Hausa NovelsMijin Malama Book 2 Hausa Novel

Mijin Malama Book 2 Page 36

Sponsored Links

Wani irin deep hot kisses ya yi mata mai sanyi wanda ya sanya ya ji numfashinta ya sauka a neck ɗinsa, wani irin ƙamshin mai haɗe da sanyin Spraymint mouth freshener ya ratsa hancin Khalil, wanda yake jinsa har ƙasan zuciyarsa, ta ɗan hasken daya rage ya tallafo fuskarta yana mata wani irin zallar kallo mai cike da sahihin so da ƙauna, kallonta yake kamar zai cinyeta ɗanya, ya jima da fahimtar ba a reality take ɗaukan dukkan wani abu da yake mata ba.

Jikinsa ne ya ɗauki rawa da ɓari, kamar yadda nata yake, jikinta ya gama farkawa ita ɗince dai har yanzu idanunta yake rufe, amma ilahirin gab’ɓanta karkarwa suke, jikinta ya mimmiƙe wani irin hargitsatsen fitinannan saƙo Khalil yake aika mata, a hankali ta fashe da siririn kuka tana riƙe kansa tare da danna shi a ƙirjinta da kyau, yadda zai samu full access na yin abinda yake, cikin raɗa daidai kunnen shi ta furta. “My poor darling Khalil? Kaga me su kaiwa ruhinka ko? Ina ce ka gani? Nasan ko baka raye zan kasance da kai, ruhinka zai dawo gareni zan sake haifa maka wasu babies ɗin”

“My fatalwar duniyata? Ka ce su raba aure na da Alpha bana so, bana so ba zan iya cin amanar ruhin mijina ba, Man ko a fatalwa ne kazo ka shaida musu zaka rayu dani, sun yi mini aure bana so” Ta faɗa tana shassheƙa sosai, a hankali kuma kamar tafiyar tsutsa take tura yatsun hannunta cikin sumar shi tana shafawa slowly slowly, wanda yake ƙara hargitsa da gigita Khalil, wutar abinda yake ji tun a U.s ta ƙara tsananta. Wani irin gigitaccen rikitattan al’amarin ne ya ruftawa zuciyarsa, jin tana furta kalmar aure? Is he dreaming or what? Tayi aure bayan auren shi da yake kanta? Bayan ya ce kada ta manta da shi?

Related Articles

Ya runtse Idanunsa, zuciyarsa na kerma, jikinsa na jijjiga, ya kifa kansa a ƙirjinta domin They’re already naked! “Why? Sweet why? Zaki tarwatsa mini zuciya?” Jee da take tunanin komai mafarki ne, irin kyakkyawa bacci mai ɗauke da mafarkin mijinta da ruhin Dr Ibrahimul-khalil Abraham, ta girgiza kai ita kanta ɗin jikinta rawa yake muryarta bata fita saboda tsananin buƙatar mijinta da take ta damƙo wuyansa tana mannawa a fuskarta bakinta a saitin kunnen shi numfashinta mai zafi na fita yana saukar masa a jikinta yana haifar masa da wata kalar kasala jiki ta ce “I have no choice, sun ɗauka na haukace, bana son auren ka fito daga kabari ka shaida musu a raba”
Khalil ya zuba mata narkakkun idanunsa wanda suka jirkice, hannunsa na kyarma while duk ilahirin jikinsa ɓari yake, tare da wata tsuma kamar mai shirin sumewa.

“I love you sweet” Khalil ya ƙanƙameta yana jin salama a zuciyarsa ya ce “Say it again, say it, i want to hear it a millions time from you!” Majeederh tayi shiru jin abin yana nema ya girmama. Khalil ya damƙi lip’s ɗinta ya yi mata kalar american kisses, ya dawo hancinta ya dawo cheeks ɗinta, ya yi saman forehead ɗinta, ya yi a kunnenta ya dawo idanunta, a hankali ya shiga sauke mata wasu lafiyayyen kisses mai nuna “I Miss you soo soo much” Kafin ya ɗora bakinsa a tsakiyar ƙirjinta ya sumbata gently clamly cikin husky voice ɗinsa so Calm and sexy ya ce “I love you! I love you like crazy, i love you so much Madam”

“I love you too hasken idaniyata” Dr Ibrahim ya yi shiru, looking at her with his eyes full of desire for her, and at the same time their breath fell on each other’s face ya ji ta ƙanƙame shi a kasalance ta ce “Don’t leave me, I’m deadly in love, with you ruhin mijina” Kspider ya kasa magana, al’amarin ya juye duk yadda taso ƙwacewa ta kasa ta fara kuka a gaggauce jin wata matsananciyar azaba, domin ya gama farke ɗinkin haihuwar su Al’hussan da akai mata, tana jin kamar yanzu ne ta fara sanin namiji, idan tayi kamar zata tashi ko buɗe ido amma bata iyawa, gani take tana buɗe ido zata farka daga daddaɗan mafarkin da take, al’amarin da yafi ƙarfinta Khalil babu alamar dainawa yasa a gigice ta buɗe ido ya yi saurin saka tafin hannunsa a fuskarta a hankali ya furta “Karki tsorata ruhina, yanzu zan koma kabari cikin salama, I love you Malama na har abada” Tayi shiru tana sauke numfashi, Khalil ya ja kayansa ya faɗa ƙasa tare da shigewa ƙasan gado, daidai nan Majeederh ta farka a gigice tare da kunna switch ɗin bedroom, baki ta buɗe za tayi ihu tayi saurin sanya tafin hannunta ta toshe bakin, ta shiga ganin kanta naked, tashin hankali ya wanzu a fuskarta, ta sulale ƙasa ta durƙushe ƙasa kan ƙafafuwanta, jikinta ƙyarma da tsuma haɗi da wani irin ɓari da jijjiga yake, what’s happening? What’s going on? Da gaske ruhin Khalil ko fatalwar shi tazo gareta? Fatalwar mijinta ta kusanceta? Ta haɗe kai da quiwa ta kasa tunani ko fahimtar komai, wanne irin nightmare ne wannan? Ya bambanta da irin wanda take.

“Man! Kai ne? Da gaske ka fito daga kushewarka? Ka dawo gareni kar na samu taɓin hankali, ba zan iya amsar Alpha matsayin miji ba, sun kasa fahimtar mijin Malama yana duniya, ina jinsa, ina ganinsa gashi yanzu mun samu haɗin auratayya!” Gashin kanta ya birkice wani Irin harbawa zuciyarta take, deep down na zuciyarta wani daɗi da farin ciki take ciki yau ta gana da ruhin mijinta har sun yi magana. Khalil dake kwance bayan gado ya lumshe gajiyayyun idanunsa yana jin kansa wani fresh, wasu kalar hawaye suka sakko masa cikin ransa ya ce “I am sorry Madam” Wai shi soyayya ke sanya shi hawaye? Shi Kspider? Majeederh ta miƙe da ƙyar ƙafafuwanta na mata ciwo da duk jikinta ta nufi bathroom.
Cikin sauri Khalil ya fito ya saka kayan shi, har zai shige sai yaga farar powder ya ɗauka ya burshine fuskarsa da ita, a hankali without making any sounds ya fita ya nufi Main parlour daidai nan kuma Yaya Bilkisu ta fito raka Innati fitsari domin a gidan suka kwana. Cak! Yaya Bilkisu ta tsaya jikinta na rawa saboda babu wani hasken kirki a main parlour ɗin, sai wani haske mai duhu, kamar daga sama taga mutum tsaye saboda tsananin firgita da kaɗuwa da tayi sai taga gabaɗaya fararen kaya ne a jikinsa, ta ƙura wa fuskarsa Idanu dam! dam! Zuciyarta ta bada sauti ganin Khalil, wani irin karkarwa jikinta ya fara zufa na yanko mata tuni wani irin fitsari ya fara bi ta gefen cinyarta hankali tashe ta ce “Innalillahi wa’inna ilahir raji’un! Wa’innahu sulaimanu wa’innahu bismillahir rahim, Fatalwa?” Khalil ya washe fararen haƙoran shi yana kumbura murya ya ce “Nine, fatalwar mijin Malama” Innati ta gwalo idanu ta ce “Innalillahi mun shiga uku, fatalwar Khalil?” Khalil ya karkace murya ya ce “Fatale ba fatalwa ba zan jaku izuwa kabarina mu rayu tare” Tuni sauran fitsarin ya gama sakin kansa, Innati gudawar da take riƙewa ta saki tana rushewa da kuka ta ce “Wanne irin kabari ba daɗin ji, don Allah Allah kayi haƙuri” Khalil ya ce “Sharaɗi ɗaya ne, ku gaggauta raba auren matata da wani idan ba haka ba zan ɗauke ku” Yaya Bilkisu ta ce “Wallahi tallahi za a raba ko zai mutu gobe goben nan zamu raba auren, ruhinka ya zauna cikin salama a kabari” Kuka suke suna rungume da juna, Khalil yana toshe hanci saboda warin gudawar Innati ya ce “Matata ce, abar ruhina ya samu sauƙi” Innati ta ce “Uban ubanwa ya isa ya sake taɓa ruhinka, baiwar Allah fatalwa kiji tausayina” Khalil ya yi kansu yana miƙa hannu lokaci guda suka saki ihu suna rungume juna sai kuma suka zube saman carpet a sume, daidai nan Uncle Bello ya fito a gigice,kamar gilmawar walƙiya Khalil ya fice, a hankali ta bayan gidan ya kama katanga ya dira, ya samu John zaune cikin mota yana jiran shi, yana shiga yaja motar suka bar unguwar.

Har safiya Innati bata farfaɗo ba, Yaya Bilkisu tayi zuru idan ka ganta zaka ɗauka tayi shekara bata da lafiya, time to time take miƙewa zuwa bathroom. Innati na farkawa ta ce “Bello kira uban kowa metin a gidan nan” Uncle Bello ya ce “Meeting kuma? Ba jiya akai ba?” Ya fusace ta ce “To wallahi Allah ya isa idan na sake maimaitawa” Uncle Bello ya ce “A’a, Allah ya baki haƙuri” Waya ya ɗauka ya kira iya manya hadda Jawaad, General Alpha, Abbu, Uncle Isma’il, Mami. Maman Alpha dai bata ce komai ba ta miƙe tsaye ta nufi bedroom ɗin Majeederh da taƙi fitowa ta sameta tsugune tana haɗa coutan, ta nemi waje ta zauna ta kalli Alhassan da kansa ke ƙasa baya ko motsawa ta kalli Al’hussain shi kuma yana bayan Majeederh ya ɗan rungumeta. “Sai yanzu za suyi breakfast?” Majeederh ta girgiza kai a taƙaice ta ce “I had a sleepless night jiya, shiyasa na makara” Maman Alpha ta ce “Ai kinsan Alhassan yanzu bari kiga zuwan da dawowar, da kin kawo su wajena” Majeederh dai bata ce komai ba, tana gama haɗa cup ɗin farko ta kalli Alhassan gabanta na faɗuwa a hankali ta ce “Sweet amshi kasha” Ya kalleta sosai sai kuma ya kwaɓe fuska a hankali ya amsa kamar zai sha ya doka cup ɗin da bango ya tarwatse ya shiga buga kansa yana kuka, Maman Alpha ta ce “tirƙashi, gobara a gemu, ji dashi bari na haɗawa Al’hussain” Majeederh ta rasa ta ina zata fara, komai na Alhassan tana so acting ɗinsa yana ƙara tuna mata da mahaifinsa, ta matsa kusa da shi a hankali ta ce “I am sorry sweet, na baka chocolate” Ya yi mata shiru ta dinga lallashi daga ƙarshe bacci ya yi bai sha costan ɗin ba. Majeederh ta sauke ajiyar zuciya tana rungume shi. Baby khalil ne ya shigo ya ce “Mimi Kizo” Ta zubawa first born ɗin nata Idanu a hankali ta ce “Come” Ya ƙarasa ta ɗauke shi ta ɗora a cinyarta tunda bashi da wani girma sosai saboda ciwo ta sha kansa ta ce “Ya ƙafan?” Ya yi murmushi yana girgiza kai ya ce “Shaaahh ya daina” Ta rufe ido tana son fahimta da sanin ina Baby Khalil ya samu sikila? A wacce ƙwayar halitta? Ta miƙe goye da Al’hussain ta rungume Alhassan a ƙirji hannunta ɗaya riƙe da Baby Khalil ta nufi parlo.

Gabaɗaya suka zuba mata Idanu cike da tausayi da sha’awa, Alpha kamar ya cinyeta don kallo, Abbu ya kalleta ta durƙusa a ƙasa ta gaida su, Innati ta ce “Ubanwa kake Alfi ko wa? Maza maza rubutawa Majeederh takaddar saki” A makake Alpha ya kalli Innati ya ce “Hujja?” Ta ce “Ubanka kai da hujjar, mu kaɗai muka san me muka gani” Ya miƙe tsaye ya ce “Ji mata? Idan don wannan ne, wallahi wallahi Allah ba zan taɓa sakin Hawwa’u ba, I love her! Babu kalmar saki ko da wasa” Ya zube gaban Majeederh yana kama hannunta tare da ɗorawa a ƙirjinsa, ji tayi zuciyarsa kamar ta fito waje saboda bugawar da take da ƙarfi,ya rame ya yi wata kala, muryarsa na rawa hawaye na bin fuskarsa ya ce “Ina son ki, not today, not now ina sonki tun ranar da kika zo duniya, don Allah don girman Allah Hawwa’u ki tausayawa raunatacciyar zuciyata, i love you so much ina son ki fiye da rai da rayuwata”
Ya durƙushe sosai a gabanta jikinsa gabaɗaya rawa yake, tunda suke a rayuwa babu wanda zai taɓa cewa yaga hawayen Alpha ko da wasa balle kuka, rawa jikinsa yake da kyarma a hankali ya kifa kansa a cinyarta yana sakin wani irin raunataccen kuka mai cin rai da zuciya, ya jima kafin ya ɗago ya ce “I live every seconds, every minutes, every hours, every week, every month, every years, i live just because of your love, ban taɓa sawa ko kawowa bani ne first and last Husband ɗinki ba fid duniya wal lahira, ki tausaya mini” Majeederh hawaye take sosai ta ce “Ka tausayawa zuciyata yaya, ina son ruhin mijina ban iya cin manar shi har abada bazan iyaba…..” Daga bakin ƙofa aka ce “And i love you too husband, ka shaida musu kafin Majeederh kana da wata matar Zuleehart da yara uku….

Kuna manta Littafin nan na kuɗi ne? Don Allah ku sauke hakƙina, ba zagi ba baƙar ba cewa ban yafe ba, domin nafi ƙarfin na yi zagi darajata tafi haka😂🤌🏽 08119237616
[

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button