Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 20

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

Related Articles

20
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

************
Asibiti take sukai filing matsalan Amatu akan rape gashi ba qaramin duka da azabtawa Tasha a hannun Wanda yaso raping din nata ba da kuwa fuskarta da jikinta koina shatin hannuwansa ne na Mari da naushi ga tashin hankali matsananci da tsoro sosai me hade da firgici Daya daketa sosai shiya qara tsananta yanayinta ta fice hayyacinta gaba Daya batasan waye yake kantaba.

Haydar da idanuwansa sukai jajir qurawa kofar dakin datake idanuwa yayi Yana Jin zuciyarsa bayan ci da wuta Babu abinda takeyi,
Abdulhameed Daman tinda suka zo asibin Bai iya qara dogon motsi ba zaune yake shiru idanuwansa jajir suna jiran tsakanin maamah da Amatun waye zai fara farkawa Dan kuwa idan har ansamu nasarar lalata rayuwar Amatu to zamansu TALBAs ya qare har abada sbd zuciya zata iya Kaisa ga aikata abinda zai janyo babbar matsalar da zata iya fin wannan.

Faisal ma kusan tasa zuciyar me rauni kasa dauka yayi Saida yafara tsiyayar hawayen baqin ciki idan har abinda suke Gani ya tabbata din Wani ya lalata masa rayuwar Amatunsa.

Mum Aysha kaida kawo takeyi zuciyarta itama kusan tafi ta kowa shiga tsalle da tsinkewa,
Batasan tayaya zata rufe Naufal daga wannan maganar Dan kuwa ana sanin shine yayi wannan aikin yagama yawo a gurin ASH hakama ga maamah na Neman rasa nata ran sanadin Hakan.

Tamkar zaman makokinda baa samu gawar ba sukeyi a kofar dakin emergency din asibitin Babu Wanda hannuwansa basa rawa da zuciyarsa hakama Yan mazan uku kowannensu idanuwansa tamkar an zuba masa borkono sbd jajir din dasukai.

Har Akai Kiran sallan asuba Babu Wani zance Saida sukaje sukai sallah suka dawo likita ya fito ya sanar musu Amatu anyi dressing raunikan Dake jikinta da fuskarta sedai sakamakon anyi mata fyaden ko baayi ba sai anjima idan babban lokitansu ya fito zai sanar musu,
Maamah kuwa jininta ne yayi mummunan Hawa tareda bugawan zuciya Wanda suke fatan idan zata farfado ta farko lafiya batareda matsalar dasuke gudu ba ta shanyewan jiki ba.

Wanna bayanin na likita ya Saka dukkaninsu shiga sabon tashin hankali da radadin zuciya Mai tsananin gaske Dan kuwa a matse suke kowannensu da Jin ko kaddadar ta faru ne da Amatun ko kuwa?

Haydar ne yafara juyowa ya Kalli mum data yi nesa dasu tana waya a hankali tana fadawa Naufal yafara Shirin barin gari sai komai ya lafa.

Daga Haydar har Abdul da Faisal Babu Wanda ba Naufal dinne a zuciyarsa ba Dan haka kowa da abinda zuciyarsa ke Saka masa.

Faisal ne yafara juyawa ya fice daga gurin yana Isa motarsa ya fada Bai tsaya komaiba ya tada motar yabar asibitin cikin mugun speed ko Gani sosai bayayi Allah ne kadai ke taredashi.

Haydar ma juyawa yayi zai fice Abdul ya rigasa juyawa ya fice Dan haka kusan tare suka fito a karo na farko rayuwarsu da suka hau motar haya.

A tare suka furta ASH TALBAs..

Babu me magana a cikinsu hakama Babu Wanda hannuwansa da zuciyarsa Bata rawa har suka Isa gidan.

Securities ne suka biya me motar su kuwa Kai tsaye ciki sukai Babu me Rahama ko sauki a fuskarsa.

Kai tsaye sashen masu aiki suka nufa suna Isa Abdul ne yafara cin karo da Farida tana ganinsa tayi Baya da sauri Bai tsaya komaiba ya shaqota cikin rawar da jikinsa keyi yanason tambayarta waye ya shigarwa Amatu Amma zuciyarsa ta rufe sai hawaye kawai matsu tsananin zafi suka gangaro masa jikinsa ma sake daukan rawa,
Haydar ne ya jefa mata tambayar Shima nasa Idanuwan na sake hada hawaye masu tsananin zafi.

Yanda jikinsu ke rawa da tsananin baqin ciki mara misali yasa Farida data shiga tashin hankali da tsoro ambatar sunan Naufal Wanda ya fito daga sashensa janye da qaramar luggage da jakar laptop dinsa da wata jakar zai nufi harabar gidan.

Haydar ne ya juya da sauri yabi bayansa daidai ya Isa bakin motarsa zai Bude motar Faisal na shigowa harabar gidan da Wani irin gudu.

Saurin Kai hannunsa Naufal yayi kan motarsa zai Bude daga bayansa yaji tahowa Yana juyowa Bai gama tantance waye ba yaji daukan Wani mummunan naushin Daya Sakasa yin baya ya fada jikin motarsa,

Haydar ne Wanda yafara Kai masa wannan naushin idanuwansa na rufewa sbd gaba Daya baa Dan uwansa Kuma yayansa yake kallansa a lokacin ba se rapist Wanda ya illata masa rayuwar macen dayake tsananin so rayuwarsa.

Abdulhameed na isowa a tare dashi da Faisal suka Sakar musu nasu naushin dasuka Saka bakinsa da hancinsa fashewa da jini a tare.

Acikinsu Babu Wanda idanuwansa Basu rufe ba da zuciyarsa da tsananin tiririn bacin Rai da zafin zuciya.

Husnah data Dan ji sauki ta fito cikin tsoro Jin hayaniya da ihun masu aiki na tashi
Hakama securities tini suka yo harabar gidan ganin abinda yake faruwa Dan kuwa duka ne su ukun sukewa Naufal kaman zasu rabasa da ransa duk da basuyi girma da shekarunsa ba Amma Suma karfinsu na samartaka ya Riga yazo gasu suna geamin a dakin geamin na Mai gidan Wanda Babu kalar kayan geamin da Babu a makeken geamin room din.

Shi kuwa Faisal ma kusan yafi Naufal din karfi Dan Shima sosai yake exercise na Bude jiki sh kuwa Naufal Neman mata da Hutu kawai yasani baisan ya motsa jikina bare building jikin nasa.

Kowannensu zuciyarsa tafasa takeyi me tsananin gaske Dan haka kusan basaji basa Gani.

Shigowar motar mum Aisha gidan Taga abinda yake faruwa ko parking batai ba ta kashe motar ta fito tana qarasawa da wuri tana cewa securities su futar da Faisal da Abdul a gidan tinda ba gidan ubansu bane zasu kashe make a ‘da ana kallo.

Dole securities suka ja Faisal da Abdul da sai alokacin yake fashewa da kukan baqin Daya danne zuciyarsa tin tsakar Daren.

Securities ne suka fito da motar Faisal daga mansion din ya shiga tareda Abdul Dake kuka sosai suka bar anguwar kowa zuciyarsa na fadawa da rage baqin cikin dasukai.

Haydar kuwa Husnah ce ta qanqamesa tana fashewa da kuka cikin tsoron ganin yanda jikinsa ke rawa dakuma ganin tashin hankalin da Bata taba Gani ba ga shiga mummunan tsoron Jin abinda akaiwa Amatu a cikin gidan.

Mum kwasar Danta tayi jiki na rawa itama Tayo asibiti dashi Dan kuwa ba qaramar sa’arsa suka samu ba sun dakesa sosai ga illar da Amatun tai masa cikin dare.

Haydar ciki Husnah tai dashi har lokacin kuka takeyi sosai tana sake qanqamesa sbd Bata taba ganin fushinsa haka ba,jikinsa koina rawa yakeyi.

Isarsu mum Aisha asibiti Shima kusan Naufal din qin amsarsa Akai dataga Yana Neman mutuwa a banza dole ta sanar musu shine Wanda yayiwa Amatu abinda Akai mata hakama su Barr Faisal ne sukai masa wannan dukan Da wannan suka amshesa tafara kaida kawo cikin masifa da balai biyu da biyu.

Bata taba ganin baqar Rana irin wannan ba Dan kuwa ASH kawai take tinowa da zancen kowane lokaci zai isar masa Menene zai biyo Baya shine babban tashin hankalinta da masifarta.

Abdulhameed Faisal turaki gidansa ya Kaisa yayi jarimta da karfin halin danne nasa damuwa da dacin ran ya rarrashesa tareda basa qwarin gwiwan inshallah Babu abinda ma yafaru har tsawon lokaci suka samu zuciyoyinsu suka sauka kafin suka koma asibiti.

Koda suka Isa Husnah ta iso asibitin tareda Haydar hankalinta tashe Jin halinda maamah take ciki harma da tausayin Amatun.

Kallon tsanan da takaici harma da damuwa mum Aisha tayiwa Faisal turaki da Abdul din dasuka iso kofar dakin emergency da kusan duka su uku dakunansu na ciki Kuma baa buqatan kowa ya shiga.

Suma babu Wanda yace komai sai Husnah data Kalli Faisal cikin sanyi da kulawa tana tambayarsa idan Yana lafiya bayan tashin hankalin.
Gyada mata Kai kawai yayi Yana Dan kallanta cikin nutsuwa.

Abdul ta Maida kallanta akansa Shima kasa magana tai da idanuwa kawai ta masa alaman komai zai daidaita inshallah.

Wuni guda suke Neman yi a asibitin Babu Wanda aka samu kansa a su ukun Dan haka hankalinsu yafara tashi musamman akan maamah da AmatulMaleek.,

Basu sake shiga tashin hankali ba Saida yan jarida suka zagaye asibitin take aka juya labarin cewan

“Anyiwa ‘yar me aikin gidan ASH TALBA Dan takarar governor fyade tareda attempting na kasheta sbd zancen kada ya fita,hakama ana zargin ‘dansa na cikinsa da ‘dan yar uwarsa hakama uwar yarinyar ma na kwance Rai a hannun Allah.”

Wannan mummunan labarin ne ya girgiza gaba Daya jamaar gidan da duk Wani masoyin ASH TALBA ta bangaren siyasa harma da dangi sbd take aka girmamam abin cikin mummunan sigar danganta lamarin harda kisa.

ASH Baya qasar wannan mummunan labarin Mai Muni da girgiza zuciya ya samesa Dan haka take ya shirya dawowa Dan kuwa babbar masifa ta sauka a familynsa kenan.

Su kansu ‘yayansa dake asibitin Dole jamian tsaro sukazo aka zagaye asibitin sbd komai zai iya faruwa Dan kuwa mutane sosai suke Neman tada fitinar datafi karfinsu.

Husnah tsoro da tashin hankali ta shiga kamar yanda mum Aisha ta shiga nata tashin hankalin Mai tsananin gaske Dan haka ta fara shirye shiryen hadawa Naufal tafiya ya gudu kafin ASH Yadawo Idan komai ya lafa ya dawo Dan kuwa tasan wannan guguwar zaiyi wuya Bata Bata siyasar ASH ba da Daman bawai sonta yakeyiba gashi akan Hakan maganganun masu zafi da cin zarafi ke fitowa Tako Ina.

Abdulhameed ma tashi hankalinsa yayi tareda baqin cikin fitar zancen sbd duniya taji fyade akaiwa Amatu bayan likitan ya tabbatar musu da Bai samu damar yi mata fyaden ba.

Gaba Daya jin yayi garin da rayuwa acikin TALBAs din ta fita ransa
Rayuwar mutunci kawai yake yiwa yar uwarsa fata Dan wannan mummunan tabo ne Daya Riga ya taba rayuwarta.

Naufal ne yafara farfadowa cikin dare Kuma dayake anyi dressing raunikansa tareda allurai da ruwa na rage radadin da tsamin jiki
Da Dan damarsa ya tashi.

Mum na ganin Hakan Batai sanyaba a cikin Daren ta tserar dashi daga asibitin zayyan Mande Dake jiransu ya daukesa da motarsa suka bar garin Dan Shima yasan koma Menene Naufal ya aikata ranar akwai sunansa aciki tinda shine ya basa qwayar Daya sha din me qarfi.
##MAMUH#

 

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button