Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 78

Sponsored Links

*************
Karfe goma Abdulhameed yabar gidan ya koma bayan sun jima suna magana sosai tsakaninsa da Amatun.

Mum Aisha har guduwa daga mansion din taso yi Amma Sam securities sun Hana kowa fita Dan haka dole ta dawo da motarta tayi parking ta dawo cikin kaman mahaukaciya Dan kuwa tin kayan jiya ne a jikinta gashi Naufal Se kiransa takeyi wayarsa kashe sbd har lokacin gidan Yola din baa mayar da wuta ba daqyar yake zuwa ya samo caji a gun masu caji da kekensa ta qafa Daya.

ASH ko breakfast ya kasa yi a cikin gidan sbd rashin dawowan su little Abeeda har lokacin Dan haka ya fahimci gidan Farha ta wuce kenan Bata dawo Nan din ba.

Related Articles

Numfashi ya sake me dumi Yana Dan Jin sanyin jiki na shigarsa ya daure ya kame ya shirya ya fito qarfe goma da Rabi lokacin Kuma Abdulhameed ya dawo gidan yayi parking mota ya fito kenan Mr Jameel Shima ya shigo harabar gidan yayi parking tasa motar ya dauko tsadaddun shaddodi da yadikan manya masu tsada ready made kusan duka size din Abdulhameed din ya wuce dasu ya miqawa Abdul din ya wuce gurin ASH Dake jiransa.

Abdul su kawu ne suka kirasa da kansu suka isar masa da sakon ASH din na yau din duka zaa daura auren harda nasa Dan haka Saiya shirya zama magidanci Kuma wlh ya riqe yar mutane da kyau tinda Shima gashinan tasa yar uwar ta samu guri har uban yar masu gida akeci akanta.

Shiru kawai Abdul yayi sbd Bai dauka tinda ya amince ba zaace zaa daura auren yanzu ba.

Fitowa yayi yaje ya sanar da maamah wadda itama zataso Daman a daura auren Husnah ta samu me kulawa da ita yanda ya kamata tinda su dole yanzu zasu bar Nan din.

Albarka ta sakawa auren tana danne damuwarta da halin datake ciki ita tareda fada masa ya riqe yar mutane da kyau da kulawa.

Mum Aisha na ganin lokaci ya sake matsowa ta fito a rikice ta koma gurin ASH ta ringa kuka tana rokonsa Amma Sam baima Kalli inda takeba Saida su kawu suka shigo kallo daya tayiwa dukkaninsu batareda ma tasan waye nata angon a cikinsu ba ta fasa kukan baqin ciki sbd ganin su dukan kaman baqin aljanu kowannensu karnin shaddarsa kawai zai iya sumar da ita,ita datake shafa turaren da kudinsa zai ciyar da kaf gidan Sanda Fulde din na tsawon kwanaki koma satittika Amma ace aure zatai da wainnan fataken.
Ficewa tai tana Jin Hawan jininta na tashi da baqin cikin ganinsu kawai.

Tana ficewa kawu ashiru ya bita da Satan kallo Dan shi gaba Daya Sonta ma qara shigarsa yakeyi,
‘dan nata ma da ake fada shi taje dashi agolanci zai amshesa ya hada da nasa manyan yayan ya riqe.

Husnah na daki ta rasa meyake mata dadi,ta rasa wa zata kira wa zata kama gashi Haydar yace tayi zamanta daki karya fito sai komai ya kammala sunga abinda ya faru tukuna.

Maamah ma tana dakinta zaune yanzu tinanin Amatu ne Kuma yake rufeta gashi dai ma zata koma kauye tabar Amatu anan karshe abinda taita tashin hankali Akai tana ji tana Gani Amatu zata cika gidan da yayan ASH batada ta cewa,
Amma Kuma har lokacin mamakin samun cikin Amatun Bai Dena jijjigata ba,
Tayaya ASH ya iya kebewa da Amatun har cikin ya samu?
Suna cikin gida Daya yarta tayi ciki harya bayyana Bata saniba,
Kunyar kanta da damuwa me nauyi ce ta sake danne zuciyarta gashi yanzu kiri Kiri tana kallo zata tafi tabarta zaman auren da Basu shirya ba.

Karfe goma sha Daya da mintina aka fara daura auren Abdulhameed Sanda Fulde da Husnah Ashraf Talba akan sadaki Naira dubu dari biyu Wanda Abdulhameed dinne ya biya abinsa da kansa mutane qalilan ne suka sheda a masallacin gidan nasa,
sai Kuma na maamah da kawu bello akan sadakinsa da Shima shine ya biya abinsa dubu Tara.
Na mum Aisha da kawu ashiru shine na qarshe da aka daura akan sadakinsa Shima Daya biya dubu Tara Dan dubu goma goma aka yanka musu sadakin.

Mum Aisha ko da aka gama daurin auren ciwonta ya tashi gaba Daya na hawan jini dole aka kwasheta zuwa asibiti,
Maamah kuwa kukan datasha kaman qaramar yarinya ita kadai cikin daki tana Jin baqin cikin su kawun Dan batasan ma inda zata fara zama da matansa ba da Babu hakuri ko hankali a cikinsu ba ko kadan,
Da anbarta ba aurenma zata iya komawa kauyen tayi zamanta Amma auren baida Wani amfani da girmanka.

Husnah na daki duk tayi zuru cikin matsanancin halin tsoro da fargaban Menene makomarta,
Yanda zuciyarta ke bugawa kaman zata fado da tsantsan tashin hankali ya Saka hannuwanta ma rawa sukeyi tana dai zaune cikin fita hayyacinta aka Bude kofar bedroom din nata aka shigo…

Haydar ne cikin cikin fararen manyan kaya da Dan adonsa Dan inganta auren yar uwarsa da nuna farin cikinsa Koda kuwa ana cikin damuwa ne.

Ganinsa ya Sakata juyo da jajayen idanuwanta ta zuba masa bugun zuciyarta na tsananta har yayi yawan da ba’a cika so ba.

Qarasowa yayi da sauri Dan ganin ta kusa rasa bugun zuciyarta yana isowa ya riqeta Yana cewa

“Andaura aurenki da Abd…..
Bai qarasa ba Idanuwanta suka juye tana sauke numfashi me qarfi ta sume a jikinsa Dan sanyin Daya ratsa kunnuwanta da zuciyarta haryafi karfin bugun zuciyarta a lokacin.

Tarota yayi jikinsa hankalinsa na tashi ya fara Ambatar sunanta da qarfi Yana Dan jijjigata.

Daukota yayi gaba Daya a ya Sauko zai fita da ita zuwa asibiti Abdulhameed Daya baro gurinsu kawu ya gansa da sauri ya qaraso Yana tambayar abinda ya sameta.

Kasa amsawa Haydar yayi Yana kallan fuskanta.

Hannuwa Abdulhameed din ya Saka ya karbeta daga jikin Haydar din Yana cewa

“Mu koma a kira likita yafi zuwan asibiti tinda kaman Suma ne”

Juyawa sukai suka koma saman tana jikin Abdul Daya daukota kaman Bai dauko budurwa ba kaman yarinya ya dauko.

Bedroom din nata suka koma ya kwantar da ita khaltume ta kawo ruwa da sauri tace a fara yayyara mata a Gani.

Abdul dinne ya Karba ya zuba mata a fuska Yana ambatar sunanta har lokacin tana jikinsa.

Ajiyan zuciya tafara saukewa tana jerowa kafin ta Bude idanuwanta ahankali tana sake sauke ajiyan zuciya Wani bayan Wani.

Khaltume na ganin Hakan ta sauke numfashi itama hakama Haydar shi kansa Abdul din ajiyan zuciya ya sauke.

Akan fuskar Abdul ta sauke idanuwanta ko kyaftawa Batayi jikinta gabaki daya ya matu Bata iya motsa ko hannunta ahankali ta Bude bakinta kuka na Neman kwace mata tace

“Thank you”

Kalman data furta ya Yanke zuciyar Haydar gaba Daya har hawaye suka ciko Idanuwansa ace tana yiwa namiji godiya Dan ya aureta.

Shi kansa Abdulhameed kalman yankan zuciyarsa tayi Dan haka ya dora hannunsa ahankali kan bakinta tareda girgiza mata Kai yana kallan cikin idanuwanta yace

“Dad dinki Bai Bani aurenki Dan kice thank you ba Ya bani ne sbd yasan kinada mahimmanci me girma a zuciyarsa da bazai iya Bada ki kauyen ba”

Kalamansa suka Saka hawayen cikin idanuwanta saukowa tana Jin zuciyarta na samun nutsuwan fara dawowa hayyacinta idan har da gaske tanada sauran mahimmanci a zuciyar Dad dinta.

Haydar juyawa yayi ya fita Dan amsa wayar iyayensu na porthcrt da yanzu ne suka gama magana da ASH ya sanar dasu auren Husnah din.

Bayan ficewan Haydar Shima Abdulhameed din sake rarrashinta yayi da magana ta sake dawowa hayyacinta kafin ya fice daga dakin tabi sa da kallo tana Jin yanzu Kuma da aka daura nata auren dashi batasan tayaya zasuyi zaman aurenba da Wanda ta girma duk da mantawama tayi da Hakan kwata kwata Amma dai koma yayane zuciyarta tana samun Nutsuwa da kulawansa tin kafin su zo yanzu tun suna Yara.

Ana gama daurin auren da duka Wani gaishe gaishe Akai Sallahn Azahar ASH ya shige.

Abinci yaci sama sama ya shige sashensa Babu Wanda ya sake ganinsa sai laasar ya fito cikin Shirin fita Bai buqatan driver sbd Mr Jameel Baya Nan da kansa yaja mota ya fita Kai tsaye gidan Farha ya nufa.

Ko Daya Isa motar Mr Jameel tana gidan Shima yanata ganin shege a gun Farha da gaba Daya ya rasa gane kanta duk ASH din ya ja masa.

Ganin Mr Jameel ya Saka ASH Dan kamewa Shima Mr Jameel din ganin ASH ya sakashi mamaki Amma ya boye ya danne mamakin tareda masa barka da zuwa ya masa jagora zuwa ciki Dan shi yafi awa Daya a harabar estate din Amma Farha taqi fitowa Dan haka zuwan ASH zai basa Dama da saukin lamarin tinda shi dole a iso dashi ciki sbd matarsa datake ciki.

Kofar palon yayi knocking tareda danna door bell lokaci daya

Karima na palon Dan haka Koda taji door bell din zuwa kawai tayi ta Bude
Gani Mr Jameel da ASH da kansa ya Sakata saurin yin gefe kanta a qasa cikin tsananin girmamawa ta musu sannu da zuwa tana gaidasu.

Lafiyayyar Palo ne me girma Daya Hadu sosai Dan haka guri Mr Jameel ya nunawa ASH din ya zauna Yana sake Saka kiran numbern Amatun a karo na kusan dari da Wani abun Bata dagawa karshe ma wayar a kashe.

Anty Farha na dakinta tana Shirin fita tareda karima siyayyar wasu abubuwan buqatan Amatun Dan Mr Jameel din dayake waje zata Saka ya kaisu ya dawo dasu Dan haka Bata San da baqin ba Saida ta fito a shirye sai ganin the great ASH TALBA tayi zaune palon Ya gauraya musu numfashin palon gaba Daya da qamshinsa me sanyi da gigitarwa.

Rikicewa tayi sbd ba zatan ganinsa da kwarjinin Daya cike musu gurin dashi Dan haka murya duk a rude ta Dake suka gaisa tace bara ta kira Amatu.

Shiga tayi dakin Amatun ta Tararda tana wanka ta fita ta sanar masa tana wanka.

Mr Jameel da duk ya gama susucewa da ganin Farha din fita yayi daga waje itama Farha din text tayiwa Amatu cewan ASH TALBA na gidan ta bi bayan Mr Jameel karima na bayanta suka fita bayan ta sanar masa Amatun zata fito.
Suna fita Mr Jameel ya juyowa Yana kallanta ta daure fuska tana sake Jin zafinsa na qin sanar mata tareda ASH din sukazo bare Amatu ta sani.

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

79
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button