Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 80

Sponsored Links

*************
Karima Daman tana kitchen a rufe tana aikinta tinda ASH din ya shigo gidan,
Anty Farha kuwa Dr beeba ta juya rakiya Shima Mr Jameel din bayansu ya bi Yana Dan sake yiwa Dr beeba Godia.

Acan mansion kuwa su kawu sun Yanke shawarar akaisu su biya su duba Amatu kafin wucewansu hakama maamah dole zatai magana da Amatun kafin wucewarta Dan haka bayan motocin sun fito Kai tsaye hanyar gidan Farha suka kamo.

ASH a natse ya Bude dakin ya shiga duk zuciyarsa ba dadi da zancen Dr beeba na fadin damuwa ne yake damun Abeedan.

Related Articles

Tura kofar dakin yayi bayan shigowansa idanuwansa akanta tana zaune tsakiyan gadonta sanye da Riga da wandon jeans Daya lafe jikinta sai rigar Ralph Lauren fara data Dan kwanta jikinta duk da freesize ce Rigan.

Kyakkyawar fuskarta ya zubawa idanuwansa datake jinsu a kanta Amma Bata dagoba ta kallesa kafin ya Maida kallansa kan cikinta ya Tako a natse ya zauna ahankali gefen gadon tareda janyota baice komaiba Saida ya shiga da ita gefen jikinsa ya rungume ya saki ajiyan zuciya kusan guda hudu a Jere kafin ya Bude Baki yace

“Good morning LA”

A natsenta ta amsa masa itama da ce masa…”Good morning”

Hannunta ya kama ahankali yakai bakinsa yayi kissing kadan kafin yace

“Yaya jikinki?
Did you eat your breakfast?” Yaqarasa fada Yana kallan abincin da aka aje mata Jere a trey kan bedside.

Gyada masa Kai tayi ahankali tana Dan Bude Baki tace

“Naji sauki”

Hannunsa ya Kai ya Dan dago fuskanta Yana kallan doguwar hancinta zuwa idanuwanta da suka nuna alaman kuka tai sosai sbd idanuwan sun Dan kumbura hancin Kuma yayi ja.

Tafin hannunsa ya Saka ahankali ya shafi idanuwan nata Yana Jin baisan Yaya zaiyi ya Sakata Bude masa zuciyarta ya wanke duka damuwa da bacin ran Daya Sakata a ciki ba.

“Meyasa kike damuwa bayan kinsan yanayinki Baya buqatan duk Wani damuwa?”” Yafada kalmomin cikin muryar Dake bayyanarda damuwansa akan yanayin nata.

Hawayen da batasan da su bane suka ciko idanuwanta kafin su sauko ya Ciro handkerchief ya taresu Yana kallanta da tsananin kulawa da damuwa yace

“Zaki hukunta ASH ne ta Hakan?
Wannan yayi tsauri sbd kukan naki Yana sakaki ciwo ne”

Fasa masa kuka kawai tayi take ya qarasa rikicewa cikin zuciyarsa Yana rasa abin yi sai kawai ya rungumeta Yana maimaita kalman sorry a sauti me bayyanarda damuwansa da halinda take ciki.

Kukan taci gaba da yi Yana sake shigar da ita jikinsa Yana rarrashinta kaman zai maidata cikinsa.

Ganin bazata Daina kukan ba Kuma kukan yankan zuciyarsa yakeyi Dan haka ya dagota Ya zaunar a qafafunsa yana share mata hawayen Yana sake Saka mata magana da sautin da ita kadaice take jinsa sbd qasan maqoshinsa da maganar ke fitowa.

Daqyar ya samu tayi shiru ya goge mata fuska ya kamata sukaje har ciki toilet din dakin ya rakata ta wanko fuskanta suka fito Yana riqe da hannunta duk bayajin dadin ransa.

Zaunawa suka sake yi yana kallanta Yana Dan sarqe hannunsa Daya da nata Yana sake rarrashinta.

Dago jajayen idanuwanta tayi ta Dan kallesa ya Bude Baki zaiyi magana Akai knocking kofar dakin anty Farha ce ta sanar dasu su maamah sunzo ganin Amatun.

Shiru yayi Yana kallan Amatun Dan ganin yanayinta idan Hakan yayi mata dadi kokuwa,
Ita Kuwa gabanta faduwa ya Dan yi tareda Jin tana Dan shiga fargaban haduwa da maamah sbd cikinta da rikicin da Akai akansa dakuma samun ASH din da sukai a gidan.

Kallansa tayi Taga Babu Wani yanayi na rashin Jin dadin samunsa da Akai Kokuma damuwan zuwan nasu da kunyar su gansa duk Babu ko Daya a tareda shi hasalima shi itan yakeson sanin idan zata iya fitan.

Numfashi ta sauke ahankali tareda saddaqarwa da komai sbd tinda cikinta ya bayyana ga duniya batada mafita ko zabi bare tinanin gardamawa ko boye waye uban cikin,

Ko maamah dai batada yanda zatai ta ci gaba da boye mata ko guje mata akan duk hukuncin da zatai akan cikin sbd kaddara ta riga fata.

Tashi tayi daga qafafunsa datake Kai a zaune tareda nufan dagowan hijab dinta ta dauka,
shine ya Saka mata hijabin da kansa Yana kallanta cikin kulawa ya furta

“Zaki iya fitan??

Gyada masa Kai tayi a hankali tana daidaita kanta ta nufi kofar dakin ta fito Yana gefenta suka nufo palon gidan Wanda kusan dukkaninsu kawun dasu maamah da kowa na palon.

Anty Farha ce ta fara ganin tahowar tasu ta juya da sauri ta kalli maamah da mum Aisha harma da Husnah da Haydar kafin ta dawo da kallanta kan ASH din sbd Bata dauka zai iya biyo Amatun su fito tare ba asan Yana gidan duk da motarsa Dake harabar gidan dasu Haydar zasu gane Amma ai ganin Mr Jameel zaisa su dauka shine yazo da motar ba ASH din ba.

Husnah,mum Aisha da maamah a tare suke kallan ASH din mamakin ganinsa da inda ya fito Yana Saka jikinsu gabaki daya sanyi,. Mum Aisha hawayenta kasa riquwa sukai suka fara gangarowa tana sharewa jiki ba qwari.

Husnah ma nata idanuwan cikowa sukai da hawayen sedai tana shanyewa batareda ta bari sun saukoba Wani ya Gani musamman Dad din nata.

Maamah qasa tayi da kanta itama nata idanuwan kaman zasu ciko da hawayen ta danne,
Haydar kuwa kallo daya yayiwa Amatun ya sauke kansa ganinta tareda Dad dinsa.

Abdulhameed Husnah da maamah yake kalla Yana fatan sun Dena Jin abinda suke ji abaya.

Su kawu Dake gefe rakube kuwa jajayen hakoransu suka ringa washewa suna Jin zamzam da ganin ASH guda Yana bin ‘yarsu.

Zaunawa yayi dukkaninsu kowa na sake gaidasa bai Wani tsayaba ya tashi suka bar gidan da Mr Jameel da shidai har lokacin Bai ganewa komaiba.

Bayan ficewansa tsit palon yayi Babu Wanda ya motsa bare magantuwa sbd kowa da abinda ya kashe jikinsa yayi sanyi laqwas.

Anty Farha ma shiru tayi sbd batama San ta Ina zata fara kame Kamen zancen ba ga Amatu ma duk tayi zuru ta rasa abin fada bayan gaisuwar da taiwa kowa harda maamah dasu kawu.

Abdulhameed ne yafara Dan gyaran murya Yana katse shirun da tambayar anty Farha ya jikin Amatun dakuma Dan tsokanarta Bata tayasa murnar aurensa ba.
Itama anty Farhan cikin sauri tana San sakin dariyar qarfin hali ta amshi zancen da Sako maganar auren tana tayasa murna tana yiwa Husnah ma congratulations kafin ta Kalli mum Aisha tanason tayata murna da fatan Allah ya Sanya alkhairi Amma tana gudun yanzu gidan ya rikice da sabon tashin hankali Azo asake laifin da baa San Ina abin zai tsaya ba.

Kan maamah ta Maida kallanta tana son magana itama Amma bazata iya ba Dan haka ta Maida fitarta ga su kawu da suketa washe Baki suna ta sambadawa Amatu albarka da fatan ta haihu lafiya.

Mum Aisha gaba Daya komawa tayi kaman an tsoma ta ruwa itada Husnah da hawayenta ke cigaba da cikowa tana hadiyewa seda Abdul ya lura da Hakan ya miqe hannunsa Daya ahankali ya Dora akan nata Daman itace a kusa dashi Dan yanzu kaman cingum take Neman zaman masa shi da Haydar sbd tsoro.

Dago idanuwanta tayi ta kallesa Shima ita yake kalla cikeda sanyi da kulawa akan ta kwantar da hankalinta karta sakawa zuciyarta komai.

Qura masa idanuwanta tayi tana Jin hawayenta na komawa,
Hannunta ya kama ya sarke da nasa Yana Dan sake bata nutsuwa batareda yayi magana ba.

Anty Farha ce ta cewa maamah ta shigo daga ciki suka miqe suka shige harda Amatu wadda Haydar kawai dayaqi kallanta take kalla sbd damuwan fushin datasan itama yanayi da ita.

Maamah da Amatu da Abdul ne suka shiga dakin Amatun harma da anty Farha wadda Bata Wani jima ba ta fito tabarsu suka qarasa magana bayan sun taru sun bawa maamah hakuri su ukun ita da Amatu da Abdul sun Kuma rarrasheta tareda tabbatarda ta nutsu ta yarda da kaddara akan komai Taga Allah ya kaddaro.

Sun Dan jima kafin suka fito mum Aisha dai tana zaune kaman ma Bata hayyacinta Dan Nisan datai a tinani.

Suna fitowa suka dauki Shirin tafiya Amatu na gefen maamah tanajin Sam hankalinta bazai taba Kwanciya da zaman maamah a kauye ba Dan haka batajin zata yarda da Hakan.

Har waje suka rakasu suka wuce bayan su kawu sun sake wa Amatun nasihan aure hakama maamah a karo na farko yau din data mata adduar samun farin cikin rayuwar auren.

Haydar ne dayaqi kulata har lokacinda zasu wuce ta kalla idanuwanta na cikowa da hawaye tai masa magana.

Tsayawa yayi tareda juyowa ya kalleta ya mata fatan samun lafiya ya wucewarsa.

Ko da suka wuce ta dawo cikin gidan Jin tayi Wani nauyi na zuciyarta ya sauka sbd mahaifiyarta data shirya da ita duk da ba fada sukeba Amma a zuciya sun kasa samun Nutsuwa da juna sai yau din.

Abdulhameed ticket ya siyawa kansa da Husnah da maamah Amma su kawu suka rufe ido sukace a mota tareda su maamah zata tafi.

Mum Aisha ma ticket dinta ta Siya tabi su Abdul din suka bi jirgi ba tareda sanin ASH ba suka wuce.

Haydar Daya ga an Hana maamah bin jirgi Saiya fasa siyan ticket din shi ya bisu a motocin sbd Abdul dayace Husnah da maamah subi jirgin shi zaibi su maamah sai Haydar yace ya tafi dasu Husnah din shi yabi su maamah din.

Su Abdul da Babu Bata lokaci ko wahala suka isa Yola Kai tsaye TALBAs mansion suka nufa da motan datazo daukansu.

Kafin su Isa an gyara wuta da ruwan gidan da komai harma da masu aikin duk sun dawo Dan haka Mansion din ya rayu.

Ga mamakinsu Koda suka Isa anata aiki ana tana Manson din biyu Daya maamah Daya mum Aisha.

Mum Aisha data Tararda Hakan Wani kukan farin ciki da sanyin zuciya ta fasa tana Jin asirinta ya rufu sbd da niyar guduwa tazo akan ta tafi kauyen Kuma idan ta gudu ba gurin zuwa ne da ita ba Dan haka taji ta Dan dawo hankalinta.

Su kawu dayake tin acan daman ASH ya sanar musu dasu maamah din ya Basu gidansa na yolan zaa Raba musu su zauna anan Kuma sun amince Dan haka ko zama Basu yiba duka wuce kauye sbd duk hankalinsu baa kwance yake ba Suma da tarin dukiyar da suka samo a matse suke dasu Isa kauye su raba su adana ko su siya gona da dabbobi Dan haka suka wucewarsu akan sai angama gyara an natsa zasu ringa zuwa gurin matayen nasu suna musu auren dangan Sanda.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

81
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button