Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 49

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

Related Articles

49
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

*****************
Kallan da Husnah takewa anty Farha ya Saka anty Farha din kallanta tana sake fuska da kulawa tace

“Husnah kinfito kenan,barka da safiya,Yaya gidan?”

Cikin Dan kokarin boye mamakinta ta amsa da cewa

“Barka da safiya anty Farha,yau sammako kikai kenan keda ya kamata ki huta anty Farha kinyi hidima jiya”

Dariya anty Farha tayi tana qarasa zama a palon daukeda cup din custard me zafi data Saka karima ta hada mata tace

“Wlh Hutu Nan Ina buqatansa haryanxu Amma matar gidan Nan taku ce ba lafiya sosai shiyasa kika Ganni da sassafe a gidan,Amma inshallah tana Dan warwarewa zan tafi Nima na huta”

Kofar bedroom din Amatu Husnah ta kalla cikin takaici da mamakin yanda anty Farha din ta ambaci Amatun wai da matar gidan da Dan mamaki tace

“Me ya sameta ne?
Lafiya kalau fa ta kwanta jiyan da daddare.

Murmushi anty Farha tayi zatai magana kenan mum Aisha ta shigo palon maamah na bayanta dukkaninsu kallan Farha din sukeyi da mamaki dakuma ganin yanda Husnah itama take tsaye da mamakin tana jiran amasan anty Farha din.

Ita kanta kallansu tayi duk da mamakin ganin yanda kowannensu ke kallanta kaman wainda Basu taba ganinta ba.

Tamkar zakunan dasuka ga nama haka suke kallanta kafin maamah ta Dan juya ta Kalli hanyar dakin Amatu tana sake dawo da kallanta kan Farha wadda ta nutsu ta hadiye maganarta ta saki murmushi tana kawar da tinaninsu duka akan koma me suke tinani da son jin duk da Babu Wanda ko a giyar hauka acikinsu ya kawo tinanin da itama takeyi din akan nasu tinani ta Bude Baki fuska a sake Kuma cikin girmamawa ta gaida maamah kafin ta gaida Mum Aisha tana cewa

“Amatu ce ta kwana ba lafiya shine nayi sammakon zuwa sbd jiya Koda muka rabu Daman tana Jin zazzabi sosai da ciwon mara shine nayi sammakon zuwa da likita ta dubata Amma taji sauki”

Gaba dayansu a tare suke sake juyawa suka kalli kofan dakin Amatun maamah ma abinda Husnah ta fada ta maimaita cewa

“Lafiya kalau fa na rabu da ita jiyan da dare,wane ciwon mara Kuma a tsakiyan wata?

Mum Aisha dakin ta zubawa idanuwanta Bata ce komai ba kafin ta juya ta nufi bedroom din Kai tsaye sbd ganewa idonta ciwo da jikin Amatun.

Husnah ma kusan Daman dakin take kokarin nufa Dan gaba dayansu Hakanan sukaji ciwon nata na Neman Hana zuciyarsu nutsuwa.

Maamah ce a bayansu lokacinda suka Bude kofan bedroom dinta suka shigo dakin idanuwansu akan Amatun Dake bacci sosai fuskarta ta kumbura sosai alaman tayi kukan ciwon Kokuma kukan Wani abin.

Rarraba idanuwa kowannensu a fakaice yakeyi a dakin batareda sunga komaiba sedai hancin Husnah dayake Dan shaqar mata qamshin Dad dinta a dakin zuciyarta na harbawa Amma tana sake bawa kanta tabbacin ba Hakan bane shedan ne kawai da ke Sakata Jin qamshin dan haka Allah ya Bata lafiya kawai sukai mata fata suka fice Banda maamah data qaraso har bakin gadon na Amatu ta zauna a hankali tana kallanta cikin tausayawa ta dawo da kallanta kan Farha Data zauna kan sofa tace

“Menene ya sameta a dare Daya haka?
Likitan me sukace yana damunta?

Shiru Farha tayi tana shiga nazarin abinda zata fadawa maamah wadda ya kamata ace ta sanarwa gaskiyar maganar abinda ya samu Amatun Amma Kuma tasan fadawa maamah gaskiar zai kawo babban tashin hankali da baraka me girma tsakanin uwa da ‘ya Wanda bazataso Hakan ba musamman yanzu da Amatun take cikin wannan halin.

Numfashi ta sauke me sanyi wanda ya Saka maamah sake zuba mata idanuwanta tana jiran amsarta.

Kallan maamah din tayi ta Bude Baki a natse tace

“A yanzu dai taji sauki Se Dan abinda baa rasaba,ciwon mara ne kawai Se Kuma damuwa da sukace tana ciki tana buqatan kulawa…..

“Damuwa Kuma?
Damuwan me?
Akwai abinda yake damunta ne Wanda ban saniba?”

Cikin sanyi da damuwa Maamah ta jerowa Farha din tambayoyin wainda suke kashe jikinta da son fadawa maamah Amma Kuma tana danne zuciyarta da Hana kanta
Tace
“Damuwa bazai wuce na karatu da Kuma yanda kike kasa yarda da ita wasu lokutan maamah akan abinda ba laifinta bane,ba ita ta zabawa kanta Hakanba, a gabanki gaban kowa lamarin ya fada kanta Wanda kaman yanda kikaji haka tajisa maamah Amma kina ganin lefinta akan Hakan lokuta da dama,
Maamah Amatu na buqatanki sbd ke kadaice uwa Kuma abokiyar shawara da walwalanta,
Dan allah maamah ki Dena nesanta kanki da ita akan auren da Allah ne ya daurasa Dan kuwa shine ya qaddara ASH TALBA ne mijinta ba Itace ta kaddarawa kanta Hakanba…..

Kalmominta na karshe ne suka Saka maamah data fara yin sanyi da nasihar Farha din sauya zancen tareda dakatar dashi ta hanyar miqa hannunta ta dafa goshin Amatun daya huce Babu zafi a jikinta sbd alluran datasha da magani a asibiti ta Bude Baki tana cewa

“Allah ya Bata lafiya dai.”

Amin”Farha ta amsa dashi lura da maamah Bata son ko zancen auren Amatun da ASH tsaban zuciyarta ta bushe qyam akan auren batada Kuma niyar amsar auren.

Wayoyi anty Farha ta fara cikin nutsuwa da sakewa Wanda aket ayi mata na barkan waliman jiya
Maamah kuwa tana zaune tana kulawa da Amatun duk da bacci takeyi sosai batama San waye akantaba.

 

*****Qarfe goma sha Daya ya fito shirye tsaf cikin navy blue yadi me tsananin tsadan gaske hannunsa daure da agogon Rotary men’s Regent watch qamshinsa na tashi a cikin sanyin fuskansa fresh Wani irin nutsuwa ne ya bayyana a tareda shi duk da Shima a sanyaye yake baa ganewa sbd kasalan daya samu kansa acikinta.

Fitowansa yayi daidai da ihun da Husnah ta buga acikin gidan dukkaninta jikinta na tsananin rawa da farin ciki da rudewa harma da firgicin abinda bata taba tinanin zata ji ba arayuwartaba sbd tashin mahaifiyarta Wani abu ne da kusan kowa ya cire ya debe tsammani idan aka cire Dad dinta da Bai taba cire daga tashin matar tasa ba.

Aunt labiba Dake can qasar ce ta kirata ta sanar da ita wannan labarin Daya firgitata ta saki ihun da batasan tayi ba.

Ganin Dad dinta a gabanta lokacinda y Sako Kai palon nasu Dan isa dakin Amatun ya Sanyata qarasowa gurinsa ko Gani batayi Dan tasan ihunta ya sanyasa shigowa tana tsayuwa gabansa bakinta na rawa duk jikinta ma rawa yakeyi tace

“Dad,mum ta farfado, your wife is out of coma, she’s conscious Dad…..

Bata qarasaba kawai ta yanke jiki ta zube a ya tarota jikinsa komai nasa na dakatawa Shima cikin Wani irin mamaki da shock Dan bazai yiyu Hakan ta faru ba ace a bakin Husnah din yake ji ba batareda asibitin sun nemesa ba.

Maamah da Farha ne da ihunta suka fiddosa da gudu suka ganta some a jikin Dad dinta da sauri Maamah ta kamota tana dawo da ita jikin Farha suka kamata zuwa kujera shikuwa juyawa yayi ya fice idanuwansa na sauya batareda kansa ya dauki zancenba tsaban tashin hankalin idan ba Wani ne zai rikita masa qwaqwalwan ‘ya ba Amma tayaya matarsa zata Farka bayan shekaru a kwance ace ba shine na farko da zaa sanarwaba.

Mr Jameel Dake jiran saukowarsa a guest Palo Dake gefen security room da sauri ya fito ganin Kiran ASH din akan wayarsa.

Yana fitowa Babu mota Kai tsaye ya Bude masa ya shiga da sauri Shima ya shiga suka kama hanyar office Dan vcall yake buqata da Personal attendant na room din da Abeeda take.

Daga securities har mr Jameel take suka fahimci yau din yanayinsa a bayyane yake na bacin Rai da rashin sanin gaskiyar maganar.

Suna isowa office da sauri mr Jameel yabiyo bayansa cikin office dinsa kafin ASH din ya qara taku biyu cikin sanyi da damuwar jinkirinsa da Dan shakku yace

“Tin dare kanada pending call Daya Greece madame is conscious nayita Kiran…….

Dakatawar da ASH din yayi zuciyarsa na daukewa daga wutan bugawa ya Sanya Mr Jameel din yin shiru Yana qasa da kansa cikin damuwa.

Hannunsa Dake nade da bandage yakai ahankali ya dafa table Dake gabansa Dan jiri da nauyin da zuciyarsa ta Dan dauka da abinda Jameel din ke fada masa yanzu.

Ganin hakan Mr Jameel ya dago cikin son isar da sauran bayanin yace

“Nayi booking komai na tafiya zuwa can din komai a shirye yake ticket kawai za’a Siya”

Rintse idanuwansa da sukai jajir ASH din yayi kusan sanyi da Wani irin nauyi dayaji Yana sauka daga zuciyarsa yaji suna gangara jikinsa.

Qarasa zaunawa yayi Yana Bude laptop din da Mr Jameel yayi saurin kawowa ya ajiye gabansa Kai tsaye yayi Saka Kiran Kai tsaye me zuwa dakin Abeeda.

Mintina kafin Kiran yayi connecting aka basa Daman miqa Kiran zuwa dikinta Kai tsaye.

Abinda ya Gani ne ya sanyashi rintse idanuwansa Wani abu me nauyi da tarwatsewa daga kirjinsa idanuwansa sukai sauya take zuwa ja a Karan farko Dayaji yana kasa riqe yanayinsa na farin ciki da mamakin Daya girgizasa ganin Abeeda idanuwanta a Bude aunt labiba na tareda ita da nurse a dakin duk da kwance take Amma idanuwanta dasuke a Bude Kuma itama shi din Daya bayyana tv Dake dakin take kalla hawaye na gangaro gefen idanuwanta suna saukowa.

“Abeedah” ya furta cikin sautin Daya qarawa hawayenta gudu tana Dan motsawa ahankali.

Motsawanta ya Sanya aunt labiba fashewa da sabon kukan farin ciki shikuma Jin yayi Babu abinda yake buqata a wannan lokacin bayan ganinsa a Greece Dan haka Tim kafin ya dago ya Kalli Mr Jameel dayafi kowa sanin maanar ko motsin ASH da sauri ya juya ya fice Yana Ciro wayarsa daga jikin tsadaddiyar suit dinsa take yakira ya Siya ticket din da zasu Isa Lagos a ayau gobe su wuce.

Madame abeeda kuwa hawayenta ne suke qara gudu ganin fuskar mijinta datafi so fiyeda komai da kowa,
Shine hasken idanuwanta Kuma qarfinta kuzarinta da yayanta Dan haka hawayenta ke qara gudu tanajin tsananin son ganinsa a kusa da ita shi da yayanta.

A nasa bangaren kasa magana yayi bayan sunanta dayake ambata yanajin yau ranar itama ta musamman ce a garesa da rayuwarsa.

Mr Jameel kuwa tini ya fara clearing schedules din ASH din gaba Daya na wannan satin da satin gabansa Dan kuwa a yau zasu wuce Lagos.

A can gida kuwa a lokacinda maamah da anty Farha ke kokarin dawo da Husnah hayyacinta tana Bude idanuwanta abinda ta fara kallan maamah tana furtawa shine

“Maamah mum dina ta farfado,
Mum dina ta tashi,
Mum dina zata dawo gareni ga mijinta Dad dina,
Maamah mum Bata barmu ba ta dawo”

AmatulMaleek data farfado daga nata baccin a lokacin cikin Dan samun karfin jiki da kuzari ta tashi zaune ba zazzabi a jikinta Dan haka wayarta kawai ta miqa hannu ta dauka Dan Neman anty Farha a waya tazo sai alokacin idanuwanta suka sauka kan sakon anty Farha din tin na cikin dare.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button