matashin gaske da Babu abinda zai hanasa runguman Amatun sbd ita kadaice a yanzu zata sassauta masa radadin da zuciyarsa keyi na rashin mahaifiyarsa.

Zaunawa tayi a gefensa ahankali a darare tana sake boye cikinta sbd idansa akanta suke.

Anty Farha ma da Abdul zaunawa sukai anty Farha na masa gaisuwa cikin kulawa da nutsuwa
Shima a natse ya amsa gaisuwar tareda Godia.

AmatulMaleek ma ahankali ta dago idanuwanta cikin nutsuwa da sanyin jiki ta Bude bakinta tai masa gaisuwa tareda yiwa Madame Abeedan addua da fatan samun rahamar ubagiji.

Amsawa yayi Yana dauke kallansa daga Amatun sbd adduarta ta sanyaya masa zuciya.

Shiru gurin ya dauka sbd kowa da abinda yake ransa,.anty Farha kuwa kallan Haydar din da kusan duk kamannin ASH ne a fuskarsa hakama jikin irin nasa ne kakkarfa ingarma hakama bazaka Kalli ASH Kai tsaye kace shine ya haifesaba sedai kace qaninsa ne,
Daga Haydar din har Abdulhameed Wanda shikuma kamansa da Amatu ne ya qara bayyana sosai sun zama matasa sosai Dan kuwa kusan bazaka gansu kace sune qannan Amatu da Husnah zaka dauka sune yannen su Amatun nesa ba kusa ba sbd zamansu a qasar turai sun sauya sosai geamin sukeyi Daya qara budesu ya sake boye shekarunsu duk da suka shekarun sun fara dagawa.

Kasa cewa komai tayi da Shirun yayi yawa ta miqe ta shiga dakin maamah Dake kwance ba bacci takeyiba Amma tana Dan jin jikin tai mata sannu harma da gaisuwan rasuwar ta zauna shiru tukuna ta fito.

Amatun duk da itama ba lafiyar ne da ita ba Haka ta Dan sake matsawa Haydar din yaci abincin dayake gabansa,.

Sama sama ya qara cin abincin kafin yafara ficewa ya tafi dakinsu yayi wanka ya fita gurin gaisuwa.

Abdulhameed ma sama sama sukai magana da Amatun a agaban anty Farha da tasan komai kafin ya fice Shima yaje yayi wanka ya fita wajen.

Suma anan palon maamah suka wuni sai bayan Azahar da zazzabin Amatun dai yayi Dan yawa suka koma suka dan sake zaunawa a palon sedai ko mintina arbain basuyiba ta kasa dole suka koma daki ta kwanta tana tsiyayar hawayen abinda takeji.

Yauma har dare mr Jameel kansa baiji daga anty Farha ba bare sanin ya Amatun take Dan itama anty Farha din tafara Jin zafin abinda akaiwa Amatun Dan haka Shima Mr Jameel din ta tattarasa ta aje Dan batajin shima Yana buqatan sanin me Amatun take ciki bare ubangidansa.

Maida hankalinta kawai tayi gurin kulawa da Amatun tinda kowa Wanda ya damu dashi yake kulawa.

Husnah dangin mum dinne suke kulawa da ita,
Maamah Abdul dasu khaltume ne suke kulawa da ita harma da Haydar Wanda Shi Kuma Abdul yake kulawa dashi.

Maigidan kuwa har lokacin Babu Wanda ya gansa sbd daga can yake shigewa sashensa.

Kwana bakwai da rasuwar kowa ya watse Dan haka aka bar mutanen gidan Se masu aikin gidan Dan haka gida ya sake daukan tsit.

Amatu sosai taji jiki a kwanakin Amma sbd anty Farha da Abdul dasuka tsayu akanta Taji sauki batareda har lokacin maamah tasan ciki ne a jikinta ba harya Dan bayyana,
Hakama Husnah batasan da cikin ba sbd har lokacin Bata dawo daidaiba Saida kowa ya watse ta Dan dawo daidai sedai tana cikin mummunan halin tausayi dan kuwa ko ruwa daqyar takesha abincima Daman turawa kawai takeyi.

Mum Aisha kuwa har lokacin ita dai a tsinke take da abinda zai biyo bayan watsewan zaman gaisuwar sanin sune sukai sanadin fadowar Abeedan Wanda ta tabbatarda ASH bawai mantawa yayi ba shiru yayi ne kawai Wanda Kuma Shirun shine abin tsoro da fargaban.

Anty Farha tana waya yanzu da Mr Jameel Amma Bata taba fada masa maganar Amatu ba hasalima ko shine ya tambaya lafiyar Amatun yi take kaman bataji ba,ita jin ma takeyi kaman ta dauke Amatun su koma gidanta tinda kaman babu me buqatanta a gidan bare kulawa da ita.

Ita kanta Amatun magana ne kawai Batayi zuciyarta a cike take da qunci da damuwa Amma Bata taba nunawaba zaman daki ma kawai ta koma yi koina bata fitowa taje har maamah ta Dan warware Bata sake zuwa dubota ba sbd itama jikin take ji.

Haydar kullum Yana shigowa ya duba Amatun Amma Bata taba barin yaga cikin dayake jikinta ba Shima kuka baitaba kawo tinanin samun ciki a jikin Amatun ba Dan haka sosai yake Bata kulawa da ita da Husnah wadda a yanzu Haydar ne abinda zuciyarta ke tsananin son kasancewa dashi Se maamah wadda Kuma tsoron ma zuwa inda take takeyi Amma a yanzu harda maamah take buqata sbd Dad dinta tsoron ma ganinsa takeyi.

Yau anty Farha zata koma gidanta duk da kwana Daya zatai ta dawo da karima da suka baro acan,
Hankalin Amatu Bai tashi ba sbd tasan anty Farha din tana kokari sosai Dan haka saita danne damuwarta ta nunawa anty Farha din ba damuwa zata iya zaman ko Bata Nan.

Bayan tafiyar anty Farha din babu Wanda ya sake leqowa inda take haka ta wuni ta kwana sbd su Abdul Basu wuni gida b da Haydar komawa zasuyi a kwanakin.

Washe gari da safe wanka tayi taci abincin da Farida ta kawo mata tana cikin ci anty Farha ta dawo gidan tareda karima wadda ta hawo da kayan Amatun Dake gidan anty Farha an tattaro andawo dasu.

Gama cin abincinta ko dauke abincin data gama ci ba’aiba amai ya taso mata Dan haka ta sauri ta tashi ta fada toilet tafara Amai me qarfi Wanda ya tafi da qarfinta sosai.

Ko data gama tayi laushi sosai rigarta kusan ta Dan lalace da aman Dan haka wanka ta sake yi ta fito daure da towel me Dan girma ta zauna kadan ta shafa Mai da tirare ta Saka doguwar rigar material me tsantsi da laushi me Fadi sosai da tsada duk da bazaka gansa kace me tsadan bane sbd na Shan iska ne.

Lafewa rigar tayi a jikinta kaman fata tareda bayyanar da cikinta sosai da sosai.

Kokarin zaunawa takeyi bakin gado aka Turo kofar dakin ahankali Bayan anyi knocking so Daya Dan anty Farha Bata dakin ta fita.

Husnah ce idanuwanta a kumbure hakama fuskarta Dan har ranar ta kasa Dena kukan mum dinta,

Zuciyarta ta kasa riqe tsananin buqatanta da kewan maamah Dan haka ta danne abinda takeji tazo bawa Amatun hakuri Dan ta shiryata da maamah sbd tana tsananin buqatanta a yanzu.

Juyowa gaba Daya Amatu tayi tana kallan Wanda ya shigo idanuwanta suka sauka akan Husnah wadda ta qame cak a inda take tana kasa daga qafarta ta qaraso tsakiyar dakin sbd abinda idanuwanta suka sauka Akai wato cikin Amatun da yake kusan wata hudu harma ya fita.

Rawan disco qafafunta suka fara yi tana Jin zufa Tako Ina Yana Neman jiqata,
Kasa dauke idanuwanta tayi akan cikin duk yanda taso sbd shock da rikicewan da ganinta ke Neman yi.

Amatu ma kasa motsawa tayi daga inda take tsayen cikin tsananin mamakin ganin Husnah a dakinta da Kuma shakkan kallan datakewa cikinta cikin mummunan halin tashin hankali.

Magana zatai Husnah ta rigata muryarta na yankewa a daburce da cewa

“Cikin haihuwa ne wannan Amatu??
Ciki gareki?na haihuwa ne kokuwa?
Na mutum ne ko aljanu Amatu?

Tambayoyinta ne suka Saka zuciyar Amatu daci da mamakin haukar Husnah da Bata warkewa,
Bazata iya tashin hankalin dasuka Saba ba sbd abinda yake gabanta ya isheta Dan haka batajin tanada lokacin amsa tambayar me kama da tabin hankali Dan haka zaunawa take kokarin yi ta nufi kujera tana cewa

“Lafiya kika zo nan din?”

Bata zaunaba Husnah din cikin ihun kuka jikinta na wata irin rawa tace

“Ciki ne wannan din da gaske?
Cikin haihuwan mutum da gaske??

Fasa zama Amatu tayi tana hana zafin dayake ranta fita sbd gaba Daya gidan da mutanen gidan itama sun isheta kaman yanda suke ganin ta ishesu itama ta gaji harma da Wanda duk akeyin rigimar akansa duk ta bar musu itama ta gaji.

Kallan Husnah din tayi tareda nuna mata kofa tace

“Ki tafi kiyi harkanki a inda Zaki samu me kulawa da ita ni na gama da matsalarku.”

“Wlh Karya kikeyi saikin bani amsata idan ciki ne wannan ko sakawa kikai kice cikin ne Dake…..

Kama hannunta Amatu tayi ranta ya gama Baci zuciyarta zafi takeyi batama San tanada karfin Jan Husnah din ba Sai data janyota kaman kayan wanki ta Turota waje zata rufe dakinta Husnah din ta tare kofar itama cikin tsananin radadin zuciya jikinta na rawa ta kasa yarda da mum dinta tana cikin ciwon mutuwa har Amatun da Dad dinta zasu samu damar yin ciki.

Ihun Husnah din ya Saka anty Farha sake kitchen gurin dafawa Amatun Wani custard din hawowa da sauri hakama mum Aisha datake palon qasa zaune tana waya tasowa tayi da sauri tana kashe wayar tana cewa

“Wannan mahaukaciyar zata ballo mana fushin ASH da suka samu rasuwar Abeedan ta kwantar ta ja musu balai ana zaune kalau”
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

73
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button