Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 13

Sponsored Links

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

13
YAR UWATA TSAYA KIJI KAYANDA SISTER NA KE SAYARWA BAZAKI RASA ABUNDA KIKESO BA A CIKI IN SHA ALLAH 🙏💪

Related Articles

Sis Kinason siyen maganin Kara girman hips da breast kodai rama ce damuwarki❓kinaso kiyi kiba ki ciko kiyi kyau KO KUMA KAYAN GHT KIKESON KISIYA Na gyaran skin fatarki tayi kyau❓ko maganin infection ❓asthma ❓ ulcer ❓ rashin haihuwa ❓ hepatitis ❓ diabetes ❓ ko Kuma kiba ce da tumbi suke damunki❓ to tanada magani da yardar Allah ❓ga group link din sister na🥰 kiyi joining 👆👆👆👆Zaki samu fiyeda yanda kikeso Kuma kayanta nada sauki ga kyau tested and trusted 👍💪

Idan bakyason shiga group kiyi saving number dinta👉 https://wa.me/+2349038090328 👈kimata magana kice kinyi saving itama zatayi saving taki🥰 zaki godemin na hadaki daita danayi in Sha Allah 🤗

 

*************
Ganin AmatulMaleek da Abdul na gurin yasaka Babu Wanda yayi magana a cikinsu kowa shiru yayi jiki a mace sbd tafiya ce da Kila batasan ranar dawowanta ba.

Amatu data lura da dukkaninsu jikinsu yayi sanyi Kuma Babu me magana acikinsu kowa yayi Nisa a tinanin,
Ajiyan zuciya ta saki a boye kafin ta miqe tsaye tana kallan Abdul Dake amfani da wayar Haydar tace masa su tafi waje su Jira su Haydar su dawo su wuce gida.

Miqewa yayi a tare sukaiwa mommy Abeedan adduar samun sauki suka kalli mahaifiyarsu sukai mata sai anjima suka fita maamah na bin bayansu da kallo cikeda tausayinsu sbd tasan zuciyarsu na cikin radadi da Jin ciwon wahala da bautan datakeyi Amma Kuma abinda Basu saniba shine duk wannan sadaukarwa ba iya Abeeda bane kawai sbd sune,sbd su samu ingantaccen ilimi da rayuwa me kyau ne Abisa ga sharadin mum Aisha data shimfida mata sharadin idan ‘yayanta zasu samu ilimi me kyau ita zata maye aikinta da iliminsu.

Numfashi Amatu data fita ta sauke kaman yanda Suma bayan fitarsu Amatun maamah ta Dan sauke numfashi me sanyi a boye.

Su Amatu suna saukowa qasa cikin saa lokacin ASH TALBA yabar asibitin Husnah tabisa Dan haka Haydar kawai suka samu zai hawo saman Dan haka suka Jira yaje yayi bankwana da mahaifiyarsa ya sauko suka tafi gida.

Tsawon lokaci da tafiyar kowa har dare yayi maamah tayi maga komai na Shirin bacci ta kwanta Amma bacci ya kasa zuwa idanuwanta Dake cikeda yanayi na ciwo na irin Wanda yake Jin jiki,

Tanason magana Amma Sam Bata iyawa Dan kuwa zuciyarta tariga tayi Wani irin sanyi da saddaqarwa akan rabuwarta da ‘yayanta tazo,

Wasu hawayene masu tsananin zafi suka gangaro daga cikin idanuwanta dasukai fari fes irin na ciwo.

Saukowar hawayenta akan idanuwan maamah suka sauko Dan haka tayi shiru batareda tace komai ba sbd duk abinda ya Saka Abeeda kuka yakai qololuwar raunana zuciyarta.

Tin hawayen na gangarowa cikin rashin sauti har kuka me sanyi da radadin zuciya ya kufce mata ta rintse idanuwanta tana yin sa sosai har lokacin Bata iya Bude bakinta ba.

Wani irin sanyi da mutuwa jikin Maamah yayi itama nata idanuwan suka ciko da hawaye sosai sbd Babu kalman da zata iya fadawa Abeeda yanxu ta sanyaya mata abinda take ji din.

Shiru dakin ya dauka bayan kukan madame Abeeda Babu abinda yake tashi cikin tsananin qunci da damuwar da tasan Allah ne kawai yasan Yaya rayuwa zatai da ita kodai ta dawo ga yayanta a Raye kokuwa a dawo musu da gawarta.

Duk yanda maamah taso daurewa kasawa tayi sbd maraicinsu dasuka taso aciki kowannensu batareda iyayensa ba dakuma yanda rayuwa tayi da kowannensu shine ya dawo musu zuciyarsu ta karye itama tafara gangaro da hawayen tana rufe fuskarta da mayafin Dake jikinta sbd yanda kukanta ya qara ingizowa da yanda ta rasa kowa nata daga iyayen har mijinta Abeeda kawai ta rage Mata itama gasu a Wani hali na fargaba da tsoron me zai iya faruwa sbd ciwonta.

Ita Abeeda kukanta me tsanani dayake sake karya zuciyar maamah na yanda zata bar yayanta duk da tasan suna cikin gata gaba da Baya Amma rabuwa da yayanta da mijinta ASH Wanda take Jin zuciyarta kawai Neman bugawa takeyi idan ta Tina tana tafiya shikenan zai iya shiga Wani hali na damuwar da zai iya nesanta kansa da kowa harma ‘yayansa Dan kuwa ayanzu ta tabbatarda soyayyarta data Dade tanason tabbatarwa a zuciyarsa.

Haka suka kwana Babu me dadin zuciya sai tinanin da kowa ya zurfafa aciki qarshe Hakan ya tayarwa madame Abeeda Wani ciwon Amma ta daure sbd tanason kwanakin da zasuyi kafin tafiyar tayi su tareda yaranta cikin kauna da kulawa.

Ita kanta maamah daurewa tayi sbd damuwa na Neman tayar mata da nata ciwon zuciyar Amma batason kwantawa sai take dannewa da daurewa.

Washe gari qarfin halin da Abeeda ta nuna yasa aka sallamesu
Ko wannan Karan ASH da kansa ya dauketa ya tafi gida da ita.

Babu Wanda ya samu ganinta sai washe gari ta dawo bangarenta anan duk suka zo sukai mata sannu ‘yayanta kuwa suna tareda ita,
Ko baqin dataita yi mutanenta masu zuwa dubiya matan manya basa Wani jimawa suke tafiya sbd an Hana abarta ta gaji sosai.

Tinda ta dawo kulawan da akeyi da ita ta ninku sbd wannan Karan duk Wanda ya kalleta yasan ciwo ne a tareda ita sosai Dan gaba Daya Takoma fara tafara sauya kamanni hakama ko magana tayi sosai saita gaji Dan haka ko magana baa son ta cika yi.

Daga yayanta har masu aikin gidan a yanzu kowa jikinsa a sanyaye yake Babu me doguwar walwala a gidan kaf Dan kuwa me gidan kansa Baya cikin walwala da dadin zuciya ko kadan sbd halinda matarsa take ciki.

Husnah data tabbatarda ciwon mahaifiyarta akwai yiyuwar takewa akwai yiyuwar tafiyarta tabarsu yasa take depression yafara kamata sbd ko karatu ta dena ganewa,
Gashi kowacce safiya suka tashi jikin mum din nata ba sauki gaba abin yake sake yi,
A Koda yaushe mum din yanzu magarsu nasiha ce gareta,
Haydar ma dayake namiji depression din kamasa yayi.

Gidan ASH TALBA tini ya tashi daga gidan farin ciki sbd zuwa yanzu Madame abeeda tayi Nisa gashi tafiyar da zaayi da ita Bata kammaluba
Gashi ita kanta Abeedan ta shiga mummunan damuwa da Saka abin a ranta Dan haka sai hawan jini me tsananin gaske ya shigo ciki da ciwon zuciya Dan haka jikin ya kasa dauka.

Maamah datake Jin danginta daya data rage Mata zata barta kusan ASH da ‘yayan Abeedan ne kawai suka fita shiga damuwa Amma itama tini jikinta yake Neman rikicewa sbd damuwa Amma su Amatu nata kokarin kulawa da ita sbd ita idan ta kwanta basuda me kulawa dasu Dan haka suke lallabata duk da Suma suna cikin damuwa da kukan halinda madame Abeeda take ciki.

Madame abeeda takai matakin da ko magana Bata iyayi Amma ko acikin hali na tsananin ciwo maamah take sake bawa amanar ‘yayanta sbd kaf duniyarta tasan bayan dad dinsu Babu Wanda zai kaunacesu ya kula dasu fiyeda nasa yayan sai maamah Dan haka Babu abinda take iya daure ta furta sai amanar yayanta ga Asmau wadda itama cikin kuka sosai koyaushe take tabbatarwa da Abeeda zata kula dasu Husnah da Haydar kamar itace ta dauki cikinsu ta haifesu wannan alqawarine datai mata zata kula dasu har inda nata karfin da rayuwar ta qare.

Ciwon Madame Abeeda Wata babbar jarabawa da kaddarar familyn ASH TALBA ne Dan kuwa tini labari ya yadu sbd tayi Nisan da kusan duk sun fidda Rai,
Kuka da tashin hankali irin Wanda familyn suka shiga baa magana Dan kuwa shi kansa ASH din isolating kansa yayi sbd sai yanzu ne zuciyarsa take sake tabbatar masa da tsananin so da girman Abeeda a zuciyarsa hakama yanda yayansa abun ya tabasu musamman Husnah da tini kanta yake Neman tabuwa da lamarin da Basu tana sanin meye rashi na dukiya ba bare na Rai tinda Basu taba rasa Wanda yake shaqiqinsu da wayonsuba.

Husnah batasan cewa idan mum din tasu ta rasu ba ita shikenan batada uwa batada Uba da Kila abin saiyafi haukatar da ita,
Haydar Amatu sosai ta tsayu akansa tana kulawa dashi ta hanyar rage masa damuwa itada Abdul Wanda Shima harda Husnah Yana kulawa da ita hakama ta bangare daya maamah Kam ciwo ya kwantar da ita Amma ahakan take daurewa,

Mum Aisha tashiga damuwa Amma ta rashin dawowan Naufal a daidai lokacinda yakamata ace familyn gidan duk suna Nan tareda ASH wadda duniya ma ta tabbatarda yanda yake tsananin son matarsa Madame Abeeda Talba.

A lokacinda tafiya da Madame Abeeda yayi ta kwana biyu da fita hayyacinta Dan haka kamar gawa aka gama komai aka tafi da ita tareda mum Aisha da yayanta suka tafi.

Bayan tafiyarsu kusan gidan kwana biyu Akai ana zaman da zaa iya cewa kaman na makoki,
Maamah da abin ya Dan tabata dole su Amatu suka dage gurin kulawa da ita sai ya zamana kusan ragamar gidan ta dawo hannunta tinda a hannun maamah take khaltume yanzu ta dawo karkashin maamah Dan haka yanzu da maamah din batada lafiya sai komai ya dawo hannun Amatu.

 

*****Bayan kwanaki da tafiyar mutan gidan da addua da dagewa da kulawa suka samu maamah tafara samun sauki tana warwarewa yanda ya kamata.

Ganin karatun yaranta na Neman tabuwa yasa maamah din Saka qarfin hali tana warkewa Dan kada ta daqusar da yayanta.
Cikin wasu kwanakin ta warware gaba Daya ta koma ayyukan gidan da kulawa da Gidan Dan kusan kowa gidan a qarqashinta yake yanzu itace aka barwa amanar gidan da kulawa dashi sbd shi kansa ASH TALBA ita yabarwa kula da kowa na gidan.

AmatulMaleek kuwa tini Takoma bakin karatunta Daman tana zuwa ne tana skipping wasu kwanakin sbd jikin Maamah Dan haka yanzu da maamah ta warke saita dage tinda gamawa zasuyi watanni kadan masu zuwa.

****Sati hudu su Husnah sukai suka dawo gaba dayansu jiki a sanyaye batareda mahaifiyarsu ba wadda komai ya tsaya a duniyarta dama tasu duniyar Dan kuwa jiki dai ankai inda baason Akai,
Ana Saka ran paralyze ya shiga ciki Amma baa tabbatar ba sbd gaba Daya tayi slipping into coma Dan haka baa San ranarda zata Farka ba,hakama akwai yiyuwar daga coma din bazata tashiba shikenan ta tafiyarta Dan haka a cikin mummunan tashin hankali sukai kwanakin da sukai suka tattaro gaba dayansu suka dawo Dan qanwar mahaifinta Dake Greece din da zama zata kula da ita duk da asibitin Wani Baya zama sune suke kulawa da komai monthly ake zuwa duba patient sosai suke kulawa dasu tinda kudi masu yawan gaske ake zubewa gasu da qwararrin likitoci.

Bayan dawowansu ASH TALBA Babu Wanda ya sake ganinsa Sam Babu ma Wanda yasan yana qasar ya sanar da Personal person dinsa Jameel Baya buqatan ganin kowa da kowannen irin aiki sai bayan kwana biyu Dan haka Jameel ya sanar da securities na gidan kwata kwata ma baqi yanzu idan ba family ba kar Abar kowa yashiga mansion din.

Mum Aysha kuwa Basu fi sati biyu da dawowa ba ta bar qasar zuwa Spain sbd Naufal Dake Neman buga mata zuciya da baqin cikinsa da bacin Rai yaqi dawowa duk kira da massages din datake aika masa Dan haka a yanzu da ASH zaiyi rayuwa ba tareda matarsa ba abu biyu take buri da buqata a wannan bagiren Amma Naufal din da Allah yayi da jinin ubansa data Jin ranta na quna idan tana ganin halinsa yaqi dawowa sbd anan Yana ganin bazai samu mata yanda yakeso ba yana biyan buqatansa,Dan haka gwara taje ta taho dashi da kanta.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button