Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 11

Sponsored Links

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

11
Rayuwa a Mansion din ASH TALBA tamkar rayuwa ne a wata aljannar duniya Amma Kuma ga AmatulMaleek ba Hakan bane sbd halinda mahaifiyarta yake ciki ya danne duk Wani farin cikin datake samu a gidan,
A tsawon shekarun da suka share a gidan kowa yasamu ci gaba ya sauya daga sanin da Akai masa,sauyi kuma me girman gaske Amma Banda maamah wadda ta koma tsohuwar qarfi da yaji ga ciwon kirji Dana jiki Dana qafafu da Baya Wanda kowanne dare Bata iya bacci me dadi,
Ita kadaice tasan halinda mahaifiyarta ke shiga kowanne dare,
Maamah a Koda yaushe boye mata gajiyawarta da ciwonta takeyi sbd kada ta sani ta nuna damuwarta Dan haka maamah din ta zabi ta ringa hadiye damuwarta da ciwon dayake cinta sbd ganin AmatulMaleek na ajiye kowacce damuwarta a ranta kada Hakan ya taba rayuwarta da karatunta Amma Kuma abinda Bata saniba shine hakan ya Riga ya zaunu a zuciyar Amatun ta yanda take musu kallan Yan cin alfarma da jiran komai akashe abasu kaman yanda Husnah ke fada mata tin suna Yara.

Related Articles

Su ‘yayan me aikin gidan ASH TALBA ne Kuma bazasu taba tashi daga Hakan ba shine kalmomin da mum Aisha akoda yaushe take fadawa maamah a gabansu tin suna Yara haryanxu dasuka girma Hakan Bai taba canzawaba.

Ko mum Aisha da Husnah basa yawan tinatar dasu su din da matsayinsu Hakan a bayyane yake ba buqatan tini sbd haryanxu data zama budurwa Abdul yafara zama Dan saurayi a daki Daya suke su da mahaifiyarsu anan suke rayuwarsu.,
Jimawa sukeyii baa dinka musu sabuwar sutirar rayuwa ba kayanda su Husnah suka cire su ake Basu,
Basa shiga sashen madame Abeeda Sai Idan aikine ya kaisu Wanda tinda ta girma take kamawa mahaifiyar aikin gidan,
Har gobe abincin dasuke ci da Wanda mutanen gidan sukeci akwai bambamci,
Dan wannan matsayin dasuke Basai an tinanar dasu matsayinsu ba a cikin ASH TALBAs Mansion.

Abdul ma duk da kasancewarsa namiji har cikin ransa Yana tausayin mahaifiyarsu da wahalar datake sha Amma Shima kusan Amatun ne su dauko halin maamah na danne abu a zuciya tareda nuna ba komai bane Amma kusan Shima Yana taimaka mata da wasu ayyukan duk Yana gida kamarsu aikin kitchen Dan dole daga shi har Amatu sun iya aikin girki sbd taimakawa maamah.

Duk tsawon shekarun da sukai a gidan Babu abinda ya taba kaisu bangaren Mai gidan wato daddynsu Husnah sbd sam baa zuwa gurin hakama duk ganinda sukai masa daga nesa ne tinda ba mazauni bane sosai hakama Koda Hange Babu abinda ya hada bangaren masu aikin gidan da bangarensa bare su samu kusanci dashi.

Husnah anan Abuja take karatunta Dan haka wayewarta ta yayan masu kudin qasa suke bayyane gata batada hakuri ko saukin kai ‘yar Kai tsaye ce Bata iya boye zance ko maganar Dake ranta ba shiyasa da dama ake mata daukan me wuyar shaani,
Kusan Tako wanne bangare halayenta Dana AmatulMaleek sunyi hannun Riga Dan ita kanta Husnah duk yanda taso ganin bacin ran Amatu ko fushinta Bata taba iya Gani.

Shaquwan AmatulMaleek da Haydar wata irin kaunace a tsakaninsu me girma Dan kuwa jinta yakeyi a ransa fiyema da Husnah hakama itama Amatu a cikin familyn TALBAs gaba Daya Haydar shine Wanda tafi so fiyeda kowa da komai na gidan bayan Maamah da Abdul Dan ma kusan yanda take Jin Abdul haka take jinsa a ranta.

 

*******
Ayau gidan ASH TALBA sun tashi da sabon tashin hankalin dawowan ciwon Madame abeeda wadda haka kawai aka wayi gari ta sake shiga mummunan halin data taba shiga kwanaki.

Babbar rashin sa’ar da akaci shine ASH Baya Nan Dan haka su mum Aisha suka kira ambulance akazo aka dauketa hankalin gaba Daya jamaar gidan a tashe aka tafi da ita.

Bayan antafi da ita asibiti lokacin dukansu suna makaranta Dan haka maamah da mum Aisha ne dole a asibitin.

Wayar ASH da mum Aisha keta kokarin kira Bata samu ta sake Saka Kiran Amma dai still Bata samu Dan haka suka zauna jiran tsammani.

Har yamma suna asibiti Kuma har lokacin baa samun wayar ASH Dan haka likitocin basuda zabi bayan sanarwa mum Aisha Cancer ce da Madame abeeda Kuma takusa kaiwa last stage.

Shiru mum Aisha tayi idanuwanta akan likitan Daya gama bayanin cikin Hausa da turanci sbd bahaushe ne.

Maamah kuwa dafawa tayi Takoma zaunen data miqe sbd nauyin da qafafunta sukai mata suna Gaza daukanta.

Shiru sukai dukkaninsu Babu Wanda yake motsi sbd tinanin dasukai Nisa a cikinsa na ba zata da tashin hankali musamman maamah da hannuwanta duka dauki rawa ahankali
Ta damqesu sbd rawar da sukeyi zai iya haifar da matsala babba gareta musamman ciwonta datakeji zuciyarta na Neman Dena bugawa.

Cancer” mum Aisha ta furta ahankali tana Dan share guminta Dan duk abinta tana tsoron mutuwa haka Kuma duk lokacinda aka ambaci Cancer ga mutum Babu abinda suke fara hangowa akansa sai mutuwa a kusa kusa.

“Innalillahi wainna ilaihirrajiun” maamah ta fada ahankali tana rintse idanuwanta dasukai nauyi suna son hawaye Amma sunma kasa haduwan.

Mum Aisha a gurin ta ciro wayarta Babu Wanda ta fara kira sai ‘danta da kusan Babu abinda suke boyewa juna,kaf duniyarta shi kadaine Wanda takeso tsakaninda Allah da gaskia Dan haka ta tsaya akan karatunsa Dan yayi arzikin Daya kusa na ASH TALBA idanma har bazai fisa ba kenan.

Ringing wayar tasa takeyi harta katsae Bai daga ba Saida ta sake kira karo na biyu jikinta na rawa ta isar masa da zancen sbd damarsu tazo ta dawowansa gida ya baro turai sbd tabbas hankalim ASH TALBA zai tashi daga dukiyarsa da harkokinsa ya dawo Kan Abeeda sbd mahimmancinta da matsayinta yafi na komai daya mallaka so yanzu ne NAUFAL dinta zai samu matsayi da Daman shiga cikin huldodi da dukiyar ASH EMPIRE.

****
Madrid,SPAIN.

kwance yake akan lafiyayyan gadon dakinsa acikin gidansa da babu abinda ya rasa na Jin dadin rayuwa da Hutu,
Dagashi sai Men’s tight Wanda baida bambamci da Babu komai a jikin nasa sbd kusan daga saman ya zame kadan hakama ya kamasa sosai ta yanda kana ganin shape na komai nasa.,

Fatar jikinsa Dake shining na qyallin Hutu da kyan fatar duk a Bude Dan bayan tight din baida komai a jikinsa,
Gefensa wata lafiyayyar blown skin mace ce da itama Babu komai a jikinta sai pant da bra wadda itama kusan a zame take,
Bacci sukeyi hankali kwance Wanda ke nuni da idanma da daddare idanma da safen to sungama mu’amalar mace da namiji ne kafin baccin.

Ringing wayarsa keyi duk da tana silent Amma vibration din na tashi sosai harya fara jinsa cikin baccinsa Dan haka ya Dan motsa Yana Bude idanuwansa ahankali daidai lokacinda Wani Kiran ya sake shigowa.

Akan fuskar sabuwar budurwarsa Dake kan jikinsa idanuwansa suka sauka ya Dan yamutsa fuska ahankali tareda janyeta daga jikin nasa Yana miqa hannu inda wayarsa take daidai kira na uku na sake shigowa.

Qaramin numfashi da tsoki ya Dan sake lokaci Daya kafin ya duba Mai Kiran yaga sunan Mum dinsa baro baro.

Ajiyar zuciya ya sauke me sanyi tareda tashi zaune Yana zamowa bakin gado ya sauko da qafafunsa qasa ya miqe daga gadon Yana daukan wayar Kai tsaye tareda dorawa kunnensa ya nufi hanyar fita dakin Yana cewa

“Yes mum,good morning”

Kallan time mum Aisha din tafara yi gana su anan din ba safiya bane Amma dai koma yayane bashine matsalarta ba cikin kulawa da ‘yar kamewa tace

“Morning,ka tashi lfy?
Ya karatun??

Ruwan dumi Daya zuba a cup ya jefa lemon aciki ya Kai bakinsa Saida yasha sosai kafin ya amsa da cewa

“All good mum,
Yaya Su Husnah and Aunt Abeeda?

“Husnah lfy kalau Aunt din taka ce dai take kwance asibiti batasan inda kanta yake ba.”

Shiru yayi Yana ajiye cup din hannunsa ya nufi Daya daga tsadaddun kujerun palonsa ya zauna Yana cewa

“Meya sameta mum?
Wani abu ya faru ne?
Meyake faruwa?

Katsesa tayi da cewa

“Cancer ne da ita duk tsawon lokacin Nan Amma ba Wanda yasani sai yanzu..

Katsesa Naufal din yayi cikin mamaki da cewa

“Uncle ASH fa? Ya sani?

“Bansaniba ko ya sani Amma dai yanzu besan muna asibiti da ita ba bana samun wayoyinsa duka,
And duka bayan wannan ka saurare ni da kyau kaji……

“Heyy baby good morning” …shine abinda mum Aisha taji daga cikin wayar tayi shiru zuciyarta na yin nauyi sbd bata buqatan kowanne irin bayani ta sani mace ce a tareda Naufal din a cikin irin matan dayake kawowa gidansa suna kwana,

Babban baqin cikin mum Aisha a duniya biyu ne zuwa uku,
Na farko dukiyar ASH TALBA data tsone idanuwanta ta Hana zuciyarta sukunu tsawon shekarun datake zaune a gidansa cikin dukiyar tana yanda takeso da ita hakama ‘danta yake yanda yakeso da rayuwarsa tamkar shine magajin ASH TALBA din,

Na biyu shine Neman matan da Naufal yekeyi kamar bunsuru Sam Baya iya kwana a rayuwarsa batareda ya kusanci mace ba
Duk ranarda ya kwana biyu batareda mace a tareda shi ba to kamar zai zauce yake jinsa shiyasa gaba Daya Baya iya zama Nigeria sbd Jin Yana aikata irin wannan zinar haka kaman abinci zai iya Saka ASH TALBA nesantasa da ko inda zaibi ya wuce bare Kuma sakashi cikin dukiyarsa dasuke fata tin shekara da shekaru Shida mum dinsa.

Abu na uku kuwa shine Haka kawai takejin tsana da rashin Jin nutsuwar zaman maamah da ‘yayanta a cikinsu sbd maamah din tamkar kariya ce ga Abeeda data Dade tana Jin qyashinta da kishinta ga Dan uwanta dayaqi qara ko kallan wata macen bare Wani tinanin qarin aure da babusa a tinaninsa ko rayuwarsa ma gaba Daya.,
Zuwan maamah yasaka duk yanda Husnah take renanta Kuma tarbiyarta harma da yanda takeson ta zama sbd amfani da ita gurin ASH sosai ya ruguje sbd komai rashin saukin kan Husnah da zafin kanta tana kaunar maamah da gaskia Kuma kamar yanda maamah din ke tsananin sonta kaman AmatulMaleek da Abdul, Husnah Takoma kusancinta da maamah da shaquwarta da ita yafi na kowa Dan haka Sam yanzu sedai ayiwa maamah duk abinda zaa mata na cin zatafi ko aikin wahala Amma baa iya canza matsayinta gurin Husnah da zuciyarta.
Wanna dalilin ne yasaka taji tayiwa shigowarsu Maamah rayuwarsu tsana me karfi.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button