Daurin Boye Hausa NovelHausa Novels

Daurin Boye 15

Sponsored Links

15

 

 

Related Articles

 

Qarfe takwas da rabi na daren ranar yana tsaye farfajiyar gidan,cikin sanyin san nan mai cike da nutsuwa yake qarewa wajen kallo tamkar mai wani nazarin abu na daban,sanye da shadda wannan karon sabon dinki daya siya ready made fara qal wanda kudinta bazai wuce naira dubu takwas ba baki daya,saidai kayan sun masa kyau ainun,haka Allah ya halicceshi wani irin jiki ne da shi mai kyau,komai arahar kaya ya saka suna amsarsa.

“Ah,muhammad ya ka tsaya daga nan?,kaifa dan gida ne daga yanzu ko ka manta?” Daddy da yayo tattaki tun daga parlournsa ya fito tarbarsa yake fadin haka,murmushi khalipha yayi,sai yaji kunya ta kamashi,ya dan sadda kanshi qasa yana shafa qeyarsa
“A’aha….kodai ba wajena akazo bane na koma?” Ya fada cikin zolaya yana murmushi
“A’ah….a’ah daddy” ya fada cikin yanayin kunyar,yana tuna karamcin mutumin wanda ya sani tun wasu shekaru baya da suka shude,da alama har kwanan gobe haka yake yana nan da karamcinsa,ba abinda ya sauyashi
“Ba damuwa ma koba wajena aka zo ba,muje ciki mu gaisa tukunna” a baya yabi daddyn suka taka har zuwa cikin parlournsa,cikin girmama juna suka gaisa ya tambayeshi anninsa da jikinta,ya amsa mishi lafiya lau take yanzu
“Ina fata dai komai lpy babu wata matsala ko?” Nauyi da kunya suka hanashi furta dukkan abinda yayi niyya,duk wani plan dinsa sai yaji ya ruguje,ya nemi dukkan hanzarinsa ya rasa shi,sai a sannan ya dinga tuna waye daddyn,wane irin halacci yayi musu a rayuwa?,banda shi da ya tabbatar ya rasa anninsa,banda shi a wannan rana da tuni yanzu yana gidan prison,banda shi da tuni yanzu bai a wannan bigiren da yake kai a yanzu,zaiyi wuya ya iya furta masa buqatarsa,idan da amana ruwa bazai dafa kifi ba,kuma rama halacci sai dan halak,bashi da manta alkhairin mutum a gareshi komai qanqantarsa
“Babu daddy alhamdulillah”ya ambata yana son tursasawa kanshi amsar duk wata qaddara da zata fadowa rayuwarsa
“To ma sha Allah…ni bari na kira maka indon da kaina” ya sake fada cikin zolaya yana ciro wayarsa daga aljihu ya lalubi mummy yace ta turo ayshan falon baqi.

Lantana ce ta shigo ta shaida mata lokacin da take tashi saman abun sallarta bata kai ga ko ninkewa ba,hakanan ta samu faduwar gaba duk da batasan dalilin kiran ba,kwanaki biyun hankalinta ya soma kwanciya kadan saboda ganin babu ta inda maganar aurenta ta sake tasowa,kowa harkar gabanshi yake,abun sallar ta aje hakanan ta fito da hijabin sallarta a jikinta tana takawa a hankali cikin fargaba.

Cikin sanyin nan nata da nutsuwa ta kutsa kai falon muryarta dauke da sallama,dukkansu suka amsa saidai khalipha bai iya dagowa ya dubeta ba saboda taraddadin wace ce indo,gefe guda ta samu ta gaida daddyn da baqonsa,baqon da bai dago ya kalleta ba,koda ya dago din batajin zata gane wane
“Ga baqonki nan indo…..kinsan da zuwanshi kika barshi tsaye a waje?…next time idan kika sake saikin bani ladar shigo miki da shi” ya fada da tsokana cikin amonsa sannan ya miqe yayi hanyar fita yana cewa
“Toh malam muhammadu…a gaida gida”
“Na gode daddy” abinda ya iya cewa kenan daddyn ya fice a falon aka barsu iya su biyu,shuru na ratsa falon,kowa najin baqunta tattare da shi,kowa da abinda zuciyarsa ke kai komo a kai.

A hankali ya daga kanshi dai dai da sanda itama ta tada kanta don ganin waye din duk da yadda zuciyarta ke luguden bugu,tare da yi mata gargadi da nuna mata kuskuren aikata hakan,a tare suka sauke idanunsu cikin na juna,karon farko ya tuna wace ce duk da cewa gani daya tak ya taba mata a rayuwarsa,saidai alkhairi bai mantuwa kamar yadda sharri bai mantuwa,yarinya ya gani wadda shekarunta basu kai na asma’u ba,hakanan shekarunta basu kai na amal zeenart ko rahama ba,farar bafulatana wanda bata da jiki sam,sai manyan fararen idanunta da suka sauka cikin nashi,daga haka bazaice yaga komai ko yaji komai ba,daga nata bangaren bata ganeshi ba ko daya,saidai abu guda da taji shine tausayin kanta da wani nauyi na musamman,ta san bata da wata daraja ko qima data rage mata a rayuwa,sadakar ko kyautar ta asma’u tayi ba tare da sanin daddyn ba,saidai ta yaya zata qaryatata bayan ita din tana jin kanta dai dai da baiwa maras ‘yanci,wadda bata da ikon fadin albarkacin bakinta.

Kusan shuru shi ya biyo baya babu wanda ya sake cewa da dan uwansa komai,kowa da abinda yake saqawa cikin zuciyarsa,haka nan khalipha yaji duk abinda yayi niyyar fada baida wani muhalli ko gurbi,me zai gaya mata da zata fahimta,basu san juna ba bare a kai ga batun fuskantar juna har a fahimci me abokin magana yake fada?kusan haka suka qarar da lokacin kamar masu gasar nuna tsantsar iya rashin magana,yana da abinda zaiyi da yawa hakan ya sanya ya miqe ya doshi fita,yana gab da ficewa ya tsaya hannayensa zube cikin aljihun rigarsa yana dan nazari kadan,kaman zaice wani abu sai kuma ya fasa ya rufe da
“Sai anjima” yasa kansa ya fice,ta jima zaune a wajen ta qurawa waje daya ido tana jin yadda zuciyarta ta kacame da lissafe lissafen da basu da tushe bare makama,ta sani cewa bata da wani abun yi saidai ta zubawa sarautar Allah ido,haka ta gaji da zaman ta miqe zuwa cikin gida.

Tana gab da dakinsu asma’u na fitowa cikin hanzarin da batasan na meye ba daga nata dakin,saita ja birki tana duban aysha kafin ta soma mata dariyar data saba qasa qasa
“Yaron oga ya tafi?….ina fata kun gayawa juna kalamai masu dadi ko?,ina tayaki murna fa aysha kinyi dace da samun kyakkyawan miji,ko banza zaki more kyau…..kinga fa nayi taimako,bakiyi biyu babu ba,wato ba kudi kuma babu kyau,kin tsira da abu daya a nan……” Bata tsaya ta gama jin kalaman banzanta ba ta sa kai zuwa cikin dakinta,tana iya jiyo dariyar shaqiyancin ta kafin ta gaji tayi gaba.

Gefan gado ta zube tana dafe da kanta,wasu hawaye masu dumi suka soma bin kuncinta,karo na biyu kenan…..karo na biyun da saura qiris yayi kamanceceniya dana baya,wai shin ko bata da rabon zabin abokin rayuwa ne,bata da rabo a soyayya?…me yasa take rasa soyayyar mutane da dama?me yasa qaddararta ke fadawa hannun mutane kala daban daban suna juyata yadda suka ga dama haka?,wai ita din ba mutum bace yar adam tamkar kowa?,ko bawa tana tunanin yana da yancin kansa ko yaya ne ta wasu fannin,a haka ta sulale ta kwanta hawaye na fita daga idanunta,tana jin kanta cikakkiyar marainiya,cikakkiyar mara gata wadda tafi duk wani mara gata rashin gata,ba dangi suna nan amma akawai ya babu,babu uba ga uwar da bata da maraba da wadda babu wanzuwarta a doron duniya tsahon shudewar lokutta,iskar kadaici na ratsata da narkakkiya kuma karyayyar zuciyar da da take tsammanin samuwar daidaituwarta taci gaba da zama cikin dakin ita daya har dare ya soma nisa bata sani ba,saida lokacin tashinta yin sallar dare yayi sannan ta ankara ta miqe ta shige bayi ta daura alwala kamar yadda ta saba tun wani zamani can baya,tun a sannan batasan muhimmancin abinda take ba,tun a sannan bata da yaqini kan abinda take tazo ta hau saman abun sallarta.

*******************

Sau uku yana sako kai parlour din zai shigo sai yaja ya koma,muryoyin da yake ji ne sam baya son ganinsu,duk randa suka hadu gaba da gaba kuwa saidai tsautsayi da qaddarar ranar zasu ganshi,a duk sanda ya gansu ko yaji muryoyinsu wasu abubuwa marasa dadi da suka faru shekarun baya ke masa tariya akwanyarsa fes,tariyar da baya buqatarta,da yana da hali zai dawo da rayuwarsa baya ne ya cire wannan wajen don ya daina tunawa da shi gaba daya,yana mamakin ma yadda sukan iya shigowa har cikin gidan nasu su dubi idanun anni suyi magana da ita.

Wannan karon daya koma din sai daya bada tazarar awa guda sannan ya sake shigowa sashen annin,ga sa’ar daya ci kuwa sun tafi.

Da sallama ya shiga annin na zaune qasan carfet qafafunta miqe tana jan carbi da alamu ciwon qafarta ne ya motsa,da kallo ta bishi tana son karantarsa saidai ya basar yaqi yadda hakan ta faru
“Sai yanzu ka dawo daga cewa bari kaje kayi wanka?”
“Wallahi anni na….”
“Bance ka rantse min ba…ga abincinka can” ta fada tana dubansa,miqewa yayi yaje ya zuba ya dawo gabanta ya zauna kamar yadda ya saba koda yaushe,saidai wannan karon babu hirar da suka saba yi,saboda duk yadda yaso ya manta da tunanin dake katse masa hanzari hakan ya faskara,yana da damuwa ga zuwansun gidansu ya qara masa wata damuwar,ya tsani su rabi gidansu sam saboda yana jin babu alkhairi sam tattare da su,ya bayyana qarara ba don Allah suke sonsu ba
“Ya maganar kudin registration din ibrahim…naji har yau shuru” lomar dake bakinsa ce ta tsaye masa,sai da yayi dagiyar hadiyeta sannan ya lumshe idonsa ya bude su kan annin
“Saboda shi suka zo?” Idan saboda shi ne karsu sake zuwa don girman Allah….zan dinga tura musu,haidar yazo ya bisu da shi”ya fada yana laluben number qanin nasa,bacin rai nason taso masa yana danneshi don baison annin ta gani,ido anni ta zuba masa,halin ruqo ba halin khalipha bane,amma wani sauyin yanayi da jama’ar da suka fada rayuwarsu sun sanya ala dole yana kwatanta halin a kansu,ita kanta badon koyarwar ma’aiki ba batajin akwai wani abu da zai sanya ta sake tada kai ta dubi idriss da iyalansa bare har taimako ya shigo ciki,saidai wasu dalilai da koyarwar addini su suka mata burki…hakanan ita din uwa ce,duk abinda ta aikata zai zama abun kwaikwayo ne ga tsatsonta a kansa zasu tashi,ajiyar zuciya ta saki bata sake tada masa zancansu ba don tasan radadi da yake ji a duk sanda aka masa zancansu,har haidar ya shigo khalipha ya masa transfer din kudin yace ya tsaya a atm ya cira ya kai musu,sai daya fice sannan annin ta sako wata hirar wadda ta mantar da shi damuwarsa,duk da tunaninsa na kasuwa….yana so ya sake komawa daddy…yana son su zauna ya fahimtar da shi yadda maganar take,amma kuma zamanshi da anninsa ya shafe komai.

*******************

Karo na biyu ya sake dawowa wajen daddyn,saidai girman halaccinsa da yake masa yawo cikin ido da qwaqwalwa yasa ya kasa furta masa wata magana makamanciyar wadda yake zuwa da ita,a wannan karon bai nemi ganin aysha ba,ya nuna sauri yake daddyn kawai yazo gaisarwa,saidai ita din ta ganshi sanda take cikin garden,ta kuma baro ciki ne saboda asma’u da qawayenta dake karakainarsu sake ba qaidi,uwa uba bata son hayaniyarsu wadda take ratsowa har cikin dakinta,hirace mara ma’ana da sam bata da buqatar jinta,ko kadan basu da kintsa bakinsu,har yazo ya fita din tana zaune wajen,shima din ya ganota,saidai yayi tsammanin bata ganshi ba.

Sau uku khalipha na zuwa saidai ya gaza furta komai,wani arashi kuma duk sanda zaizo tana hangoshi shigarsa da fitarsa,shi dinma yana ganota daga cikin garden din data mayar muhallin zamanta,baisan meke zaunar da ita a wajen ba,saidai yana zaton ko yanayin tsirran dake wajen ne ke qawatar da ita,amma bbai taba ganin tana wani abu da zai nuna hakan ba.

A zuwa na hudu ne ya nemi ganinta,yana son yayi aiki da shawarar da zuciyarsa ta bashi,ya fara sanin wace ita halayyarta da dabi’unta,hakan shi zai dorata a mizanin hukunci daya dace,yana tsoro kar yaje ya tafka kuskure,kar yayi gudun gara ne kuma ya tadda zago,sanda akai kiran nata wannan karon daga wanka ta fito akace mata tazo tayi baqi,mamaki ya mamayeta,ita din?,baqi kuma?,ina take da mutanen da suka damu da ita har zasuyi tattaki zuwa wajenta,aliya dai bata nan bare tace itace,bugu da qari ko kadan bata qaunar fitowa sararin gidan baki daya saboda yau sarkin isa da taqama hamid zaizo,hakan ta shafa mai ta zira atamfa riga da zani ta dora hijabinta ta fito.

Tun daga falo take duba baqin saidai bata ga kowa ba,lantana ce ta gaya mata yana can cikin lambu
“Waye” take tambayar kanta,kamar wadda ke a tsorace haka take takawa har zuwa cikin lambun,har ta isa tsakiya bata ga kowa ba,hakan ya sanya ta tsaya dude dube,sai data gaji ta juya da niyyar fitowa a nan ta hangoshi kan wasu kujeru dake can gefe guda na lambun,yana zaune da waya a hannunsa yana dannawa,dauke idanunta tayi daga kanshi gabanta na faduwa,wani irin kwarjini taga yayi mata irin wanda babu wani namiji data taba gani yayi mata,sai taji kaman ya cika wajen,kamar wani tsoro tsoronsa haka taji tana ji cikin jininta,duk da cewa itaba ba ma’abociyar kallon maza bace,bama maza ba ko mace ‘yar uwarta bata iya irin wannan kallon ba.

Bayan daya daga cikin kujerun ta tsaya tamkar mai tsoron wani abu,idanunta zube saman teburin dake gabansu
“Salamu alaikum” ta furta cikin muryarta mai sanyi wadda ta soma rawa rawa alamun ko yaushe tana iya sakin kuka,kujerar da take tsaye kusa da ita ya tura mata idanunshi a kanta yana karantarta,ta fuskanci me yake nufi ga kuma nauyi da taji idanunsa sun mata a kanta,hakan ya sanya bata jaa ba ta matsa kusa da ita ta zauna tana curewa waje daya kamar zai cutar da ita,sai data zauna din sannan ya amsa mata sallamar
“Suna na muhammad khalipha…kefa?” Ya tambaya yana maida vivo dinsa aljihun gaban rigarsa
“Aishatu….” Idanunsa ya dan lumshe kadan sannan ya budesu saboda girman da darajar sunan da yake gani,sunan anninshi ne hakan ya sanya yake ganin qimar duk mai sunan da shi sunan kansa,gyaran murya yayi bayan ya hade yatsunshi waje guda
“Ban sani ba…ko kina da masaniya kan abinda yake faruwa…abinda ‘yar uwarki tayi da abinda ke shirin faruwa a garemu gaba daya,da amincewarki?..da saninki?…ko da sa hannunki?”
“Ina mai baka shawarar ka bijirewa auren aishah,saboda bakasan wacece ita ba….sanin wace ita ya sanya asma’u shirya abinda ta shirya din” ta fada kanta tsaye,rauni da dakiya na tarayya cikin zuciyarta lokaci guda,abinda bata taba zaton yana haduwa cikin zuciyar dan adam cikin lokaci daya ba,idanu ya tsira mata cike fal da mamakin wacce iriyar mutum ce ita?,a yadda tayi maganar ya tabbata da shi matsoracin namiji ne babu abinda zai hanashi miqewa ya nemi arcewa,bai taba gamo da mutumin dake baiwa mutane shawarar su gujeshi ba komai girman laifin da yake aikatawa ba,amma fuskarta kawai ta karantar da shi akwai wani lamari mai girma dake cin zuciyarta wanda bazaiso yanke hukunci ba sai yasan meye shi,idanunshi ya janye daga kanta ya saki ajiyar zuciya bayan ya sarqafe yatsunsa na hagu da dama waje guda.

“Sannunku masoya” muryar asma’u cikin sautin amon dariya yayi kutse cikin nazarin da kowannensu ya fada,a tare suka daga kai suka dubeta ba tare da kowannensu yace komai ba
“Yaron oga an samu damar bullowa kenan?….hakan yayi kyau” ta qara fada cikin dariya dariyar da tafi gama fa izgili
“Allah ya barku tare,musha biki” ta kuma fadi tana dai dariyar izgilanci
“Ammm….yaron oga….ina muku fatan alkhairi fa a auren da zakuyi….saidai ina fatan ta gaya maka cewa ita din ba jinin gidan nan bace….sannan yana da kyau ka shirya zuwa qauyensu ka gano tushenta….don kada ma ta yaudareka tace maka nan ce mahaifarta ko daddy na shi ya haifeta ni sistern ta ce…na barku lafiya” ta fada tana ficewa daga lambun,yanayin kwalliyarta kawai ya isa ya gaya maka cewa hamid ne yazo,khalipha shi ya fara dauke idanunsa zuciyarsa na tafasa,yana jin kaman ya tashi ya nunawa asma’u true colour dinsa,yana jin kaman ya hukunta asma’u a wajen,mahaifinta shi ya fado masa a rai,tunashin da yayi shi ya katse masa dukkan wani hanzari nasa,tilas ya tattara duk wani fushi da bacin rai daya taso masa ya lanqwameshi ta hanyar sakin ajiyar zuciya mai tsaho,yana mamakin yadda ta zamto jinin daddy ‘yarsa tsatsonsa,ba shakka Allah dama ya fadi yana fitar da rayayye daga matacce ya kuma fitar da matacce daga rayayye,wani bari na zuciyarsa yaci gaba da tausarsa da danneshi yana gaya masa cewa AKWAI LOKACI…..

Idanunsa ne suka sauka kan fuskar aysha wadda tuni ta jiqe da hawaye,bakinsa ya bude zaiyi magana ta daga hannunta da sauri ta dakatar da shi
“Har abada tushena shine abun alfahari na koda kuwa wa na zama cikin doron qasa….har abada inason iyaye na komai lalacewarsu sune silar zuwa na duniya….har abada dangina sune dangina bani da makwafinsu da zan sauya su da su komai girman sabani ko rashin fahimta,ni aisha har abada ina son qauye ina taqama da shi saboda shine asalin kowanne dan adam koshi waye saidai idan shi din ya zama kaza ce ci ka goge bakinka” wadannan kalamai su suka sauka cikin kunnuwan khalipha da asma’u dake shirin ficewa a wajen,kamar zata tanka saita tuna hamid data bari yana jiranta kada ranshi ya baci yayi tafiyarsa,hakan ya sanya ta waiwayowa ta kalleta da niyyar bata gargadi,sai kuma tayi rashin sa’a idanun ayshan bai kanta ta sanyasu tsakiyar tafin hannunta kamar mai qayyade adadin jijiyoyin dake kaiwa hannun nata jini da dawo da shi,dole ta juya ta fice ba tare data samu damar maida raddi ba.

Wani irin abu shi ya shiga kaiwa da kawowa cikin zuciyarsa idanunshi a kanta,karon farko da ya yiwa wata mace kallon qurilla tsahon girmansa
“Bana buqatar sanin ko ke wace ce?….ki riqe tarihin rayuwarki naki ne.”jiqaqqun idanunta da suka jiqa har gashin idanunta suka qara fito da tsahonsu da baqinsu
“Ya zama dole kasan wace aysha matuqar zaka karbi aure na….rashin sanin wace ce ni ya ta’allaqa ne da hukuncin daka yanke wa karbar aurenmu”
“Kinsan waye daddy kuwa a wajena?,kinsan me ya taba yiwa rayuwata?”
“Kamar yadda bakasan waye ba a wajena da abinda ya yiwa tawa rayuwar yake kuma kan yi mata….indai haka ne dole kasan wace ni” ta fada hawayen idonta naci gaba da zuba.

“Suna na aishah umar sanda,hafaffiyar wani qauye cikin qaramar hukumar takai dake jihar kano takai,mahaifiyata sunanta naja’atu,mahaifina cikakken bafulata ni ne,hakan ya sanya sunansa na asali ya bata saidai a kirashi da baffale,mahaifiyata kuwa ‘yar manoma ce amma dukkansu mazauna qaramar hukumar takai ne,duk da irin wakaci ka tashin dake faruwa tsakanin manoma da makiyaya amma haka Allah ya qaddara aurensu,saidai irin abubuwan dana dinga gani bayan an haifeni na soma girma nasan cewa ba qaramin kai ruwa rana akayi da iyayen baffana ba kafin su yarda ya auri ummi na.

Ni kadai mahaifina ya haifa har ya rasu,nayi wata iriyar rayuwa daga tashina zuwa girmana,wanda tunda na girman baisan wani abu waishi qauna tausayi ko jin qai ba,bansan soyayya ba,bansan lallashi ba,bansan kula ba,rana tsaka na tashi na girma na gani a matsayin ‘YAR TSAKAR GIDA,da wahala na budi ido,da bauta na saba,da bin umarni ko hani nake aiki koda yaushe,babu mai cemin sannu,babu me cemin na gode,babu me cewa me yake damunki,babu mai cewa me kikeso meye bakya so?,mahaifiyata ta bar gidan ta barni da qananun shekaru,ta barni tun bani da wayo sanin ciwon kaina,bana ce ga abinda ya faru ba don bani da masaniya,a hannun kakata inna yelwa ta barni,saidai kuma hakan a baki kawai yake,mahaifina yana da yayye uku qanne hudu,dukkansu cikin gidan suke suda matansu da ‘ya’yansu,duk cikinsu babu mai mace daya,daga mai biyu sai mai uku,ga tarin yara da suke da shi,tunda na tashi nafi kowa rashin gata cikin gidan,kusan a tsakar gida nake qare rayuwata,hakanan duk wani aikin wahala na gidan yana wuya na,nice lungun baba auwalu,nice lungun baba sani,nice lungun baba salisu,nice na baba rabi’u,khamisu tasi’u,sabi’u,babu wanda ban gararamba a lungunsa yaransu na zaune,kuma ban isa nayi kuskure ko inyi ba dai dai ba,yadda akeso haka zanyi komai sauqi komai wuya,ba ruwansu da zafi sanyi rani da damina,kuma kakata tana kallo,asali ma sai na lura da babu abinda ya shafeta,ita kanta idan ta kama sai ta jani ta daka iya son ranta,duk cikin jikokinta ni tafi tsana,duk wanda zai hukunta ni koda hukuncin yafi girman abinda na aikata din ba damuwarta bane,saidai ta tayasu ma da jifana da miyagun kalmomi kala kala
“Shegiya ta gado baqin hali irin na gidansu uwarta naja,tur da jinin gidan saluhu,jinin fitsara jinin kafirar zuciya” wannan kalmar tun ban fahimtar me take nufi har nazo na ganeta,na kuma haddace ta ta zauna daram a kaina,bansan me nayi musu ba,bansan wanne girman laifi ne dani cikin gidan ba da kowa bai qaunata,yaqi jinina,tsangwamar bata tsaya iya cikin gidanmu ba,koda sauran mutane sai suke min abinda suka ga dama ganin bani da wani tsayayye wanda zai tsayan,ko cikin yara sa’anni na ina cin duka,kyara da tsangwama,musamman daya zamto nafi kowa qazanta na kuma fi kowa rashin gata,a lokacin mahaifina yana raye,bashi da abin cewa duk da cewa shima na lura bai wani damu dani sosai ba,yafi nuna kulawa ga sabuwar matarsa mai suna kuluwa,zuwan kuluwa gidan sai ya sake zama tamkar sabuwar babin azaba ne a tare da ni,yar kulawar da baba na ke nunawa kaina sai na rasa,ta janye hankalinsa tsaf,hakanan hatta da kakata ta koma qarqashin iko da mulkin kuluwa,a da babana kan zauna dani mu danyi hira,yakan yawaita cemin na yafe masa,zuwan kuluwa gidan da komawar inna yelwa qarqashin ikonta sai ya haddasa sababbin jam’iyyu kala kala a gidanmu da kuma kishin bal bal mai azabar zafi a tsakanin faccalolin,nidai a sannan bani ga tsuntsu bani ga tarko,ta rayuwata nake,duk inda na tattala ta sai anga an rushe,walau baba kuluwa ko sauran faccalolinta,kowa yagata yake figata yake,ina da son tsafta,ina son karatu kaman me,ina son gayu amma duka sun gagareni,duk da kaf cikin yaran gidan babu wanda ya damu da karatun saini daya,walau arabi ko boko,kuma babu wandaya matsanta musu kan hakan,son karatu na sai ya zama kamar wani sanabe ne ko iyayi ne a ganinsu da ganin ina nuna ai ni nafi kowa,hakan yasa aka qara qaimin datsemi duk wata qofa ta ilimi,tun sallar asuba idan na tashi nake bauta cikin gidan ba wanda ya damu da tsaftata ci na sha na suturata ko karatuna har dare ya shiga sannan ya maida haqarqarina na kwanta,da qyar nake samun sauran abinci naci ko sau biyu ne kacal a rana,haka zan hada guntu guntunsu duk lalacewarsa naci,watarana na kwana tsakar gida gefan dakin inna yelwa,watara na na kwana gefan turken awaki idan ta koreni daga qofar dakinta,watarana kuma ta barni daga cikin dakin nata amma daga bakin qofa komai sanyi komai damuna,kayan sawata kuwa a wani tsohon kwandon qarfe na shara suke,idan damina ta sauka haka zasuyita jiqewa ina matsewa ina shanyawa,dama gashi ba cikakken wanki suke samu ba.

Wani abu da Allah ya doramin shine son mahaifiyata da qulafucinta,saidai abinda ya soma girgixa hankalina fiye da dukkan abinda yake faruwa dani shine….” Tsinkewa maganar tayi daga harshenta,saboda wani daci da abu mai tauri daya riqe mata maqoshi,kuka nason kufcemata,aduk sanda ta tuna wannan gefan na rayuwarta bata iya jurewa

 

*mrs muhammad ce*??
[3/6, 8:49 PM] Binta Mustapha: *_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA MAI BUQATAR SAYA ZATA TUNTUBI WANNAN NUMBER*

0803811300

*ko kuma*

07067124863

*DB*

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button