Daurin Boye Hausa NovelHausa Novels

Daurin Boye 53

Sponsored Links

53

Tunda gari ya waye ranar bata shiga sashen anni ba,tana sashensu bayan ta gama duka gyare gyaren da zatayi ta sake kwanciya,ta ware fanka da acn dake falon duka saboda zafin da ake zubawa,wanda alamun zuwan damina duka sun gama bayyana,donko a jiya hadari sosai garin ya hada har aka tsammaci samun ruwan sama,saidai ruwan bai samu ba sai yayyafi da akayi wanda shi ya sake tada zafi a garin duka yau,da kuma wani sabon hadarin dake hadowa kadan kadan yana curewa waje daya gami da bada kala mai duhu,hakan ya sanya rana ta kasa samun dama fidda haskenta,qarfe hudu saura ta tashi daga bacci,ta daura alwala ta bada faralin sallah sannan ta shiga bandaki ta saki ruwa mai sanyi ba tare data sirka ba tayi wanka,hakan ya haifarwa da zuciyarta wani irin nishadi,zuciyar da gangar jikin dukka sukayi fes dasu,iskar dake busowa cikin windows din dakin tayi mata dari,sai taji tana bata wani sanyi na musamman dake ratsawa har cikin qwaqwalwa da zuciyarta.

Tana shafawa qafafunta mai murmushi ya subuce a fuskarta sabida tuna hirarsu da khalipha ta jiya,sassanyar muryarshi,yanayin maganarshi dake fita a nutse da sauransu,saita kada kai kawai tana dariya,itama sai taga wautarta,ba lallai yana nufin abinda ya fada din ba,don yanayin maganar bai nuna cikin zafi ko fushi yayita ba,bayan ta kammala ta shafa powder da man lebe kadan don kada ya dameta,jikinta ta feshe da turare sannan ta ciro kayanta da tuni dama sun rine da qamshin turaren wuta na kaya,doguwar rigar material ce cotton mai taushi yadda bazai dameta ba,saidai hannun rigar iya dantsenta ya tsaya,sai kuma mayafinshi wanda tayi rolling daya sauka mata har gwiwar hannu ya rufe hannun nata kenan bayan ta matse kanta da ribbom wanda yasha relaxer jiya,fuskarta ta kalla a mudubi,kayan sun mata kyau sosai,bata taba sanyasu ba saiyau,bata zaci ka zasuyi mata kyau haka ba,plat din takalmi ta sanya wanda ya dace da kayan sannan ta zira carbinta a yatsanta ta fito daga sashen.

Related Articles

Maryam ce kawai zaune a falon,saboda haka sallama tayi mata don fita haqqin addini,ganin ta amsa mata saita wuce kitchen ba tare data ce mata komai ba,don ta lura tunda annin ta tafi kowa kanshi rawa yake,dama ita maryam ba magana take mata ba,hakan ya sanya itama ta yi mata aji irin wanda ya dace da ita ta sanyata.

Bara’atu ke kiciniyar aiki ita kadsi,duk kitchen din a lalace yake kaman wanda akayi dafe dafe na mutum talatin
“Sannu da fitowar uwar masu gida” murmushi ta saki saita tuna da baba atika,tayi kewarsu sosai ita da anni
“Yauwa bara’atu sannu da aiki,ya haka gaba daya kitchen din ya kacame?” Ajiyar numfashi tayi sannan tace
“Ai kinsan aikin su waye,wallahi bansan me yasa suke abu ba bayan sunsan bai kamata ba sarai” sai aysha taji ranta ya baci,karo na farko tun sanda suka soma iskance iskancensu na kowacce ta dafa abinda ranta yayi mata,koda anyi girkin gida in general,koda su haidar dake yaran gidan duk abinda bara’atun ta dafa ci suke,bare ita da abinci bai dameta ba
“Kiyi haquri,komai mai wucewa ne,da zarar anni ta dawo naga wanda zaici gaba da yin hakan” aysha ta fada tana tausar zuciyarta,don bata son tayi musu magana sam,hannu ta sanya tana taya bara’atun gyaran kitchen din,sai da taga komai ya hau saiti sannan ta bar mata sauran,ta samu waje ta zauna suna jira jifa jifa,bayan ta zuba dan abincin da zata ci cikin plate.

Kadan kadan take tsakurar abincin suna hirarsu,bata wani ci da yawa ba zeenart ta shigo kitchen,tana ganin ayshan ta hade girar sama data qasa,tana yiwa ayshan kallon wata babbar naqasu a garesu,wadda ta kawo cikas da kuma hana ci gaban gudanuwar dukkan al’amuransu
“Bara’atu,maza maza dafamin couse jallop,ki saka nama da yawa a ciki yunwa nakeji” a ladabce bara’atun tace da ita
“Gafa abincin da kika asaka a aka dafa dazun baki cinye ba,sannan maryam da anty rahama dukansu an dafa musu abinci gasunan duk ba wanda ya cinye,ki duba ko wani abun a ciki zaiyi miki” ta fada tana buda mata fulasan dake shaqe da abinci
“Dalla malama ban tambayeki wannan ba,couse couse nake sha’awa shi nace ko dafamin”
“Ba za’a sake dafa komai ba a gidan nan sai Allah ya kaimu gobe” aysha ta fada hankali kwance kuma kari na farko tunda suka fara rashin mutunce mutuncensu,,saidai can qasan ranta a hasale take,ta karanci takunsu gaba dayansu babu abinda ke damunsu face tsantsar mugunta da almubazzaranci,saidai muguntar da qetar ma tafi yawa,waiwayawa zeenart tayi tana dubanta
“Au,harda su kaza a cin danqo?,ke kuma waya saka da ke?to bari na gaya miki tun ba’ayi nisa ba baki isa ba”cokalin hannunta ta aje sannan ta amsata
” na isa?,ban isa ba duka wannan bata taso ba ba’akai ga can ba,magana daya ce babu abinda za’a sake dafawa a gidan nan saidai idan har mun iya cinye duk abincin dake gidan nan muna da buqatar qari to wannan fa,barema nasan wannan abincin saidai a fitarwa da mabuqata a waje”
“Ke aisha!’muryar rahama dake takowa cikin kitchen din ta katsewa zeenart niyyar bata amsa da takeyi,hannunta harde a qirji fuskarta a dinke tsaf ta qaraso gaban ayshan,hannu kawai ta miqa mata sannan tace
“Bani muqullin dakin anni”sosai ta dubi rahaman cikin ido sannan tace
“Bamuyi wannan da anni ba”
“Ki bani malama ko,abina zan dauko a ciki”
“Idan kina da buqatarsa saidai ki jirayi dawowarta,saboda amana ce a gareni bazan iya wofantar da ita ba,ni dinma ban sake taka dakin ba tun randa na rufeshi”ta bata amsa tana janyo faranti ta rufe abincin dake gefanta,tsaiwa rahaman ta gyara tana dubanta cikin bacin rai
” ke ki saurara fa,naga alamun kina wuce gona da iri,saboda kinga an zuba miko ido kina yadda kikaga dama,toba tsoronki kowa keji ba”
“Duk saboda taga anni ta daure mata gindi ai take komai,ta fifitata a kanmu” zeenart dake cike ta fada
“Koma meya karki manta auroki akayi,a yau idan aka sakeki.magana ta qare,hakanan ana iya sauya mata amma dan uwa komai lalacewarshi lalala lalala”
“Don Allah anty rahama duka mai ya kawo wannan maganganun marasa dadi haka?” Bara’atu ta fada cikin tsoro da nuna rashin jin dadi,da hannu aysha ta dakatar da ita,murmushi ta saki tana dan kada qafarta kadan kadan sannan ta dubesu daya bayan daya
“Shi dan uwa suna ya tara ai,baku da labari?,da wani dan uwan gwara bare sau dubu?” Dukkansu sai kowacce tasha jinin jikinta,ba zasu so ace tasan komai game dasu ba,ganin karta ramfo wani abu ya sanya rahama sake yunqurowa cikin kurari tace
“Malama ki bani maqullin dakin uwarki anni tunda indai bana uwarrr……..”
“Rahama!!” Dakakkiyar muryarshi mai cike da mazantaka ta karade ilahirin kitchen din gami da bada sautin amsa kuwwa,ba rahama ba hatta bara’atu da zeenart hantar cikinsu sai data kada,da hanzari dukkansu suka waiwaya bakin qofa,yana takowa ne cike da nutsuwa saidai kana duban fuskarshi zaka san cewa ran ‘yan maza ya baci,tun kafin ya iso zeenart ta samu wajen jingina,yayin da rahama ta gyara tsaiwarta kamar mai shirin tarbar isowarshi saidai sam jikinta ne ke rawa takeson bawa kanta qwarin gwiwa,sai daya iso tsakiyarsu ya dubesu tsaf,sannan cikin wani irin sauti yace
“Matata?,kukewa haka a cikin gidanta?” Ya jefesu da tambayar yana binsu da kallo,zeenart kam babu bakin magana,sai rahama ce don kada ta bada kanta da shekarunta tayi qarfin halin cewa
“Haba khalipha?,kai bakagani ba kuma bakasan duk abinda take mana ba tunda anni ta tafi don kawai ta……”
“Will you shutup kosai nayi qasa qasa dake a nan” zaro ido tayi cikin mamaki,kalmar da bai taba gaya mata ita ba koda wasa,ko vanza yana dan bata girmanta ta wani bangaren saboda shekarunsu da suka kusa zuwa daya,waiwayawa yayi ya yiwa zeenart wani kallo wanda ya sanya take gumi ya rufeta
“Har da ke ko?….stupid,idiot….banda darajar anni da kuke ci ke kin isa kiga matata ma nare ki samu damar yin sa’insa da ita?banda kima da isar da anni ke dashi kin isa cin abincin gida na?,banda anni abincin gidana ko wanda na zubar ne bazan lamunci kuci ba” sai ya waiwaya wajen rahama
“Baki da damar da zaki nuna cewa anni wata ce a wajenki ko ke wata ce a wajenta,sanda muke wahala daga wannan mataki zuwa wancan na rayuwa kuna ina?,sanda muke tsakanin mutuwa da rayuwa kun taba tunawa damu?,kun taba kwana da tunanin ya rayuwar ayshatu zata kasance bayan kun sallamata a dangi?,to na meye a yanzu da muka samu nutsuwar zuciya da gangar jiki duka zaku kutso cikin rayuwarmu ku hanamu sukuni?,mu ba wawaye bane hakanan kyautatawa ba rashin sanin ciwo da darajar kai bane,saka sharri da alkhairi bai nufin ka manta komai daya faru,saka sharri da alkhairi bai nufin kai shashasha ne koka sarayar da dukka haqqi da mutuncinka” waiwayawa yayi ya dubi zeenart cikin kakkausar murya
“Kije ki kiramin dukkan yarinyar da tayi saura cikin gidan nan na baku minti biyu kacal” da hanzarinta ta fice,ba jimawa sai gasu sun dawo gaba daya,yatsunshi ya hada ya murza suka bata sauti sannan cikin kaushi yace
“Na baku nan da awa guda kowacce qarfe shida tayi mata cikin gidan mahaifanta,karku yadda na fito sallar magariba na samu daya daga cikinku…ko wacece kuwa…kome nisan da take dashi” ya qarashe maganar idanunshi yana kan rahama,tasan da ita yake ita da take nijer,wani abu mai tauri ta hadiye idanunta sun sauya launi saboda bacin rai,bai kuma bi ta kansu ba ya damqi hannun aysha da duka take jin babu dadi cikin ranta,tamkar ita ta zama sila kenan ta faruwar komai,batasan ya anni zata dauki hukuncin ba,kada hakan ya zama Silar tabarbarewar kyakkyawar alaqar dake tsakaninsu,haka suka ratsasu suka fice tana biye da shi.

A hankali ya tura qofar sashen nasu ya sanya kai tana biye dashi,sanyi da qamshin dake falon ya cika hancinsa ya haifar masa da wata nutsuwa ta musamman,suna isa falon ya aje jakar hannunshi ba tare daya saketa ba,idanunta ta daga ta dubi qwayar idanunshi,ta sauya kala hakanan kana dubansu kasan an tono wani abu dake zuciyarshi,sai ta zame hannyenta cikin sauri ya rungumoshi ta baya,kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya shi da ita,bacin ran daya tabashi sai taji duka babu dadi,bai kamata daga dawowarsa yaci karo da wata matsala ba,ya kamata zuwa yanzu ya samu hutu da kulawa da kuma dukkan wani kwanciyar hankali daya kamata,bata taba ganin bacin rai a fuskarshi kamar haka ba,bata taba ganin fadanshi kamar yau ba,da alama wannan gyambon dake zuciyarshi ne aka taba,sai taji zuciyarta ta karye,hawaye suka biyo kuncinta,wanda sukayi nasarar taba jikinsa,idanunshi na lumshe ya sanya hannunshi ya dawo da ita gabanshi,ya bude hannayensa ya sakata cikin faffadan qirjinsa ya maida hannayenshi ya kulleta gam,muryarshi can qasa yace
“Meye abun kuka?”
“Bai kamata ace wannan ne abu na farko da zaka tarar ba bayan ka dauki wani lokaci baka gida” ta furta cikin sanyinta da muryarta data bayyana kukanta qarara,tattausan tafin hannunshi ya sanya ya soma goge mata fuska,har a lokacin tana jikinsa
“Abu mafi ciwo shine abinda sukayi miki,me yasa kika tsaya saurarensu da banxayen maganganunsu?,me yasa bakiyu umarnin an fitar miki dasu daga gidanki ba?,ke din ba sa’arsu bace,darajarki da tasu ba daya bace..”
“Kayi haqur…..” Ta fada cikin raunin murya da zuciya gaba daya,saidai bai barta ta qarashe furucin nata ba ya hade bakinshi da nata cikin wani irin zafin nama da ba zatan da bata taba tsammata ba.

A hankali ya zare bakinsa kana ya dan dafe kanshi
“Ya salam” ya furta cikin matuqar sanyi,da hanzari ta dubeshi duk da sanyin da jikinta yayi matuqa
“Me ya faru,ya khalip….” Ta kasa qarasawa tana dubanshi,dubanta yayi suka hada idani,duk da yadda kanshi ke sarawa amma hakan bai hanashi tuno yanayin daya shiga ba,idanu daya ya kashe mata kafin yace
“Kaina”
“Sannu am sorry,ka zauna pls” ta fada tana nuna mishi kujera hannunta daya riqe da nashi hannun,sai ya kalle hannayen nasu dake cikin na juna,ya daga yakai bakinsa yayi kissing kafin ya saki a hankali ya koma saman daya daga cikin kujerun ya zauna,tausayinshi take ji,ciwon kan da su suka zama silarshi,gashi kuma basu qyaleshi ba suna haddasa tashinsa lokaci zuwa lokaci,sunkuyawa tayi a nutse ta dauki jakarshi daya aje a wajen ta nufi bedroom dinsu.

Minti uku kafin ta fito ta sameshi idanunsa a rufe
“Ga ruwa can ko watsa ko zaka ji dadin jikinka” a hankali ya bude idanun nashi ya warasu a kanta,sun qara girma hakanan sun sauya launi,sai taji sun mata nauyi da kwarjini da yawa,kanta ta dan dauke tana basarwa,kunya na lullubeta sakamakon tunawa da tayi da abinda ya faru daxu
“Yau garin akwai zafi,hadarine tun jiya kuma ruwa bai sauka b….” Bata qarasa ba ta jita cikin jikinshi,saitayi sak kunya na addabarta,bakinsa yakai saitin kunnenta
“Ki shirya kayanki kafin na fito” a hankali ya saketa yana takawa zuwa cikn dakin gadon yana jin yadda kanshi ke sarawa,yasan mawuyacine idan baiyi jiyya yau zuwa gobe ba,yayin daya barta nan tsaye tana saqe saqen me yake nufi?,watsar da wannan tunanin tayi ta shiga kitchen dinsu cikin hanzari ta soma sama masa abinda zai saka a cikinsa mai sauqi da dad’i.

Har ta kammala komai ta shirya bata ji motsi ko fitowarsa ba,duk sai ta kasa zama,saboda haka ta shirya komai ta tura qofar dakin duk da yadda zuciyarta ke gargadarta.

Zaune yake daure da towel,hannunshi daya dafe da kanshi,yayin da daya hannun yake amsa waya,yanayin yadda yake amsar wayar ya tabbatar mata ranshi a bace yake,magana ta qarshe yayi ya katse kiran,sai ya sake kiran wata number,haidar ya kira yace su dawo gida shida mus’ab,sannan ya sake kiran wani layin shima yayi magana ta ‘yan sakanni ya sauke wayar a kunnensa,kashe wayar yayi gaba daya ya ajeta gefanshi,idanunsa suka sauka akanta,ya saki qaramar ajiyar zuciya yana jin bacin ranshi yana zaganyewa,idanunsa ya lumshe cikin ranshi yana addu’ar Allah ya sanya ta zama sanyin idaniya a gareshi,ta fahimceshi ta soshi cikin qanqanin lokaci kamar ko fiye da yadda yake sonta
“Uwaishah!” Ya kirata cikin taushin nan dake kasheta,kasa amsa mishi tayi da.baki saida idanu,wanda hakan ya masa tasiri matuqa
“Taimaka min…” Sai.yayi mata nuni da ma’ajiyar kayanshi,ta fahimci me yake nufi,saboda haka ta miqe a nutse zuwa wajen shi kuma ya bita da kallo,kayan data sanya din sun amsheta sun burgeshi qwarai,sun fidda duk wata qira tata,wani azababben kishi daya sake sanya kanshi sarawa yaji ya saukar masa,saiya dafe kan nashi,har ta dauko kayan tazo gefanshi ta aje masa,ta juya da niyyar fita yace da.ita sanda ya.miqe ya ware kayan zai sanya
“Karki motsa ko ina,samu waje ki zauna” hakanan ta zauna inda ta tashi,ta dan kauda idonta gefe don kada ta kalleshi,ya fahimceta sarai,sai yaci gaba da sanya kayanshi har ya kammala,

Wata jaka ya janyo gabanshi ya soma hada wasu kaya cikin wata jaka,kayan abinci ta aje tana murza tafin hannunta
“Ga abinci nan” ta furta cikin sanyi da nutsuwa,kallonta yayi da idanun nan nasa dake mata kwarjini matuqa
“Ki shirya abinda zaki shirya nan da minti biyar” kamar zata tamnayeshi sai kuma ta fasa,koma meye ta sani bazai cutar sa ita ba,saita qarasa a hankali ta amshi jakar da yake saka kayayyakin a ciki taci gaba da sanya mishi,gefe daya ya koma ya zauna kawai yana binta da kallo ta qasan ido,duk wani motsinta yana biye da ita,duk da ciwon kan dake matsa mishi kadan kadan amma sai yake jin dadin kallonta fiye da tunani.

Bayan ta kammala.itama ta debi ‘yan qananun abubuwan da take da buqata ta zuba a tata jakar,sai data gama tsaf ya juyo da niyyar sanar masa taga ita yake kalla
“Na gama” ta fadi tana neman wajen zama,saiya ciro wayarshi tana ji ya kira sunan mus’ab da haidar da alama da daya daga cikinsu yake sake magana,bayan ya gama saiya kashe wayar ya aje,yaci gaba da kallonta cikin zuciyarshi yana wassafa yadda zai dasa mata sonshi da qaunarshi mai tafiya da hankali da kuma ruhi,ba’a dauki dogon lokaci ba suka jiyo knocking,saiya miqe a hankali cikin mutuwar jiki ya nufi qofar fita yana cewa
“Ki sanya mayafinki ki taho” hijabi ta sanya saman kayan jikinta,ta dauki jakar hannunta sannan ta fito falon,suna tsaye su uku,haidar mus’ab da shi khaliphan yana miqa musu key
“Kada yarinyar da kuka sake bari ta zauna cikin gidan nan har anni ta dawo,ku kulle ko ina zanyi magana da securities din gidan”
“Toh yaya” haidar ya fada yana karbar muqullin
“Mus’ab shiga ciki ka daukon jaka ka sameni a mota” ya fada yana yin gaba tana biye da shi.

Motoci biyu ne tsaye suna jiransu,da kanshi ya bude mata mazaunin baya kamar yadda ya dinga mata wancan karon,ta shiga shima yabi bayanta,mus’ab ya sanya kayan a motar ya rufe sannna ya zagayo ya musu sallama bayan ya miqo musu kwandon abincin da ayshan ta hada wanda baici ba,bata sani ba koshi yace ya dauko din,driver yaja motar suka fita daga gidan.

Shuru motar ta dauka,idanunshi na rufe da alama ciwon kan ke takura mishi,duk sai taji bata ji dadi ba,ta dokanta ta ganshi sai gashi yazo cikin bahagon yanayi
“Sannu” ta furta cikin nuna damuwa da kulawa,idanunsa da suka qara girma ya ware a kanta,murmushi ya sakar mata wanda ya sake sanyata cikin rudu,hannunshi yakai ya dora saman nata hannun sai ya maida idanun nashi yadda suke,yana jin yadda laushin fatarta da dumin jikinta ke ratsa shi

Tafiya ce da bata wuce ta minti ashirin ba suka shigo cikin wata unguwa,a ido kawai ya isa yasa ka gane kyau da tsari da kuma yanayin wadata da jama’ar unguwar keda,sai takejin kamar tasan unguwar kota taba ganinta,a hankali motocin suka ci gaba da tafiya har xuwa qofar wani katafaren gida daya tilastata daga kai ta kalleshi,horn daya akayi qofar gidan ta wangale,sai a sannan taga yayi mata kama da gidanta da aka fara kawota.

A harabar aje motoci sukayi parking
“Zauna ina zuwa” ya fada yana ficewa,ta cikin motar tana iya hango abinda ke faruwa,kayan da sukazo dasu aka shiga dasu ciki har kayan abincinsu,tsahon minti biyar sannan ya dawo ya mata izinin fita,wannan karon hannunshi cikin nata suka dinga takawa zuwa cikin gidan,suna tafiya tana sake gane gidan dukda ba wani shahararren kallo tayi masa ba tun a wancan lokacin.

Kwandon abincin dake aje a falon ya sunkuya zai dauka tayi saurin dauka da azama,suka hada ido tadan basar sukaci gaba da tafiya zuwa wani sashe na daban wanda batasan dashi ba cikin gidan,idanu ta ware tana kallon ko ina,bai saki hannunta ba sai da suka dangana da wani bedroom wanda yafi kyau a kirashi da aljannar duniya,idanunta basu taba tozalin ganin dakin bacci mai kyau da aka qawatashi ba irin haka
“Barkanki da dawowa gidanki” ya fada yana shigewa toilet dake cikin dakin,tilas bayan ta gama kalle kallenta ta aje kwandon daura da ita ta samu waje ta zauna kan wata kujera dake can nahiya guda ta dakin saboda yalwar da dakin yake dashi.

Bai jima ba ya fito daure da alwala,tana lura da komai yake yana yine cikin juriya,wani saqo dake cikin dakim shimfide da abun sallah ya shiga ya tada sallah da alama shafa’i da wuturi xaiyi,don tuni sunyi magariba da isha’i a gida.

Ya jima saman abun sallar yana addu’a sannan ya shafa,ya taso cikin nutsuwa zuwa inda take zaune,gefan gadon ya samu ya zauna yana fuskantarta idanunshi akanta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button