Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 74

Sponsored Links

*************
Asibitin Yana Isa parking yayi tareda fitowa cikin saa Dr beeba na harabar asibitin tana waya shigowarta kenan itama asibiti Bata qarasa shigaba Daman Taga motar gidan ASH din ta farko ta shigo saiga ta biyu kafin ta kashe wayarta saiga ta ukun take ta qaraso gurinsa daidai ya fito da Amatun
da sauri cikin daga murya tafara Kiran nurses suka fito da sauri akai ciki da Amatun.

Emergency dinsu dayake sama aka nufa da ita Kai tsaye aka shiga da ita Dr beeba din na tambayarsa meya sameta Bai iya cewa komaiba bayan ta dubata tareda tabbatarda Babu abinda ya samu cikin jikinta ko yayane su kokarta kawai.

Tabbacin zasu kokarta din ta basa tareda shigewa aka rufo kofar.

Mr Jameel da sauri ya nunawa ASH din gurin zaman Dake gurin Yana komawa mota Dan kawo tissues da wipes da zai goge jinin Daya taba kayansa sosai.

Anty Farha kuwa kanta har Wani sarawa yakeyi tana Jin da tanada Iko Amatu na tashi ba zata koma gidan ba gidanta zata tafi da ita.

Abdulhameed kuwa hannunsa yake Dan girgizawa a wuyansa cikin fargaba da tsoron Wani abu ya samu yar uwarsa ko cikin dayake jikinta.

Haydar har lokacin Bai samu kuzari ko nutsuwan tambayar abinda ya juyar masa da Kai ba kawai lafiyan Amatun yake fata kafin biyowar komai.

Ga Dad dinsa Babu ko fuska data bawa kowa Daman ko kusantosa bare tambaya.

Zaman shiru sukai a gurin harna kusan awa biyu kafin Dr beeba ta fito tana kallan Mr Jameel da anty Farha da suka Dan fara motsawa tukuna ta nufo ASH Dake zaune har lokacin bai iya cewa komaiba bayan idanuwansa da suka qara daukan Jan yanda zuciyarsa ke dauke da zafi me tsanani.

Dan sauke kallanta Dr beeba tayi daga idanuwanta tareda miqawa anty Farha takardar hannunta ta maganin data sauyawa Amatun ta Dan sake kallan ASH Daya dago idanuwansa ya zuba mata tana Neman rudewa sbd shakkar yanayin nasa tace

“Cikin ya Dan zuba ne Amma Allah yasa Bai fadi ba sai Kuma BP nata Da yayi mummunan Hawa sosai Wanda Bai kamata ace me ciki BP dinta Yana kaiwa Hakan ba kusan ma shine ya Sakata sumewa cikin na kokarin fita so,
Amma Inshallah komai is ok yanzu Se a kula sosai please musamman Daya fara zuba cikin komai zai iya faruwa idan aka sake ganganci”

Mr Jameel da anty Farha kusan a tare suka saki ajiyan zuciya a Fili abinda ya danne kirjinsu Yana fadawa,
Abdulhameed ma numfashinsa dayake a rikice ne ya sauka tareda dawowa daidai.

Haydar kuwa sai alokacin hankalinsa ya dawo daidai ya zubawa dukkaninsu idanuwansa tinaninsa na tsayuwa guri Daya shine cikin waye a jikin Amatun?
Yaushe tayi aure?
Dama zata iya aure batareda ya saniba duk tsawon lokacin Nan harma da qaruwar ciki??

Juyawa yayi batareda ya iya cewa komaiba yabar gurin Abdulhameed Daya lura da tafiyarsa juyawa yayi ya bisa jikinsa na sanyi.

ASH kuwa miqewa yayi ahankali daidai lokacinda aka fito da ita aka kaita Wani lafiyayyar dakin da kaman a luxury hotel room kake me nutsuwa.

Gadon da zaa maidata shine da kansa ya Saka hannuwansa biyu cikin kulawa ya dauketa ya kwantar bacci takeyi batama San waye akantaba.

Nurses din na ficewa ya zauna ahankali gefen gadon tareda zubawa cikinta idanuwansa Daya ji suna Neman tara ruwa a cikinsu na abinda yake Gani a gabansa.

Cikinsa ne a jikinta,
Haifar masa ‘yaya zatai bayan ya cire Rai daga sake samun wasu yayan,
Duk wannan lokacin Dasuka dauka nesa da juna ciki ne a jikinta batareda ya saniba,
Azabar Daya ringa bawa kansa na rashinta Ashe baida Rabon kulawa da jininsa dayake cikinta ne,
Da mahaukatan gidansa sun Saka cikin ya fita da shikenan yayi rashin tsatsonsa batareda ya San dashi ba ne ko me??
Meyasa farha duk tsawon lokacin Nan Bata sanar dashi Amatun juna biyu ne da ita ba,
Tayaya yarinyar da Bata taba ciki ba zaa barta da dawainiyar renan cikin ita kadai,
Yasan tayi kuka tayi rashin bacci ta shiga tashin hankali da fargabar maamah dinta gameda ciki Amma batada me Bata kariya da kulawa……

Rintse idanuwansa yayi zuciyarsa na qara masa ciwon halinda ta shiga batareda saninsaba,
Duk wanna lokacin a cikin qunci sa radadin zuciya yake na rashinta Amma ya zabi hukuntasu su dukan akan lefin mahaukatan gidansa da sunyi Nisan da basa Jin kira.

Hannunta ya kama ahankali tareda hadewa da nasa tafin hannuwansu suka Hadu bayan tsawon lokaci da suka dauka batareda ganin juna ba ko jin juna.

Ajiyan zuciya me sanyi ya sauke Yana Maida idanuwansa akan cikin Dayake kasa gasgata shine ubansa,
Shine zai haifi Yaya da macen da tinaninta kawai ke dakatar da duniyarsa gabaki daya bare kallanta da idan tai masa yake Jin itace dalilin duk Wani farin cikin rayuwarsa.

Hannunsa Daya ya daga Ya Dora akan cikin take Wani numfashi me qarfin gaske ya kufce masa kowannen kofan zuciyarsa na budewa wasu sabbin feelings suna shiga suna narkashi.

Shafa cikin ya sake yi ahankali Yana kallansa sbd mamakin ganin cikina a cikin LA dinsa dayake Tina lokacin farko Daya fara ganinta a baby ya dauketa cikin zanin haihuwanta Bai dauka itace zata basa feelings da farin cikin ganin yayansa a cikinta ba sbd lokacinda Abeeda take da cikin Haydar nesanta kanta tayi dashi ta koma porthcrt gaba Daya sbd batason ya ganta da ciki kamanninta wai zasu Sauya batason ya ganta da kammanin masu ciki Dake kumbura komai Dan haka Sam bai samu dama ta kasancewa da ‘dansa lokacinda yake cikin ciki ba,hakama Bai samu Daman sanin dandano da dumin matarsa lokacinda takeda ciki ba.

Gaba daya Jin kansa yayi kaman sabon matashin saurayi Dan haka ya Jima sosai kafin ya fito suka tafi gida da Mr Jameel Dan wanka da sauya kayan jikinsa ba Farha kawai suka bari wadda itama hankalinta ya kwanta da samun cikin Amatun baiyi komaiba.

Haydar da Abdulhameed sun dawowa gida Haydar rufe kansa yayi a daki
Abdul yayita son magana dashi Amma Sam baya buqatan kowa a yanzu kansa yakeson ya sake,
Abinda yafi masa ciwo shine yanda Amatun ta iya boye masa aurenta da cikinta bayan basa boyewa juna komai.

Abdulhameed ganin Haydar din yaqi sauraronsa ya sakashi qyalesa ya tafi gurinsu kawu Dake bq Dan su gaisa.

Dawowan ASH mansion din ya Saka mum Aisha,maamah da Husnah shiga sabuwan sanyin jiki da fargaba.

Ga Abdulhameed ma Sam yaqi zuwa gurin maamah din bare taji lafiyan Amatun Dan Shima abin nasu ya ishesa ya rasa yaushe mahaifiyarsu ta Dena kaunar yayanta da Kwanciyar hankalinsu tareda rashin sanin inda tawakkalinta da hakuri da Nutsuwarta duk suka tafi tsoro ma yakeyi idan ba maganin Husnah takesha ba itama matsalan ke Neman tabata.

Gaisawa dasu kawu Abdul yayi ya zayyana musu abinda yake faruwa ba duka ba kawai dai iya qin amsar auren da maamah tayi sun gigita rayuwar Amatun gaba Daya gashinan yanzu tana asibiti ta kusa rasa cikin dayake jikinta.

Shiru dukkaninsu sukai cikin baqin mamakin duniya daya kashesu.
Kawu bello cikin mamaki yace

“Wato Asmau ciwon rashin tinani ya sameta kenan shine tazo ta zauna muka gaisa lafiya lafiya ta rufemu mu gama gaisuwa mu koma Se kawai ta kashe auren na da muka Hana kanmu zama muka Hana kanmu tsayi gurin yawon malamai a sake tsuqe mana shi karya balle Ashe muna zaune ganinta kawai zamuyi da Amatun ta kaso auren,cabdijm.”

Kawu ashiru kuwa rasa abin fada yayi sbd baqin cikin Asmaun da mamakinta Daya siqesa.

Kawu yusufa kuwa kallan Abdul yayi Yana cewa

“To ai shikenan tawa kanta Dan kuwa wlh kafarmu kafarta ba zaman da zata ci gaba da yi anan din,Banda rudun iska Daya shafeta a gidan sirikinta kamata yayi ace har mantawa ma ariga yi da tana gidan sbd kullen da zata ringa yiwa kanta ta zauna guri Daya Amma shine sbd samun guri har yawo takeyi koina a gidan hardasu dambe akan cikin siriki,
To zanga uban dazai Hana a Haifa cikin tinda sune sukai mata cikin.”

Shiru Abdulhameed yayi maganganunsu suna Dan Sosa zuciyarsa sedai Kuma Yana fatan akawo karshen matsalar tinda maamah su kawun ne kawai suke fada ta zaunu a gurinta sai Kuma ASH.

A cikin gidan kuwa a Palo suka zauna shiru kowa na jiran shigowan ASH Amma shiru sbd ta palonsa n qasa ya Haye zuwa samansa batareda sunsan ma ya shige din ba.

Wanka yayi da ruwan dumi toilet din na gaurayuwa da qamshin tsadaddiyar Aesop liquid soap dinsa me tsada da sanyin qamshi.

Yana gamawa ya fito daure da towel jikinsa na tsiyayar ruwan da kusan ke qarawa murdaddiyar jikinsa daukan hankalin Wanda ya Gani.

Goge jikinsa yayi da towel yana tsaye gaban mirror ya shirya tareda barin gurin ya Saka Fendi sweatsets ya fito sallan magrib da aka kira.

A gurin sallah su kawu suka samu ganinsa Shima sai alokacin yasan d zuwan nasu ya gaisa dasu sukai sallah
Bayan sun fito Kai tsaye palonsa na baqi da suka fara sauka ya Isa dasu suka zauna anan suka sake gaisawa dashi suna masa gaisuwa a tsananin girmamawa.

Bayan sun gama miqa gaisuwarsu ta rasuwar Abeeda kawu bello ne yafara jeho maganar jikin Amatu Yana mata sannu da fatan samun lafiya kafin suka sanar dashi sunji komai daga bakin Abdulhameed.

Fada sosai kawu bello da kawu yusufa sukai duk Yana sauraronsu har suka gama sai alokacin ya qara sanin wasu abubuwan na tashin hankalin da suke zubawa a gidan ya hada da Wanda yaji a bakin Farha yau din komai da komai.
bayyanarda tafiyar da zasuyi da maamah sukai daga qarshe.

Sai da sukai shiru ya Kalli Mr Jameel dayake shigowa yace ya kira masa kowa duk suzo Yana nemansu.

Mr Jameel na ficewa ASH din ya Kalli su kawun Daya bayan Daya kowannensu yasha shaddarsa ta Roba da hulunansu da baimasan wane kalar Karin ne dasu ba Dan ta kawu yusufa kaman shape din jirgin kwale kwale.

Uzaifa ya juya Yana kalla Wanda Shima yake jikin shaddar robar green Shar da ba hula akansa Dan haka qananun gashin kansa Mai kama da gonar Aya yake bayyane.

Kawu bello yafara kalla bayan ya sauke numfashi ahankali Baya buqatan tashin hankalin dazai taba L.A ko lafiyan dansa dayake cikinta Dan haka Kai tsaye ya sanar dashi hukuncinsa da sauran bayanan abinda yake buqatan daga garesu.

Daga kawu bello har kawu ashiru da uzaifa kusan gaba dayansu Wani girmamman farin ciki me tsananin dadi ne ya rufesu Dan kuwa abune Daya samesu batareda tsammani ba.

Shigowar su mr Jameel dasu mum Aisha na bayansa ne harma dasu Abdul da Haydar ya Saka su kawu gaba dayansu zubawa kofar idanuwansu cikin tsananin farin ciki suna Dan washe Baki tareda boye murnarsu.

Zama dukkaninsu sukai kowa jikinsa na jiqewa da zufa musamman mum Aisha da Husnah harka da maamah,
Abdul da Haydar kuwa basusan meye dalilin Kiran ba tukuna.

Kallan inda su maamah suke Daya bayan Daya kafin ya tsayar da kallansa kan Husnah wadda take sake tsinkewa.

Bakinsa a natse ya Yana dauke kallansa daga kansu yace

“Dukkaninku ku shirya gobe za’a daurawa kowaccenku aure Kuma a goben zaku wuce.

Maamah ya kalla yace

“Malam bello yace ze mayar da aurensa na Kuma amince masa da Hakan,
Malam ashiru kuwa na basa auren Aisha,’dansa uzaifa Kuma auren Husnah,
Kowa ya shirya duka gobe ana daurawa zaku wuce.
Kowa ta tashi ya tafi shikenan.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

75
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button