Hausa NovelsWata karuwa Hausa Novel

Wata karuwa 29

Sponsored Links

Cikin Aneey yana ƙara kwanaki abubuwa suna ƙara yi mata zafi zuwa yanzun Abdu da Hasina sun ɗinke a bayan fage ko yaushe suna tare Indai baije aiki ba to yana tare da ita a garden house nasa suna sheƙe ayarsu Allah ɗaya zuciyarsa batason yanayin da suke kasancewa amma ya kasa bijire mata tun ranar da taje har ofishinsa ta sameshi ta faɗa masa buƙatarta ya kasa yi mata musu gashi babban abinda yake ɗaga masa hankali Aneey tafi Hasina ɗanɗano nesa ba kusa ba amma baya sha’awarta koda yana tare da ita to zuciyarsa tana gurin yayarta.
Wannan yanayi yayima Aneey ƙunci tana azabtuwa ta riga ta saba da jarabar nacin mijinta cikin watanni takwas ɗinsu gashi tun tafiya batayi nisa ba ya canza mata baya kulata saidai ita ta kulashi idan ma ta kulashi ɗin baya wani sauraronta sai ya kama kawo mata uzurirrikan ƙarya dake bata saba takurawa ɗan adam ba haka zata haƙura koda kuwa zata cutu maimakon kullum abin yayi baya sai taga kamar ma gaba yakeyi cikinta yanada watanni bakwai tayi ƙiba sosai duk da hankalinta ba’a kwance yake ba yau ɗin asabar ce yana gda tayi wankanta suna zaune a falo suna kallo tana kwance kanta a cinyarsa yana wasa da sumarta tayi luf a jikinsa zuciyarta a ƙuntace rabon da ta samu lkcnsa haka har ta manta.
Hannu yasa ya ɗago fuskarta ya zaro idanu lkcn da yaga hawaye ya wanke mata fuska cikin ɗimuwa yace “Ya Salam Wyf mene na kukan me nayi miki?” Kukan ne ya ƙwace mata ta zame ƙasa ta riƙe hannunsa tace “Na roƙeka Prince ka sanar dani abinda nayi maka yasa ka juyamin baya wlh tallahi ina cutuwa meyesa saida ka sabarmin da abinda kasan banida inda zani na sameshi bayan gurinka sannan zaka janyemin tallafi Abdu matarka ce Ni kuma na faɗa maka ba sau ɗaya ba ina cutuwa da wannan matakin daka ɗauka a kaina idan ma laifi nayi maka zuciyarka ta kasa yafemin ka canzamin hukunci wannan yayimin tsauri…..”

 

Cikin tsananin mamaki ta ɗago idanunta dake zubar da hawaye abin firgici shima hawayen yakeyi tayi saurin kai hannunta ta share masa hawayen tace “Na shiga uku Ni Aneesah meye me zafi cikin kalamai na da ya sosa zuciyar mijina har tasashi zubarmin da hawayen da zai iya zama azaba garen…..”
Rufe mata baki yayi ya ɗagota ya zaunar da ita a jikinsa ya haɗe bakinsu suka rinƙa ajiye zuciya a tare kowa damuwa ce ƙunshi² a ransa ta yaya zai fara furta mata baya sha’awarta? Ta yaya zai iya nusar da ita shima baisan dalilin ba ta yarda?” Bashi da amsa hakanan ya janye bakinsa a nata ya rinƙa tausarta da kalamai masu daɗi abinka da mace da miji da ba’a shiga tsakani kawai sai gashi sun ware sun manta da wannan babin yajata suka shige ɗakinsa tun kafin ya fara komai ta kama rigarsa ta zare masa ta sanya yatsunta ta kama nipples ɗinsa ta murza ya saki wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya yayi miƙa kafin ya dawo daidai ta ɗora harshenta akai tana lasa tana lumshe ido tanajin wani shauƙin kasancewa da mijin nata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button