Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 75

Sponsored Links

*************
Maamah ce take hawaye suka tsinke mata tana rufe idanuwanta zuciyarta na daukan nauyi me girma,

Mum Aisha kuwa gushewa hankalinta ya fara yi na seconds tareda jinta gaba Daya kafin ta ji ta Dan ji jinta ya dawo ta Kalli ASH din da dukkanin karfin ganinta hannuwanta na daukan rawar datafi rawar tela murya a rikice tace

“Auren addinin islama Wanda nasani???

Wani kallon Daya Sakata rikicewa ASH yayi mata da idanuwansa da har lokacin Basu koma daidaiba..
Rudewa tayi take tana rikicewa a rude ta fito daga bayan Maamah datake zaune bakinta na rawa hakama jikinta tace

“Ka yimun Rai ka dubi Allah ka dubi Annabi ka dubi maraicina Banda uwa Banda Uba Se Kai se Naufal,
Kaine uwata Kaine ubana wlh na tuba nabi Allah na bika ta tattara tashin hankali duk na aje Amma Dan Allah Karka auramun aure da girmana yanzu Kuma a kauyenda mota ma Bata shiga wlh rayuwata mutuwa zatai,haukacewa ma zanyi,Dan Allah kayi hakuri Karka min auren dole da girmana na tuba,Dan Allah kayi hakuri…..

Tsit palon yayi maamah ma hawayen takeyi tana sharewa kai a qasa Dan ita bama zata iya magana ba Dan Iya ganin mugun Abu yau shi take Gani sirikinta zai mata aure kaman na dole,tayaya ma zata rokesa tace Dan Allah karya mata auren? innalillahi wainna ilaihirrajiun.

Husnah kuwa Bata motsaba sbd Bata dauka ita Husnah din ake nufi sbd kwata kwata ma Babu abinda ya hadata da auren kowa yanzu bare,

Abdulhameed ne da Haydar suka shiga tashin hankalin hukuncin Husnah da maamah kawai da basason ta koma kauye Dan haka Haydar ya juyo Yana kallan Dad din nasu zaiyi magana ASH ya daga masa hannu kadan alaman bayason Jin komai.

Su kawu kuwa washe Baki suka hau yi suna sauke kansu qasa kawu ashiru sai kallan mum Aisha yakeyi yanajin shi gaba Daya ma Sonta ya kamasa a gurin.

Uzaifa ma Husnah ya zubawa jajayen idanuwansa masu girma kaman yalo ya taso saman manja
gaba dayama Jin yayi yawunsa na tsinkewa kaman zasu zubo masa da kallanta kawai,
Baitaba tinanin zai taba samun mata irinta ba koma a mafarkin duniyar aljanu aka Kaisa kuwa.

Ganin irin kallan da uzaifa kewa Husnah yasaka Haydar kasa shiru cikin tsananin damuwa da tashin hankali yace

“Dad dan Allah kayi hakuri ka sassauta musu hukuncinsu duba da yanayin rayuwar da ba Daya ba,Dan Allah Dad ka duba,ayi musu afuwa musamman Husnah da take yarinya, Dad…..

Kallan da Husnah ta jefawa Haydar din tana dagowa gaban Daya ne ya Saka Haydar dakatawa Yana kokarin hanata magana tace

“Dad ni aka bawa waye aure?
Dad aure ka bayar Dani?

Uzaifa na Jin haka ya washe Baki tana Dan motsawa tareda Shafa kansa dayake kaman gashin awaki daga nesa.

Juyowa Husnah tayi ta kallesa Yana sake washe hakoransa da miyar kuka ta Dafe
Wani ihu ta saki cikin gigicewa ma da ganinsa gaba Daya jikinta na daukan Wani irin rawa da kakkarwa ta rarrafo ta wuce mum Aisha Dake gabansa zuwa gurin qafafunsa tana fashewa da kuka me qarfin gaske komai nata rawa yakeyi tafara cewa

“Dad Dan Allah ka yafemun ka yafemun Karka kasheni,wlh mutuwa zanyi idan ka auramun wannan mutumin,ni tsoronsa ma nakeji Dad Karka Kaini Karka auramun shi na tuba,na tuba na Dena komai ma,na Daina fadan,na Daina ko fitowa daga dakina Amma Dan Allah Dad Karka hukuntani haka Dad bazan iya daukaba ni mutuwa ma zanyi Dad.”

Yanda ASH din fuskarsa take daure tamau ba sauki bare ya kallesu ya Sakasu qarasa dimaucewa gaba Daya Dan kuwa ba alaman ma Yana Jin zancensu bare sassauta musu Mum Aisha take itama kukan da batasan tanasa sauran hawayen yinsaba ya kufce mata tana tonawa kanta asiri da Neman tuba da yafiya akan karya aura mata kawu ashiru.

Husnah gaba Daya fita hayyacinta tayi tafara kukan fitar hankali tana rokonsa,
Haydar ta rarrafo ta kamata tana rokonsa ya roki Dad din cikin tsananin kuka da tashin hankali gaba Daya ta fice hayyacinta cikin mintinan da Basu Gaza biyar ba.

Kallansu kawu ASH yayi Yace su tafi kawai zai nemesu da safen kafin daurin auren.

Tashi sukai suka fice kowannensu ransa fes Dan shi kawu ashiru ma yanzu ne dadin tashin hankalinsu ya rufesa tinda gashi sunyita tashin hankalin Rabo ya samesa Yana zaune kalau tsuntsu daga sama gasashe.

Suna ficewa hawayen mum Aisha suka qara gudu tana rokon ASH da dukkanin zuciyarta da qarfinta.

Ganin halinda Husnah ta shigane kwata kwata kaman ta zauce gunjin kukanta kawai ke tashi a gurin ta saki Haydar ta kama Abdulhameed Shima tana rokonsa ya roki Dad dinta karya aura mata wannan mutumin kauyen.

Mum Aisha ma kuka takeyi sosai sbd tasan maganar ta gudu ma Bata taso ba Dan batada gurin zuwa har ita har Naufal gwara ta tsaya ta roko ASH ya sassauta ya dubi maraicinta ya janye hukuncinsa.

Yanayin Husnah tini ya karya zuciyar Haydar gabaki Daya harma da Abdulhameed Wanda yakejin radadin hukuncin da tausayinta sbd yasan ko kwana Daya bazata iya a rayuwar kauyen ba.

Haydar jajir idanuwansa sukai Yana kallan Dad dinsu cikin tsananin damuwa da qasqantar da Kai duk da yaji laifukan da su Husnah din suka aikata musamman ita din a bakin Mum Aisha gashinan tanata fada Amma duk girman lefin nata aure a kauye da Miji irin wannan qarasa zauncewa ma zatai.

Qarfin Husnah take ya fara qarewa ta rarrafo gurin Haydar ta qanqamesa tana sake kuka sosai da yake jinsa har cikin ransa ya rungumeta Yana kokarin rarrashinta Amma Sam taqi tsayawa kukanta tsananta kawai yakeyi tana cewa ta tuba ta Dena komai.

Abdulhameed ne ya zuba mata idanuwansa da sukai jajir yanajin Shima bazai iya barin akaita kauyen aure ba kaman yanda bazaiso Amatu tayi zaman aure a kauyen ba,
A Baya Amatu ta samu kanta a irin wannan halin ya tsaya Kuma ASH dinma ya tsaya suka qwatota Dan haka ko Husnah duk laifinta rayuwar kauyen da auren uzaifa kashe rayuwarta gaba Daya zatai.

Juyowa yayi ahankali tareda dago kansa daga duqen dayake ya kasa kallan ASH sbd nauyin da kirjinsa yayi ya Bude Baki cikin girmamawa da nutsuwa yafara rokonsa Shima tareda basa hakuri zuciyarsa ta sanyaya.

Husnah Da qarfinta ya fara qarewa rarrafowa tayi gurin Abdulhameed da sauri ta riqe hannunsa Daya da hannuwanta biyu a rude ta Kalli ASH tace

“Dad Dan Allah idan kayi alkawarin bazata barni ba ka auramun Abdulhameed na yarda zan zauna dashi shi akan wancan mutumin wlh tsoronsa nakeji,
Dad dan Allah ka auramun Abdulhameed wlh inaso zan zauna dashi zan masa biyayya zan shiryu,Dan Allah Dad.”

Abdulhameed kusan mutuwar zaune yayi sbd mamaki me tsananin gaske da tashin hankali,
Dagowa yayi da sauri tareda kallanta cikin yanayi na rikicewa ma dayake Neman yi sedai kallan da ASH ke masa da yanda take kuka sosai har batada karfi ya sanyashi yin shiru.

Sake qanqame hannunsa tayi tana maimaitawa Dad dinta zata auri Abdul din zata zauna dashi ko inane.

ASH sai alokacin ya zuba mata idanuwansa da suka sake sauyawa sbd duk kukan datakeyi a cikin ransa yake jinsa sbd harga Allah Yana son ‘yar tasa kawai hukuncine dole yayi mata idan yanaso ta dawo daidai.

Haydar Dora idanuwansa da sukai jajir yayi akan Abdul Yana masa kallan fatan hakan ta kasance Dan Shima zaiyi farin cikin Husnah ta auri Abdul sosai fiyeda uzaifa din.

Irin kallan da Haydar ke masa hakama da yanda Husnah ke zake kuka sosai a jikinsa ya sanyashi Jin zai iya auren nata Dan kubutar da ita daga auren da bazai taba son ai mata ba.

Dagowa yayi ya Kalli ASH cikin girmamawa da jarumta yace

“Eh inasonta zan aureta,Dan Allah a auramun ita zan kula da ita ta Dena dukkanin urin wannan lefin,ayi mata afuwa ta tuba”

Duk tashin hankalin da mum Aisha take ciki da kukan datakeyi Saida ta dago tana kallan Abdulhameed din da Husnah ta maqalalewa gaba Daya batama hayyacinta,
To tayaya ma zaa bari Husnah ta kaucewa hukuncin zuwa kauye bayan itace duk ta ja musu wannan masifar.

Haydar cikin damuwa me girman gaske ya fara rokon Dad din Daya tausaya ya sassauta Husnah abawa Abdul din Dan Allah tinda yace zai aureta din.

Maamah ma dagowa tayi ta Kalli Abdulhameed din da Husnah kafin ta dawo da kallanta gurin ASH batareda ta iya kallansa ba murya a shaqe sbd kukan datasha ta fara rokonsa akan karya aurawa Husnah uzaifa a aurawa Abdul din Dan Allah.

Mamakin tashin hankali mum Aisha tace Bata yarda ba sbd Husnah dince duk me girman lefi a duk abinda suka aikata din hakama itace ai ta Saka Naufal zuwa yiwa Fyade Dan haka itace tafi kowa cancantar zuwa kauye.

Babu Wanda ya kula mum Aisha din duk da daga ASH har maamah, Abdul da Haydar Babu Wanda zuciyarsa Bata quna da yanka akan maganar Husnah dince ta tura a yiwa Amatun fyade sedai Kuma duk da Hakan bazasu bari rayuwarta ta mutu gaba daya ba ta hanyar miqata hannun zuriar Sanda Fulde a kauye,zasu hukuntata ta wata hanyar Amma wannan din Kam bazasu iya bari ta tafi ba.

Abdulhameed ma da kansa ya qasqantar da Kai ya ringa rokon ASH din hakama Haydar,
Husnah dinma kanta a cikin kukan da qarfinta ya gama qarewa rokonsa takeyi tana maimaita ta tuba bazata sake tada hankali ba ko rigima da Amatun.

Numfashi ASH din ya sauke ahankali tareda Jin nauyin da kirjinsa ya tokale dashi ya Dan fada Dan haka ya Kalli Abdulhameed din a natse cikin kamewa yace

“Ka tabbatarda kana Sonta zaka aureta?

Gyada Kai Abdul din yayi kansa a qasa
kusan itama Husnah din gyada kan takeyi kaman ita aka tambaya jikinta duka rawa yakeyi sosai.

“Zaka iya tsayawa akan tarbiyanta?
Zaka iya tsayawa akan kulawa da ita da gyara halayenta?
Zaka iya tsayawa kayi hakuri da ciwonta?”

Sake qanqame Abdulhameed din Husnah tayi tana kallansa da jajayen idanuwanta dasuka gama shiga rauni tana fatan yace zai iya duka sbd ita gaba Daya shi din ma takeson aure a ayanzu ta yafe Faisal.

Numfashi Abdulhameed ya sauke ahankali tareda zubawa Husnah din idanuwansa ahankali Ya kalleta kafin ya Maida kallansa inda ASH yake zaune cikin nutsuwa da sanyi yace

“Eh inshallah duka zan iya.”

Haydar Wani sanyi da ajiyan zuciya ne ya ringa saki cikin ransa Yana godewa Allah da Jin sabuwar kaunar Abdul din Dan kuwa ya ceto masa yar uwa daga abinda bazai iya qara rayuwa cikin dadi da farin ciki ba da anyi Husnah din auren kauyen.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

76
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button