Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 83

Sponsored Links

************
Su kadai suka wuni a gidan hankali kwance Yana juyata yanda yakeso suna zuba soyayyansu abincin ma kusan duk a shiririce suke cinsa har lokacin bacci yayi sukai wanka yamata Shirin bacci suka kwanta.

Bai mata komaiba sai bayan sallan asuba suka zuba lafiyayyar soyayyarsu Yana Jin gaba daya baisan ta ina zai fara iya rayuwa idan tana fushi dashi.

Da safe dole da wuri suka shirya sbd tafiyar suka bi jirgi suka wuce bayan ta fadawa anty Farha komai sun jima suna magana.

Related Articles

Harda Mr Jameel din sukai tafiyar shiyasa suna Isa Basu Wani Bata Lokaci ba Saida ya tabbata taci abinci tayi wanka ta kwanta baccin Hutu kafin ya Hadu da qanin mahaifin Mr Jameel din suka tafi Neman auren.

Se yamma ya dawo wanka yayi shima ya huta suka zauna fira tana basa abinci Yanaci sama sama sbd wayan dayake amsawa.

Da daddare fita sukai acan suka ci abinci Wani lafiyayyar restaurant taci abubuwa kala kala datake so sbd shi drink kawai ya sha Amma Saida suka kashe kudinta zai ciyarda Wani gidan Taron na tsawon sati nawa a gurin ciye ciyen nata kawai.

Se dare sosai suka dawo wanka sukai suka kwanta bacci me dadi take ya daukesu sbd zazzafan love din da sukai making me sanyi da nutsuwa cikin so me qarfin dayake zuciyar kowannensu.

Washe gari anty farha ta iso Lagos din sbd Yan uwa da iyaye daketa murna da farin cikin itama lokacin nata auren yazo bayan ta jima din batai aure ba.

*****Ranar da su Amatu suka wuce Lagos a ranar su Haydar suka dawo Daman Kuma yayi magana da Dad dinsa zasu tafi porthcrt da Husnah kafin wucewansu Dan haka kwana Daya sukai Suma suka wuce porthcrt din shi da Husnah sbd acan zaayi hidiman bikin aurenta da anriga an daura.

Suna Isa aka fara Shirin Biki duk da iya walima da Salalle za’ai mata da Kuma gyaran Amare tinda dai an daura auren to dole suyi mata hidiman da akewa kowacce Amarya.

Abdulhameed Bai dawo ba Yana Yola tareda maamah wadda gidanta yake daban Dana mum Aisha sbd an rabasu kowa da gate dinta daban Kuma kowa sama da qasa ne tsarin nata gidan hatta me aiki kowannensu nada daddaya da me gadi so babu Wadda ke cikin tashin hankali da masifar da suka hangowa kansu farko ga abinci da komai an zuba musu.

A waya sukaji Amatu suna Lagos maamah naji tayi kaman bataji ba sbd Jin lamarin banbarakwai haka suka gama magana a wayar sukai sallan tana yiwa farha fatan alkhairi tareda cewa zata kirata tai mata barka din.

A porthcrt ba hidima sosai akaiba bayan Salalle da waliman akaita mata nasiha da fadan kwantar da hankali kada ta sake hargitse rayuwarta ta nutsu ta gyara mu’amalarta da Dad dinta hakama ta nutsu ta sake Dora rayuwarta kan tirba me kyau.

Gyara ake mata sosai Wanda ya sauyata ciki da wajenta kaman ba ita ba duk da ta rame sosai sbd damuwa da sanyi datai.

Haydar kuwa Daman ya Dade baizo cikin dangin mum din tasu ba Dan haka ya saki jiki Yana shiga cikinsu sosai.

Kwanansu bakwai a garin suka fara Shirye shiryen dawowa Amma Haydar yace ba yanzu zai koma ba Dan haka dole Abdulhameed da kansa yazo porthcrt din kwanansa Daya ya gaisa da family sosai suka juya tareda Husnah din zuwa Abuja.

Koda suka koma Bata dauka Amatu da Dad dinta basa Nan ba da bazata dawo ba sbd kadaici na Bata tsoro ga Dad dinta duk Kiran datake masa suna gaisawa batasan Baya Abuja Dan Saida su mummyn porthcrt Suka kirasa aka basa hakuri ya sauko daga fushinsa akanta Dan Daman tana cikin ransa a kwanakin yasan tana cikin damuwa.

Su khaltume cikin murna da farin ciki suka tarbeta suna mata sannu da zuwa sune sukai sama da kayanta kafin ta Abdul yahau sama da ita hannunta na riqe cikin nasa har bedroom dinta kafin ya fice zuwa nasu dakin.

Wanka yayi ya fito zuwa masallaci sallah cikin qananun kaya
Itama wanka tayi tai sallah ta Saka kaya marasa nauyi ta kunna wayarta tana waya da mutanen porthcrt daketa kira suna mata barka da sauka.

Sai da yayi sallan ishai ya shigo gidan abincinsu a dining room din palon kasa aka Jere musu Yana zaunawa ya kirata a waya ta fito cin abinci.

Saukowa Tayi jikinta duk a sanyaye da fargaban yanda zata kwana cikin. Mansion din ita Daya duka masu aiki suna bangarensu Shima Yana nasu bangaren.

Kallo daya yayi mata tana saukowa ya dauke kallansa daga gurin yana takaita wayar dayake yi da Amatu sbd kayan jikinta Sam basuda nauyi doguwar Riga ce pencil ta lafe jikinta sai hula Dake kanta.

Tana zuwa zaunawa tayi tana kallansa ta gaidasa kaman yanda aka ce mata a porthcrt.

Da Dan mamaki ya zuba mata kyakkyawan idanuwansa ya Kalli fuskarta tukuna ya amsa Yana dorawa da tambayar Yaya dai ya ganta kaman da damuwa.

Numfashi ta sauke tana cewa bazata iya kwana a gidan ba ita tsoro takeji ya kaita gidan anty Farha kawai zata kwana acan itama.

Cikin sabon mamaki yace

“Anty Farha din Bata Nan itama tana Lagos sbd hidiman aurenta ne yasaka su Amatun tafiyan ai”

Shiru tayi tana zuba abincin tana rasa abin yi.

Har suka gama zaman cin abincin Babu Me magana Saida ya gama ya miqe yana kokarin barin gurin ta Bude Baki tace

“Zaka fita ne?

Juyawa yayi ya kalleta Yana fasa Saka Kiran da zaiyi yace

“Akwai Wani abin ne?
Akwai abinda kike buqata ne?

Numfashi ta sauke ahankali tareda girgiza Kai kawai.

Ficewa yayi
itama kasa qarasa cin abincin tai tana barin dining din.

Tana zuwa daki brush kawai tayi tai Shirin bacci ta kwanta a takure.

Duk yanda taso bacci cikin Daren kasawa tayi Dan haka Koda asuba tayi kanta tsananin ciwo yakeyi ko abinci Bata iya fitowa ci ba Shima da safe fita yayi Bai dawo ba Se yamma.

A daki ta wuni sama sama kan ke damunta harma da zazzabi,
Bata bari yasan Halinda take ciki ba haka ta sake kwana cikin yanayin damuwa da ciwon Kai
Koda gari ya sake wayewa zazzabinta yayi karfi Dan haka dole yasan Halinda take ciki ya tafi da ita dakinsa ta kwana acan Yana kulawa da ita har safe.

Da safe shiryawa sukai yakaita Taga likita ba Wani matsala bane kawai ciwon Kai da zazzabi.

A cikin gidan haka ya ringa kulawa da ita cikin kwanakin yana tattalinta harta warware amma Bata dena kwana a dakin nasa ba Dan haka ya fara janyewa daga gareta sbd yanda lamarin ke kokarin tabasa sosai Dan ita Sam Bata Wani damu ko Tina yawan haduwan jikinsu da yanda take shigarta ta bacci yanda ta Saba zai iya tabasa ko Wani abin ba daban.

Ita Kuma ganin ya fara janye mata sai duk tafara Dan shiga damuwa sbd rashin sanin abinda yafaru.

Shikuwa sosai ya sake janye mata Dan yaga zata iya Sakasa mawuyacin hali Dan haka har baccin ma da daddare sai ya Dena kwanciya gado Daya da ita gari na wayewa zai bar gidan Baya dawowa Se dare sosai.

Rikicewa tayi da wannan sauyin Dan alamunsa sosai sun nuna itace din bayason tana rabarsa Dan haka ta ranar wata talata ta zauna ta ringa kuka sbd rashin sanin wane abin tayi Shima Daya gaji da ita harya Yana janye mata.

Ko Daya dawo da daddare tayi Shirin baccinta tana zaune tsakiyar gadon tayi kuka har idanuwanta sun sauya sosai Dan haka dole bayan yayi Shirin bacci ya zauna gefenta tareda kallanta zaiyi magana hawaye suka gangaro daga idanuwanta sbd shi kadai take dashi a yanzu da Dad dinta da Haydar basa Nan Amma Ya janye mata kwata kwata ko inda take bayason raba.

Tissue ya janyo Yana share mata hawayenta cikin kulawa yace ta Dena kukan ya Isa hakanan.

Rarrashinta yahau yi dole harda Dan janyota jikinsa Yana sake rarrashin nata harta Dena kuka ta lafe jikin nasa tana yar nutsuwa na dawo mata.

Dole ya sake mata Yana tarairayarta har tayi bacci a jikinsa tana lafe harda qanqamesa.

Hakanan ya daure Shima yayi bacci Rabi da Rabi sbd uwar haduwan dasukai dakyau har safe.

Washe gari duk yanda yaso kame kansa daga gareta Hakan Bai samu ba sbd zazzabin ciwon kan data tashi dashi haka ya lalace gurin kulawa da ita,.
Abinda Bata saniba shine yanda take shiga jikinsa sosai yayi masa illan da ita kanta bazata so ya kasa riqe kansa ba,

Da daddaren ranar haka ta jiqa masa aiki gaba Daya ya kasa riqe kansa yayi mata kyakkyawar runguma Yana kama fuskanta cikin sanyi ya hade bakinsa da nata ya mata wani irin kiss me sanyi Yana qanqameta jikinsa.

Qwacewa take kokari yi Amma yanda yake kissing din nata cikin sanyi Yana zagayota gaba Daya tared qanqameta jikinsa ya Sakata kasa kwacewa Se hawayen Dake ciko idanuwanta suna gangarowa.

A daren duk yanda taso qwatan kanta daga gurinsa Bata iyaba haka tanaji tana Gani ya mayar da ita cikakkiyar matarsa halak malak,

Taci wuya taci azaba me tsanani sbd qarfin samartaka dake tareda sosai gashi da maji karfin namiji,
Shi kansa yasan Tasha wuyan dan Saida suka tafi asibiti sai gata harda Dan stitches.

Bayan sun dawo shi da khaltume ne sukai ta aikin kulawa da ita Yana tarairayarta kaman sabuwar babyn da aka Haifa ranar,
Dayake Allah yayita me shegen raki haka ta ringa kuka damuwa kala kala a ranta harta warke ya bita da kulawa da tarairaya ya sake maidata tasa cikin sanyi.

Da farko ta shiga damuwan zamansu Daya din Amma ahankali da yanda ya ringa binta kwana biyu Yana tattali da kulawa Saita cire damuwan.

Sati biyu da kwanaki suka share suna cikin yanayin amarcinsu kafin Haydar ya fara dawowa Dan haka ta koma dakinta ya rabasu bayan sun fara sabo da Kwanciyansu cikin nutsuwa da tattali harma da soyayyarta Daya fara shigarsa me tsafta.

Kwanan Haydar hudu da dawowa su ASH suka dawo Suma bayan uban sabuwar rayuwar dasuka Bude a Lagos suna bazawa.

Dawowansu Husnah ta sake bawa Dad din hakuri ya hakura hakama Abdul ya shiryata da Amatu da kansa sbd bazaiso matarsa da yar uwarsa basa shiri ba.

Bayan dawowansu Dad dinta Husnah naji tana Gani Takoma zaman daki sbd rayuwar da idanuwanta ke Gani saikuma idan Abdul ya dauketa sun fita sbd kusan sune rage cin abinci sosai a gida guraren hutawa suke zuwa matsu tsada suci su dawo.

Dawowansu ASH da sati uku su Haydar da Abdulhameed din suka koma Banda Husnah sbd visan ta Bai samu ba sai daga baya zata bisu.

Kaman karsu rabu harda kukanta sbd yagama sauya mata rayuwa gaba Daya da kulawa da tattalinsa Dan haka bayan tafiyarsu koyaushe suna kan waya.

Bayan tafiyarsu da wata biyu Ciwon laulayi ya bayyana a jikinta take kunyar bayyanarsa ya Sakata shiga damuwa ta fadawa Amatun suka ringa boyewa ASH sbd batason ya sani sai ta tafi.

Tattarawa tayi bayan da cikin yafara kokarin bayyana ta koma Yola gurin maamah daga can visanta ya fito ta dawo ta tattara ta tafi Daman mijinta a matse yake da ganinta da cikin nasa Daya Riga ya sani Dan ta sanar masa.

Haydar mamakinsu hanasa magana yayi Saida murnar cikin dayayi sbd ganin Husnah din ta zama daidai a rayuwarta.

AMATULMALEEK ta haifi baby boy dinta lafiyayye ranar da aka gama bikin anty Farha kenan,
Allah yasa maamah tazo bikin hakama mum Aisha ta samu halartowa sbd Neman yawo takeyi ido rufe,

Dayake a Lagos Akai bikin acan ta haihu dole aka fasa tarewan Farha ranar sai washe gari suka tattaro suka dawo Abuja da amarya anty Farha.

Farin cikin the grt ASH TALBA da mr Jameel kusan bazai fadu b sbd kowannensu lokaci ne farin cikin rayuwarsu Dan haka Suka tafi hutun aikinsu gaba Daya.

Mr Jameel sabuwar rayuwar Kwanciyar hankali ya Bude da amaryarsa Farha gashi suna cikin double farin ciki Dana haihuwar masoyansu wato ASH da AmatulMaleek.

Maamah hakanan ta zauna ita da mum Aisha har Akai suna baby yaci sunan FAROUK ASH TALBA da sati Daya kafin suka koma Yola din gaba Daya harda Amatun sbd ASH din zaiyi tafiya Shima a satin.

Bayan tafiyarsu Yola da kwana biyu ya wuce Cyprus.

Zaman haihuwanta a Yola na gata da kulawa sosai ne daga maamah hakama mota biyu daga kauye kusan Rabin Yan gidan suka zo ganin farouk harda ganin matar kawu ashiru da baa taba Gani ba.

Maamah sosai ta kula da gyaranta har tayi arbain da sati biyu tukuna ASH ya dawo Basu Wani zauna ba suka koma sbd aikinsa kusan shekara zeyi acan Bai kammala ba gashi dole Baya iyawa seda Mr Jameel Dan haka mr Jameel tini ya samarwa matarsa visa suka wuce Koda Amatu ta Isa anty Farha farin cikin ganinta kaman me.

Sabuwar babin rayuwar Jin dadi suka Bude abinsu hankali kwance daga su sai babynsu saisu anty Farha da itama cikin ne da ita qarami.

Husnah na haihuwan baby boy itama mamaki ya kusan daure kan ASH da baisan ‘yarsa nada ciki ba Dan haka da kansa suka tafi UK din taredasu Amatu ganin baby wanda Husnah harda kuka shagwaban kunya ta ringa wa Dad din Daya bayyanarda mamakinsa.

Abdulhameed kuwa hankalinsa kwance murna da farin cikin zamowa Uba kawai yakeyi ga Haydar ma yayi murnar ganin qaninsa da kusan Shima kamanninsa Dana Dad din yayo.

Maamah ce kawai ta samu zuwa sbd kulawa da Husnah din sai mummyn porthcrt da itama tazo baby yaci sunan ASHRAF little.
Ana 2 weeks ASH da Amatu suka koma.
#MAMUH#
ALHMDLH!!
PLEASE KADA KUCE BAI KAMATA A GAMA BA YANZU KOKUMA YAKAMATA A QARA MUKU TSAWONSA SBD BABU SAURAN ABINDA YA RAGE A RUBUTA IDAN BA NISHADINSA ZAMU RAGE BA,

ABINDA NA MANTA BAN SAKA BA KO BAN WARWAREBA KOKUMA NA RUBUTA BA DAIDAI BA PLEASE AMUN UZURI SBD AJIZANSI,

ALLAH YA YAFE BARNAR DA MUKA AIKATA A CIKI YA BAMU LADAN NA KHAIRIN.

GODIA MARA ADADI GA DUKA WAINDA SUKA BIBIYA LABARIN AMATULMALEEK DAGA FARKONSA HAR QARSHENSA,
NAGODE SOSAI SOSAI.
ALLAH YABAR KAUNA.
SAI MUN HADU A NEXT BADA DADEWA WANDA INSHALLAH INA MUKI ALBISHIR DIN ZA ZAIFI WANNAN TAKO WANE SIGA INSHALLAH.

YAN BATI KUMA SANNUNKU DA KOKARIN BIBIYA DA KUMA ZAGI.

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button