Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 77

Sponsored Links

*************
Tana shigewa toilet ta jima Bata fito ba sai ga dr beeba ta shigo dakin tareda wata nurse da anty Farha.

Gaidasa sukai cikeda girmamawa suna Dan mamakin ganinsa a wannan lokacin danma itama Dr beeba ta kwana asibiti ne yasa tashigo dakin a lokacin.

Fitowa tayi daga toilet din a natse cikin sanyinta batareda ta dago ta Kalli kowa ba bayan Dr beeba Dake mata yaya jikin ta amsa a cikin sanyi tana zaunawa a hankali bakin gadon.

Related Articles

Tambayoyi Dr beeba din Tai mata tareda fada mata ta kula sosai ta cire damuwa sai Kuma kiyayewa da yanayinta tace ta sallamesu su koma gida.

Rubutawa tai a folder din Amatun kafin ta miqawa nurse din dake tareda ita tana fadawa ASH din dole sai ankula sosai sbd samun BP ga me juna biyu baa cika so ba Gaskia.

Dr beeba na ficewa Amatu Dake zaune ta Kalli anty Farha tace ta Bata hijab ta Saka tana Dan Jin sanyi.

Doguwar hijab anty Farha din ta miqawa Amatun ta Saka a natse har qasa kusan ma cikin idan ba Wanda yasan dashi ba Baya ganinsa.

Basuda Wani kaya Dan haka Yan abubuwansu Mr Jameel ne da kansa ya dauko ya fito dasu suka fito.

ASH dinne a gaba batareda yace komaiba sbd ko kallansa ma LA din taqi yi bare ya samu Daman yin magana.

Suna isowa mota dayake akwai mota Daya a asibitin a tareda dasu kafin wadda ASH da Mr Jameel din suka zo da ita yanzu.

Kai tsaye dayar motar Amatu ta nufa tana cewa anty Farha gidanta takeson su tafi Batason koina.

Shiru anty Farha tayi tareda tsayawa tana kallan Amatun cikin Dan mamaki kafin ta juya ta Kalli Mr Jameel Dayake tsaye Shima yaji abinda ta fada.

ASH Daya Bude mata mota Yana jiran qarasowarta kafin ya juyo da sauri mr Jameel ya qaraso cikin girmamawa da kare zancen ya sanar masa LA din tace a motan Farha zasu koma gidan.

Juyowa yayi ahankali ya kalleta yaga harta Isa motan Farha din batareda ta waiwayo ba ko alaman ma zata waiwayon.

Baici komaiba ya barta suje a motan Farha din sbd kada ya takurata ko kadan.

Mr Jameel da duk yake Neman rikicewa shiga motarsu yayi bayan ya rufewa ASH din kofa bayn shigarsa motar ya tada Basu fice ba Saida sukaga motar su Farha din ta fara ficewa.

Mr Jameel dayake yasan ba mansion sukaiba sai ya bari suka bace musu Dan kada ASH ya lura da hanyar da zasu bi daban.

Anty Farha Kai tsaye hanyar gidanta ta kama su Kuma Mr Jameel ya dauki hanyar mansion Yana shiga tinanin wannan sabuwar lamarin Kuma.

Ko da suka Isa mansion su kawu sunyi breakfast sun shirya tsaf abinsu sai kyallin Mai sukeyi da suka Saka aka kawo musu suka shafa sbd yanda duka fuskokinsu suka bushe kaman anyi hayaqin yashi suna zaune.

ASH na dawowa suka fito suka qaraso gurinsa suna gaidasa cike da girmamawa suna tambayar jikin Amatu.

Amsawa yayi Yana sake Basu tabbacin karfe goma sha Daya zaa dauka auren Amma Banda na uzaifa zai masa kudi ya samu mata acan kauye ya aura Husnah zai daura mata auren da Abdulhameed idan sun amince da Hakan.

Matse fuska uzaifa yayi sedai su kawu Basu bari ya nuna ba suka hau washe Baki suna cewa ai da Abdulhameed din da uzaifa duka Daya ne duk Wanda aka nawa nasu ai.

Ciki ya shige yabarsu suka koma masaukinsu suna tausar uzaifa Dayake Jin baqin ciki a karo na biyu ana masa ta leqo ta koma haka Akai masa lokacin Amatu yanzu Kuma Yana murna ya samu zuqeqiyar lafiyayyar yar Madara anzo an Hana masa zaa bawa Abdulhameed Dan anga ya fisa jikin girma da cika ido.

Dayake su kawun Basu rasa nasu ba Kuma sun San kudine dai zasu ta shigosu Dan haka suka taru suka danne uzaifa suka hanasa magantuwa akan maganar har su koma.

Husnah gari na wayewa ta fito Kai tsaye dakin maamah Dake daki itama tin jiyan ta kasa fitowa abin duniya ya isheta ya sha mata Kai,
Ga wannan auren na kaddada baqa da zaa daura mata,ga rashin sanin halinda Amatu take ciki ga ASH din Babu Wanda ya sake ganinsa ko Jin idan ya janye hukuncin nasa ko ansamu sassauci ga Abdul Rana tsaka da zaa daurawa aure ba shiri.

Husnah na shigowa ta zube gaban maamah din tana fasa kuka sosai tana rokonta ta yafe mata tace a daura aurenta da Abdul ayau din itama kada daga baya Dad ya sake fushi da ita ya aura mata uzaifa ko Wani daban Wanda bataso.

Shiru maamah tayi mata sbd itama cikin tsaka me wuyan take Amma kukan Husnah da yanda take rokonta har cikin ranta take jinsa dan son datake wa Husnah din Allah ya Gani har qasan ranta take kaunarta kaman itace ta haifeta.

Karyewa zuciyarta tayi ta rarrasheta akan suyi addua kawai Allah ya musu zabi Mafi Alkhairi Amma ita yanzu ko fitama daga dakin batajin zata iya bare zuwa rokon ASH.

Kasa fitowa daga dakin Husnah tayi ta rakube gefen maamah din tana Jin zazzabin tashin hankali na rufeta Dan duk ta sake shiga firgici idan ba ganin tayi Yan kauyen sun kwasa sun tattara sun tafi ba hankalinta bazai taba dawowa jikinta ba.

Tana zaune zuru Abdulhameed yayi sallama dakin ya shigo cikin nutsuwa sanye da Ralph Lauren sweatsets black da suka fito da haskensa sosai slippers ne a qafarsa masu tsada.

Baisan Husnah na dakin ba Saida ya shigo ya ganta zaune gefen maamah din duk a firgice gwanin tausayi.

Tana ganinsa taji sanyi da nutsuwa na San shigarta ta taso ta nufosa tana kokarin shige masa ya riqe hannuwanta tareda tareda Yana kallanta cikin nutsuwa yana cewa ta nutsu.

Nutsuwar take kokarin yi Amma bazata iyaba ta kasa.

Janta yayi suka dawo Palo ya zaunar da ita tareda sakin hannuwanta Yana kallan fuskanta data kumbura gaba Daya ta sauya kamanni.

Magana zaiyi Haydar Shima ya shigo palon Yana ganinsu ya qaraso a natse ya zauna gefen Husnah din tareda zuba mata idanuwansa baice komaiba itama kasa cewa komai din tayi ta fada jikinsa tana fashewa da kuka sosai Wani irin maraicin rashin uwa da Uba takeji Yana daibaiyeta Haydar ne kadai sanyin datake samu a rayuwarta sai Abdulhameed idan ta samesa to Kila ta samu me rarrashinta.

Shi kansa Haydar hawayen tausayinta da kaunarta yake ji na Neman cika idanuwansa Amma Yana buqatan nuna jarumtarsa ya tsayawa yar uwarsa sbd Shima a yanzu auren yakeso a daura mata da Abdul su tafi da ita ya Bata kulawan datake buqata hakama yasan Abdul din zai Bata kulawan da zata buqata ta dawo daidai kaman yanda itama takeson binsu din can.

Abdulhameed miqewa yayi ya Basu guri ya fice zuwa kitchen ya buqaci khaltume ta Aiko Farida ta kawo breakfast dinsu a dakin maamah.

Yana juyowa Farida ta biyo bayansa da katon basket Dake cike da kayan abincin nasu.

Suna shigowa ya tarar da Haydar ya nutsar da Husnah din da maganganun nutsuwa da kulawa ya kwantar mata da hankali sbd saita nutsu ne zata samu abinda takeso idan Dad yaga ta nutsu.

Ajiye basket din Farida tayi ta fara fidda komai ta Jere musu akan table din tsakiyan palon taje ta dauko sauran kayan ta qarasa jerawa ta fice.

Kallan Husnah Dake jikin Haydar har lokacin Abdul yayi Yana cewa tazo taci abinci.

Kaman yarinya qarama haka ta taso a sanyaye ta zo ta zauna kusa dashi har Saida ya Dan matsa kadan sbd taji fada da nasihar Haydar dayayi mata duk Tayi sanyi.

Abdulhameed ma maamah yaje yayiwa nasihar me shiga jiki duk da anriga anbata Gini tin tan Zane Amma dai lokacin gyara Bai wuce musu ba,
Fitowa yayi da itama cikin sanyi tazo ta zauna tareda su.

Haydar da Abdul ne suka sake musu nasihar a tare kafin suka sakasu cin abinci sukaci gaba dayansu kowannensu jiki a mace Babu Wanda ya iya cewa komai sun koma kaman sune ‘yayan su Abdul da Haydar din yanda suka nutsu da maganganun su Abdul din.

Abincin sukaci kaman marasa lafiya suna gamawa kowa yaje yayi wanka ya shirya ya kwanta baccin da Bai samuba tsakar dare kaman yanda su Haydar suka sakasu.

Bayan sunyi baccin dayake kaman na dole ne Haydar da Abdul fitowa sukai suka wuce asibiti dubo Amatu sbd sun shiga gaida Dad din bayanan ya fita Kuma sun tabbatarda asibiti ya tafi.

Suna Isa asibitin suka Tararda su Amatun basa Nan Dan haka Abdul ne ya kirata yaji suna gidan anty Farha,
Haydar na Jin an sallameta ta samu sauki kenan sai ya fasa zuwa gidan anty Farha din dubota ya wucewarsa gida Abdul ne kadai ya wuce can din.

Yana Isa gidan anty Farha ya Tararda Amatun zaune a Palo tayi wanka harta Saka doguwan Riga mara nauyi Daya sake bayyanarda cikinta karima data kawo mata fura da yoghurt me tsami datake so tana gefenta tana fada mata yanda Akai ta Samo me tsamin.

Zubawa Amatun idanuwansa yayi cikeda kulawa da kauna da farin cikin ganin zata fara hada zuriar kanta tareda mijin dayake tsananin Sonta da kaunarta.

Jin yayi Yana sake samun qwarin gwiwan kulawa da Husnah ya Bata kyakkyawan rayuwa da kulawa kaman yanda Dad dinta ke kulawa da tasa yar uwar.

Zaunawa yayi bayan ya amsa gaisuwar karima tana ficewa daga palon,
Anty Farha na ciki tana baccin gajiya.

Cikin kulawa ya tambayeta Yaya jikin nata tana kallansa ta amsa tana tambayarsa maamah.

Numfashi ya fara saukewa Yana fara zayyano mata abinda yake faruwa na auren maamah din da mum Aisha harma da Husnah dakuma auren Husnah din Daya dawo kansa ya Dora da tambayarta raayinta akan aurensa da Husnah Yana kallanta.

Shiru tayi cikin mamaki me girma da fargaban auren maamah din Dan kuwa abun yayi Wani iri Amma tana magana maamah zata ga laifinta musamman yanzu datake cike da fushi da ita akan cikin.

Maganar aurensa da Husnah kuwa rasa abin fada Tayi Dan kaman yanda Abdul din ya fada ko ita bazata taba So Husnah taje gidan nasu aure ba Dan kuwa mutuwa kwata kwata rayuwarta zatai Dan haka batajin zata Hana Abdul aurenta sbd kubutar da ita duk da abubuwan Dake tsakaninsu wannan Wani lamarin ne daban.

Ajiyan zuciya ya sauke da amincewan Amatun Dan kuwa bazaiso ya auri Husnah batareda yar uwar tasa na kaunar alaqar ba har cikin rantaba.

Shiru sukai kafin ta kallesa tana ajiye cup din hannunta ta tambayesa Haydar murya a sanyaye.

Bayaninsa yayi mata akan fushin da yayi Amma dai zai sauko sbd duk Basu kyauta masa ba zasuyita basa hakuri harya hakura din.

Maganar maamah ya fara yiwa Amatun itama Yana mata nata nasihar akan maamah uwa ce baa fushi da mahaifi komai zeyi maka Dan haka ta tabbatarda tayi magana da mamaah ta Bata hakuri duk da batada laifi.

Shiru tayi sbd Bata taba fushi da mahaifiyarta ba hasalima tsoro ne yake Sakata yin nesa da ita sbd kada ta shiga tashin hankali ta Saka maamah din cikin Bacin Rai.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

78
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button