Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 26

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

26
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

Related Articles

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

***************
Kawu bello gaba Daya Jin yakeyi ya qagara su tashi su fara Shirin fiddo kayansu su fito sbd ASH din yace yau zasu koma Abujan ko yolan bazasu kwana ba.

Maamah kasa dauka zuciyarta tayi da lamarin gaba Daya Dan haka jikinta yafara Neman rikicewa dole su kawu suka harhada sukaita kanta dole akace a kamota a fito dasu itada Amatun su harma da Husnah suka fito tafiya.

A mota Daya aka Saka maamah da Amatun wadda itama har lokacin bat dawo daidaiba dole Abdul motarsu ya shiga sbd suna buqatansa dukkaninsu.

Husnah mota Daya ta shiga da Dad dinta ta lafe gefensa batareda ta iya ko motsi ba bare magana kaman yanda Shima Babu abinda ya furta.

Faisal ma da kusan Shima a cikin shock yake Baya hayyacinsa dole motocinsu ASH aka taho dashi.

Manyan motocin na barin qauyen gaba daya su kawu suka kwabe manyan rigunansu Dan fuskantar junansu akan uban kudin da ASH ya Basu Dan kuwa tsakanin su da yayansu ba sauki kowa ya shirya abasa kasonsa musamman su uzaifa daya Bada kudinsu daban yace abasu suda suka so auren Amatun.

Hatta su megari babbar kyauta yayi musu
Su kuwa su kawu nasu baa magana ga sadakin AmatulMaleek din Yana hannunsu Dan haka kowa ya kasa ya tsare matse suke dasu Amatun su wuce Daman ayi kason kudin.

Tafiya ce akayo shiru Babu Wanda yake magana a duka motocin sai motar securities dinsa dasuketa murna da farin cikin aurensa tareda mamakin wadda ta zamo matar tasa.,
sai Kuma motar iyayen Naufal da kusan Suma dai suna tattauna yanda lamarin ya kasance ne uwa Uba uncle din dayaso Rabonta ya fado kansa yau shima ya dawo yayi kwanan Kwanciyar hankali da samuwar amaryarsa.

A motansu maamah kuwa daga ita har Amatu dai jikinsu ba sauki tafiyar kawai akeyi Dan haka hankalin abdul dayake gaba Yana kansu Akai Akai Yana juyawa ya kallesu.

Tafiya me Dan tsayi sukai zuwa lokacin duhun yamma ya Sako Kai Dan haka Koda suka shigo gari magrib tayi Dan haka Kai tsaye mansion dinsa Dake garin aka nufa su Kuma su uncles din Naufal masauki kawai Akai dasu Dan daman daga Nan zasu rabo zasubi jirginsu daga masaukin su wuce.

Koda suka Isa Daman akwai aiki a gidan Tini komai yake gyare Amatu Abdul ya kamo ya shiga da ita har makeken bedroom din da aka ce akaita kafin yakoma ya shigo da maamah itama Wani bedroom din Daya kusan girman na Amatun.

Husnah da kanta ta shigo sbd Dad din tini yayi bangarensa sbd alwala ya fito sallah.
Dakin maamah ta nufa ta shige sbd batasan zuwa gurin Amatu tafison gurin maamah din.

Abdulhameed ma alwala yayi ya fito sallar kaman yanda Faisal ma yayi alwala duk suka nufi gurin sallan.

AmatulMaleek da kanta ke tsananin juyawa hakanan ta daure tana ganin jiri ta nufi toilet dayake dakin ta fada hannuwan na rawa ta tsaya jikin kofar lafiyayyan toilet din tareda rintse idanuwanta ko zata samu yar hankalinta ya dawo mata ko kadan ne sbd kanta daf yake da juyewa sbd tinanin komai ta kasa Dan Bata ganewa ma.

Daqyar ta Dan ji karfi ta daddafa ta Isa jikin ruwa Tayo alwala ta fito tana dafa Bango daqyar ta iya fito da kanta dakin tana lalabawa ta Isa Dayan dakin dasu maamah suke ta Bude idanuwanta basa Gani sosai.

Sallah Taga maamah na kokarin tayarwa daga zaune sbd bazata iya tashiba kaman ma ba qafafu a jikinta takeji.

Ganin inda suka kalla alqiblah yasata dawowa dakin itama ta tayar da sallarta sedai jiri sosai yake daukanta Amma ta daure sbd akwai har sallar Azahar a kanta.

Cikin dauriya da karfin zuciya tayi sallolin dasuke kanta tayi magrib ta zame a gurin ta kwanta zazzabi me qarfin gaske kawai Yana rufeta hawaye na bin gefen fuskarta masu tsananin zafi da sai yanzu nauyi da toshewan zuciyarta ke fara motsawa.

Abdul ne ya shigo dakin yayo kanta cikin kulawa da tsananin tausayinta ya tayar da ita zaune suka zauna a qasan dukkinsu tareda jingina da gadon dakin Idanuwansa na sauya zuwa ja sbd shi tako Ina damuwa suke sake nitsasa a cikinta ga bangare daya tinanin Haydar a cikin zuciyarsa dama yanda rana tsaka zaace Amatu ta zama matar ASH TALBA,

Ta bangare daya Kuma yasan Babu Wanda wannan auren zaizo masa a sauki sbd maamah hara abada bayajin zata iya karban wannan auren a yanda Bata hada komai da kaunar datakewa madame Abeeda ba yanzu Kuma ace yarta ta cikinta ce ta auri mijin Abeedan.

Kasancewar Abdul a tareda Amatun ya Sakata sakin kukan Daya taso daga qasan zuciyarta gaba Daya cikin sauti mara qarfi da qunci me tsanani.

Hannuwanta ya riqe mata sbd rawar da sukeyi cikin tausayawa Yana Bata hakurin da baima San meyake cewaba Dan Shima Yana cikin shock din sedai nasa me sauki ne Dan aure ne dai kamar kowanne aure aka daura hakama tinda anriga an daura Babu abinda tashin hankalin zai kawo bayan hakura a rungumi kaddara.

Kuka takeyi sosai duk Wani nauyi da quncin zuciyarta na saki.

Shi kansa Abdul kukanta hakuri da juriyar abin yake qara masa Dan kuwa ya gaji da ganinsu cikin wannan tashin hankalin da kukan daga ranarda duk wannan matsalar fyaden ta fado,
Shi saima yanzu yakejin gwara da auren ya fada akan ASH TALBA sbd aurensa ne zai zama duk wata kariyar da Amatun ke buqata daga cikin Mansion din har waje,
Daga yanzu data koma AmatulMaleek Talba Babu Wanda zai iya kallanta ya sake tina maganar fyade bare furta magana makamancinta Dan haka shi Kam alhmdlh,
A ransa Haydar shine Wanda yaso ya auri Amatun duk da tazarar shekarun sbd shine yake mata so tin baisan meye so din ba Kuma akan mutuncinta zai iya tsaye mata koina,
Amma Kuma a yanzu data zama mallakin ASH TALBA din gaba Daya kusan yamafi Jin nutsuwar zuciya ga yar uwar tasa Dan yanzu itace macen datake saman kowacce mace a TALBAs bayan Madame abeeda tinda sune matan shugaba.

Zazzabin Daya rufeta ne ya Saka Abdul din kamata ta kwanta kan gadon da tin anan sun San anfara samun banbanci Dan kuwa dakin shine matsayin dakin madame Abeeda duk da Basu tare gidan ba bama ta taba zuwa ba Amma dai shine matsayin dakinta Amma yanzu matar me gidan Daya ta shiga.

Fitowa yayi daki bayan rufeta da abin rufar Dake gadon me tsananin laushi ya nufi dakin dasu maamah suke Suma daga maamah har Husnah din zazzabi kowa yakeyi hakama Faisal tini nasa zazzabin yayi karfi yabar Mansion din ya tafi masaukinsa daga can jirgi zaibi a da safe ya koma Abuja.

ASH tinda yagamo sallan magrib din Shima shigewa yayi bangarensa tareda kashe wayoyinsa ya tsaya a dan qaramin closet dakin kayansa ya zare kayan jikinsa a natse tareda janyo towel Daya daga cikin towels Dake Jere a bangare daya kusan guda ashirin duk farare kowannen kalar farinsa da taushinsa zaisa ka bambamtasa da normal towels daka sani masu qarfi.

Toilet ya nufa ya shige hannunsa Daya akan towel din qugunsa Da Bai daure da kyau ba.

Wanka yayo ya fito toilet din gaba Daya ya cike da qamshin Aesop liquid soap daya biyo har dakin sbd jikinsa Dake fidda qamshin fatar jikinsa kuwa kaman wadda Bata taba shiga Rana ba fresh.
Baya Wani shafe shafe bayan body oil na Aesop din me shegiyar tsada sai body perfumes kawai.

Abinci lafiyayye da drinks dasu tea harma da snacks masu zafi aka jere babban dining table din Dake babban dakin cin abincinsu tareda sake tsaftace gurin kaman baa jima da sake tsafatace koina n gidanba.

Abdulhameed ne kawai yazo Palo ya tsaya jiran yanda zai sanar da ASH din halinda duka su Amatu suke ciki.

Masu aiki tini suka bace bat daga cikin ainihin palon cikin gidan sbd sanin kowane lokaci ASH zai iya fitowa.

Babu jimawa sai ga qamshinsa ya fara doso palon Abdul na Jin qamshin ya miqe tsaya Yana Dan saita kansa tareda nutsuwa.

Cikin wata tsadaddiyar silk jallabiyan da basai anfadaba kana gani kasan jallabiya ce ba muna jallabiya ba,

ASH TALBA matashin me kudin da yanzu ne yake kokarin shiga dattijantakarsa sbd auren gata na wuri da Akai masa hakama ‘dansa Haydar kana ganinsa kasan shine ya haifesa sbd kyansu ya banbanta Dana Husnah wadda nata mahaifin ta dauko itama Zak a kamanni Amma dayake Yana kama da ASH sai itama take diban kamannin da ASH,

Zuba masa idanuwa Abdul yayi Yana Yaba nutsatsiyar halittar da Allah yayi a gurin,
Mutumin da Babu Wanda zai kallesa baiyi fatan inama shine shi din,
Mutumin da Babu macen da bazata kallesa ba taji Ina Allah zai bata matsayin da zai kalleta da wata siffar sbd shedan da duniya tai masa na mijin mace Daya ne madame Abeeda Talba wadda bayan tafiyarta Allah ne kadai yasan matan da aka ringa basa ‘yayan manya da manyan matan Amma Yana dakatarwa sbd baitaba kallan wata macen da sunan macen so ko aure ba bayan matarsa,
Ita kadai ta ishesa a rayuwarsa yake gani hakama duk wuya duk rintse bazai taba iya kulawa ko kallan mace ko wace iri bace da sunan mace matiqar Abeedansa tana raye ba mutuwa tayiba Wanda Baya fatan ta mutu ko ahakan datake kwance yana fatan Allah ya bar masa ita karta tafi tabarsa.

 

Isowarsa tsakiyar palon yasaka shi dago fararen idanuwansa ya zuba akan Abdul din Wanda yayi qasa da nasa idanuwan Yana Bude Baki cikin girmamawa yayi masa barka da fitowa.

Amsawa yayi a natse Yana nufar dining room Abdul din ya biyo bayansa cikin nutsuwa yace

“Gaba dayansu maamah da anty Husnah basuda lafiya harma da AmatulMaleek,Kuma sosai”

Dago Idanuwansa dasuka Saka Abdul Dan shin shiru yayi ya Kalli hanyar dakunan nasu ya Bude Baki yace

“Ba damuwa likita zaizo ya dubasu yanzu kafin mu tafi da safe sun warware Inshallah”

Ok Abdul yace Yana kokarin juyawa ASH din ya basa izinin zama yaci abinci shikuma juyawa yayi yakoma Dan kira ya Bada umarnin a Aiko musu kwararran likita yanzu a Talba mansion.
##MAMUH#
for more pages joining vip or follow me @Mamuhgee arewabooks

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button